Showing 168001 words to 171000 words out of 191310 words
Chapter 57 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
lulubeni dan ganin yadda take kallona na kasa fassara hakan.
Naji tace watau zainab dazun din ne na tsunkayi wanan mutumin na tare da mijin ki yana waya a hasale .
Saidai jin abinda yake fadane yasani maida hankali in saurare shi dan na fahunci zancen kamar ya shafeki ko wani a gidan nan duk da ban tabbatar da hakan ba gaskiya.
Don naji yana fadin gaskiya ogan mu bai kyauta min ba ni a yanzu na tsani na bude ido inga wanan yarinyar a gidan nan.
A yanzu nayi nadaman yardan da mukayi har wanan mukai sake yarinyar nan ta kai haka tare dashi don yanzu gaba daya ta juye ta zama wata haddadinyar mace sosai.
Katseta nayi ina fadin anty wallahi dani yake don jiya nan da kika turani kiran yaya don na fito part din ya tsareni yana fada wai in daina shiga gun yaya din nan dai na labarta mata komai daya faru tsakanin mu.
A gigice tace wanan zancen da daure kai yake wallahi don haka kawai baki masa komai ba zai tsaneki haka ba tunda bashi ke aureki ba ai.
Me hakan ke nufi ne gareni kuma anty na tambaya cikin damuwa da tashin hankali a tare dani.
Kinsan wasu basu iya samun wuri ba ai sai sucd basa son kowa ya rabu yaci arziki sai su kadai hanyar jirgi daban ta mota daban don haka ya tsaya a matsayin sa zanwa maigidan magana kan hakan ai ta fada tana mikewa tsaye.
Ki tashi ki fita ki sake gidan kine mijinki ne banga wani da ya isa yazo yai maki wani iyawa ba a nan yanzu gaskiya don haka kada ki fara kiyi sake har hakan ya faru dake.
Har ta soma tafiya nace anty dama kin kyaleshi ai kada ki masa magana har sai idan ya kara min irin hakan zan so ayi mai magana din.
Saida ta dan tsaya kamar tana nazari kafin tace to shike nan tunda haka kikaga yafi a barshi in halinsa ne zai sake raina maki wayau ai dan iska damani sam bai kwanta min a rai ba ko kadan.
Bayan fitan ta wanka nayi na fito saida na dan dauki lokaci sosai ina kimtsa jikina a gaban mirrow kafin in shirya in fito waje sha biyu har ya gwauta a lokacin.
Tun daga nesa nake dan jiyo hayaniya a falon gidan ina dan jin muryan ya jafar din kamar yana fada sama sama wanda ban taba ganin hakan ba a tare dashi.
A hankali na tako ba tare dana san ko su waye yake tare dasu ba dasu
a falon a lokacin hankalina kwance na nufo falon .
Wanda na gani sanya saura kiris na juya don saida na kadu sosai ba kowa bane sai mami da anty Aisha a zaune tare dashi a falon .
Gaba dayansu suka juyo suna kallona a cikin mamaki da kaduwa da ganin canzawa da nayi na lokaci guda.
Mami ta dan yatsune fuska gami da tsuke fuskan a lokaci guda ta mike tana fadin ni zan koma ke nan tunda na ganka kaji sauki.
Saura kiris na sake futsari tsoron ganin mami din a bazata naga Aisha ma ta mike kamar a bazata ta ganni tana fadin cike da mamaki a fuskanta.
Zee a gidan nan dama kike zaune wai ko zuwa kikayi kema bata karasa ba don wani tsawa da mami ta daka mata lokaci guda yasa tabi bayan mami din da sauri.
Har lokacin na kasa magana sai ido nake binsu dashi a cikin tsoro da fargaba kafin na tattaro karfi da kuzari lokaci guda na bisu zuwa kofan fitan da suke shirin fita ina kokarin gaida mami din a cikin ladabi.
Tana kokarin shiga mota na karaso wurin da sauri tare da dan rusunawa ina kokarin gaida su banyi mamaki ganin irin yadda ta amsa min gaisuwan nawa a dakile ba don ba yabo ba fallasa.
Irin kallon da Aisha ke bina dashi na mamaki yasa na kara shan jinin jikina ban bar wurin ba sai da naga motarsu ta daga daga farfajiyan gidan don ko kallona mami bata kara yi ba a wurin.
