Showing 72001 words to 75000 words out of 191310 words
Chapter 25 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
Ina ban daki nake wanan fadan a raina na fito ban tsaya jiran komai ba na hau kujera na kwanta har barci ya daukeni ban sani ba don ban san lokacin da hjy ta shigo dakin ba bayan sun gama hiran su a falon don ko hidimar da nakewa mami ranan ban samu yimata shi ba.
Koda mami ta rako hjy dakin ta samu ina barci bata tayar dani ba ta kyaleni hakana sai cikin dare dana falkone naga wutan dakin a kashe.
Washe gari da safema motsin hjy ce ya falkar dani na tashi nima nayi sallah na idar na zauna a wurin hjy ta shafa tana fadin in koma in kwanta tunda ido akwai barci daga haka taci gaba dajan tasbahan ta.
A daidai lokacin da nake shiga na gyarawa mami dakina falka kamar an tasheni har lokacin tsohuwar tana zaune a inda take.
Mikewa nayi ba tare danayi magana ba na nufi dakin mami din ko a nan ma itama zaune take tana azzakar din safiya.
Ban fito daga dakin ba saidana karasa komai na dawo na samu hjy ta dan kwanta a lokacin banyi dogon motsi ba wanka nayi tare da kara wanke ban dakin har na shirya a hankali duk tsohuwar tana barcin safe wanda nasan na gajiyane.
Sai bayan goma da rabi ta falka lokacin mami tayi mayawa a dakin yakai sau uku tana duba mahaifiyar nata.
Ruwan wanka na hada mata tayi wanka na taimaka mata data fito har ta shirya saiga abin karyawa an kawo mata har daki yaran gidan suna shigowa daya bayan daya suna gaida ita da kwana.
Har suka dauke kafansu sai Aishace bata shigoba nasan bata tashi bane don ita sai wuraren sha biyun rana dama take tashi barcin safe ko ma zuwa dayan rana.
Nan muka zauna muna hira da hjy don ban yarda na fita ba ko karyawa a cikin na tsohuwar na karya dashi take tambayana ni yar wani garine ?
Nace ancau hjy tace ashema yar jaharnan ce ke na dauka ko yar shiyan jalingone ke ko bauchin don na ganki da zubin fulani.
Nace innatace dai bafullata Abban kuma bazzagene shi yar nan da asalin ki haka har yaran nan suke maki wanan tsiyar haka ?
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣2️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERI GAREKU MASOYA UBANGIJI YA DAUKAKA MUSULUNCI A DUNIYA AMIN, , , ,
Banyi zaton akwai macen da zata kai sha shidda a yanzu ba wace bata san zata mutu ta koma wurin ubangijin ta ba da har za a hada da Allah da annabi ta rufe kunne da ido don rashin tunawa da Allah dayai mata rai da numfashi da take takama dashi a duniya wanda ubangiji zai iya karban abinsa duk sanda yaso .
Yan uwa mu kulla da daraja da nauyin wanan sunan biyu idan ance Allah da annabi a zatona angama da musulmi ashe abin ba haka yake ba a wurin wasu.
Allah kasa mufi karfin zukatan mu ya Allah ka bamu cikawa da imani amin kada ki karanta idan baki biya ba mai turawa na barki ga Allah shi yasan tsakanin mu dake.
Sallama akayi daga kofan dakin yayin da mu kuma dariya ya dauke muna hankali a cikin dakin don tsohuwar dariyan labarina dana fara batane ina fadin garin mu ai kauyene kuma yan garin muma kauyawane a cikin sa don kaka hajiya bata kaiki tsufa ba amma bata wanka daga jumma, a sai jumma, a take wanka tunda wai bata da miji da zataiwa wanka.
Sallama ya kara yi nice na karba a cikin raha da walwala don dan zaman mu da tsohuwar yasa na mance da duk wani bacin rai dana kwana dashi a gidan.
Dan miko min wanan kawar da wanan gurin nan sai duba can ki miko min