Ajiyan zuciya na sauke don abin ya ban mamaki wanan wani irin kiyayya mami take nuna min hakane na ba gaira ba dalili a kaina.
Juyawa nayi na koma cikin falon gidan jiki ba karfi don ban taba zaton zamu hadu da mami irin haka ba a wanan lokacin.
Bansan har na tsaya ina tunane ba a wurin saida naji takon mutum a bayana firgigit nayi tare dajuyowa shine a tsaye daga kofa ya tsura min ido kafin ya fara takowa zuwa inda nake a nutse.
Yaja ya tsaya a gabana sai nayi saurin dukar da kaina kasa ina wasa da yan yatsun hannuna a hankali.
Maman ki har yanzu fushi takeyi damu kiyi don haka kiyi hakkuri da duk wani abinda zaki ga tayi maki a yanzu.
Samun kaina nayi da sake dan guntun murmushi a fuskana ina fadin ayyah mami har abada mami a matsayin uwa take a garen ai.
Don nima nayi missing din uwata mai tausayina da kauna na har kullun saboda kin bin umurnin ta danayi
Zan shanye duk wani bacin rai da mami zata nuna min har zuwa lokacin da Allah zai huce mata zuciyar ta akaina.
Ina fadin hakan na juya na fara tafiya don barin wurin don kiris nake dana sake hawaye a fuskana don bacin rai ga yadda mami din tayi min kamar taga mugun abu a lokacin.
A bangaren mami kuwa rai bace ta shiga mota sai masifa takeyi tare da fadin na fara yarda da zancen mutane da suke fadin harda asiri a
wanan zancen.
Yaushe na koma haka har yaushe na samu sauyin yanayi haka gaba daya na canzawa ganun ta idan badon a ko ina ta ganni zata iya shedani ba don zaman da tayi a tare dani da shakuwan da mukayi a baya.
Da sai tace wanan watace mai kama dani dai amma ba ni zainan din da ta sani band na canza haka lokaci guda a dan watannin da tayi bata ganni ba.
Muryan Aisha ya katse mata tunane da take fadin mami kinga yadda yarinyar nan ta koma lokaci guda.
Aisha ki rufa mi bakinki indai a kan zancen yarinyar nan ne zee ne kada in saba maki a gurin nan yanzu ki barni naji da abinda ya dameni please.
Jin hakan tayi shiru ta barwa ranta abinda ta hango a tare danni wai zeey din mamice wanan ta koma haka kuwa kodai mai kama da itace takoma haka haka wai ?
Har mami takai gida hankalinta a tashe sai innuwana take hanngowa a idanun ta tana kokarin kawar da zancen a ranta.
A gaskiga tasan yarinyar ba laifi a ko wani ba gare saidai zuciyar ta ya kasa natsuwa da hakan a kanta
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU
🦅
5️⃣2️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
BARKA DA JUMMA,A YAN UWA UBANGIJI YA SADAMU DA ALHERUN DAKE CIKIN WANAN RANAN ALLAHUMA AMIN ALLAH, , , , , ,
KADA KI MANTA LITTAFIN NAN NA KUDI NE DARI UKU NE NA FITAR MAKI DA SHIGA HAKKIN WANI NA FADA MAKI GASKIYA YAR UWA DON KIRA ZAKI IYA KIRANA DA WANAN LAYIN 08036959257.
Don Allah yar uwa ki guji shiga hakkin wani kada ki raina nauyin hakki a gareki kiji tsoron Allah don akwai ranan tambaya.
Ganin mami ya tayar min da sabon miki a rains don haka na shige dakina kai tsaye na fara darza kuka kaman an aiko min da sakon mutuwa.
Tambayan kaina nake menayiwa mami dana cancanci wanan sakamakon haka a gareta ?
Kafin in koma neman mafita a raina na abinda zai fitar dani wanan sarkakkiyar duhun dana jefa kaina a cikin rashin sani.
Duk da nasan ba nina jafa kaina haka kai tsaye ba yadda ake zato banda zabi a kan hakan daya faru dani sai yadda akayi dani a yanzu.
Ina cikin wanan tunanen naji an banko kofan dakin an shigo da sallama ta murya na sheda anty fadilace ta shigo dakin ashe.
Tun a kofa take bina da kallo rai a bace don a zatonta kuka nake na wani abu a yanzun ma kuma.
Sai bina take da kallon mamaki na wanan sallon iskancin dana tsiro yi a gidan bayan dawowan shi kasan ga yadda muka aje zanyi a baya da ita yanzu nazo ina masu faman koke koke haka a gida.
Wanda hakan ke nuna alaman kasawa a gareni bayan duk abinda ta koyar dani a bayan shi wanda hakan ke nufin zaman mu a tare baiyi tasiri ba kenan a yadda nake nunawa yanzun.
Wuri ta samu takai zaune a gefena ba tare da tayi min magana ba na dan lokaci kafin na dago kai na dan kalleta cikin wani yanayi ina fadin a cikin muryan kuka.
Anty me nayiwa mami da take nuna min wanan irin kiyayyan haka a fili shin anty don danta ya zabeni a matsayin sarakuwa a gareta hakan laifine anty don kawai banda gatan daya dace in zama sarakuwar nata ko mai ?
Ajiyan zuciya naji ta sauke tare da fadin meye damuwan ki da matar da ba,a gida daya kuke zaune da itaba yanzu.
Na katseta da fadin amma ai a gidan danta nake zaune anty don haka mami nada daman da zata shigo gidan nan ko wani lokaci kamar yadda dazun tazo na ganta ina gaida ita ta kyaleni.
Tazo gidan nan yau ke nan ta tambayeni cikin mamaki tazo anty na bata amsa wasu hawayen suna zobo min a idanuna lokaci guda naci gaba da fadin .
Har kofan gida na bita ina gaida ita mami ta kyakeni shin anty ni a haka rayuwana zai kare a gidan nan bansan matsayina a gun mami din ba ?
Zata soki zainab na fada maki hakan yafi a kirga kedai kawai a yanzu kiyi kokarin Allah ya mayar dake wani abu a rayuwa.
Amma fa sai idan kin cire damuwa da wanan shirmen hakan zai faru dake don idan kin matsa kin tayar da hankalinki karshen sa ki zama wani abin ki fiye da hakan ga kowa.
Do haka nake fada maki a kullun ki daure ki zama wani abin kwantace a duniya kafin hakan ya faru in ma har bata kaunar ki da danta ai ba kece kika dauko kanki kika kawo gidan nan ba kawo ki akayi da sunan aure.
Don haka ta samu danta daya kawo ki din tayi fadan haka dashi bake ba ke meye laifin ki a cikin zancen nan bayan cutar da rayuwan ki da akeyi yanzu.
Ta yaya mijin ka zaiyi tsawon tafiya irin wanan ya dawo a cikkn kasa ba tare da nuna maka wani kulawa ko damuwan shi a kan ka ba.
Don hakane nake kokarin nuna maki hanyoyin da zamu bi har mu samu a samu kanshi gareki idan ma wani abin ne akai maku a tsakanin ku har hakan ke faruwa.
Har wani lokaci muna dakin tana bani shawara akan mami dama shi ya jafar din akan inta kokarin in kawar da wani kunya ko nauyinsa a raina indinga cusa kaina gareshi ko yana nuna min baya son hakan da nake mai.
Jinta kawai nakeyi a raina sai fadi nake ta yaya zan kai kaina inda za,a wullakantani a daukeni ba kowa ba.
Zandai zauna a matsayin tallafawa rayuwan iyayyena da yan uwana a gidan sa don ni kaina nasan da bankai matsayin mata ko masoyiya a gareshi ba.
Bayan nayi sallah la,asar ne na fito zuwa dakin maizube inda na sameta zaune tana shan ferfesun a cikin wani plate mai zurfi a gaban ta sai tururi da yake tashi da kamshi a cikin plate din.
Ta dago tana fadin yanzu nake fadi in gama in kara lekaki zuwana biyu dakin yana rufe na dauka ai kina wurin mijin kine tun dazu ?
Dan murmushin yake nayi iya fuskana a raina ina fadin wani miji da baima san da zamana a gidan nan ba .
Zama nayi saman gado ina gaida ita tare da fadin tun safe ina daki kwance ban dai fito bane tunda yanzu gidan akwai maza masu shigowa ko wani lokaci.
Tace nima abinda ya zaunar dani dakin nan ke nan kada su takura da zaman mu haka shiyasa ma na fadawa malam zan dawo zuwa jibi tunda dai Allah ya dawo da mijin naki lafiya kuma.
Da sauri na dago kai ina kallonta tare da fadi cikin mamaki ki koma gida kuma maizube shifa ba mai zama bane kasan nan wata kila wani abin ma ya kawoshi yanzu haka dayazo din.
Don dazun ma naga mahaifiyarshi tazo gidan nan da safe sai naji tace a cikin mamaki ta shigo gidan nan bamu sani ba yar nan ai a gaisa dai ko ?
Maizube koni fitowa nayi na gansu a falo tare dashi haka kuma naga ta mike a cikin bacin rai ta bar gidan nan ko gausuwa dana bita waje nayi mata ban samu amsawan arziki a wurinta ba ta wuce.
Kai wasu dai sun dauki duniyan nan da zafi a ransu har yaushe wanan matar zata sauko daga fushi da kaddaran Allah da takeyi ne daku ?
Kada ki yarda ki biye ma duk wani hali datake nuna maki na kyama a gareki dan ba ita kike aure ba biyewa halinta kuma mijin ki ba zaiji dadin hakan ba don mahaifiyarsa ce ita.
Kinga kuwa ba zai taba lamuntan hakan ba koda itace bata da gaskiya kuwa ranshi zai bacine ga abin da zaki mata ke don haka ki daure ki hade tunda ba ko yaushe ne kuke haduwa da ita ba sai irin haka idan tazo ko kinje inda take din.
Shima kasa ki daure da halinsa ki zauna kiyi hakkuri mai hakkuri yana tare da riba wata rana duk wanan abin zai zamo tarihin rayuwa a wurin kine a kuma hada da addua ga komai da sadaka don kariya ga ko wani irin bala,in rayuwa.
Insha Allahu zan yi maizube na gode da shawaran da kuke bani a kullun keda anty fadila a gidan nan ba zan taba matawa daku ba a rayuwana na fada idanuna yana kawo hawaye a lokaci guda.
Nikan yaya kowa keson nayi ta cusa kaina ga ya jafar ne mutumin da har yau ko murmushin arziki ban samu a gurin shi ba balle wani maganan arziki irin na mata da miji ya shiga tsakani na dashi.
Ta yaya ake son in biye masa har muyi zaman auren da mutane suke hasaso min rayuwan jin dadi nan gaba dashi.
Don in kawar da zancen nace amma dai ba yanzu kike nufin komawan ki gida ba matar malam ?
Me zan zauna inyi a nan kuma tunda Allah ya dawo da mijin ki lafiya wurin ki kuma ai sai a raina muna hankali kuma idan na zauna haka.
Haba dai wa zai damu da zaman ki a nan don Allah kada kice zaki tafi ki barni a gidan nan ni kadai ba zan iya zama dasu ba wallahi.
Zaki iya mana ta ban amsa ko wace mace da kike gani haka ta koyi zama a gidan mijin ta harta saba da hakan kema a sannu zaki saba da zama ke dayan ai.
Maizube ban dauka wanan zaman da nakeyi a gidan nan ba na aure ne ba subbahanallahi naji ta fada da sauri har naji tsoro na dago kaina.
Idan ba zaman aure kikeyi ba zaman me kikeyi a nan kada ki yarda ki bata auren ki don wani dalili can da kike hange .
Kowa da yadda kaddaransa ke zo masa a rayuwa wanan shine naki kaddaran rayuwan kke zuwa mai Allah yayi akwai aure a tsakanin ku wanda muke fatan harda zuria idab Allah ya yarda nan gaba a tsakanin ku .
Jinta kawai nakeyi duk da nake yarinyace ni amma nasan hakan ba mai yuyuwa bane a tsakanin mu don ruwa ba sa,an kwando bane.
Tambayana tayi da naci abinci kuwa itama dai nasan kokarin kawar da damuwa a zuciyana takeyi lokacin.
Idan nabar nan zanje na duba abinda zanci na bata amsa da hakan na dan dade zaune ina tunane kafin in mike zuwa falo na bar dakin nata.
Ina ficewa falon na nufa dining erea dan samun abinda zan saka a cikina don naji cikina ya fara kugi a lokacin.
Kai tsaye wurin dining din na nufa kayan abincin dake wurin na fsra budewa a hankali gaba daya hankali na gurin abinda nake dubawa din duk sai naji ba zan iya cinsu ba a yadda nakeji lokacin.
Haka yasa sam bansan yana falon ba a lokacin yana zaune shi kadai a cikin falon ya tasa takardu da laptop din shi a gaba yana aiki a cikin su.
Zaune yake yabar abinda yakeyi ya zuba min ido daga inda nake tsaye ina bude kayan abincin danaga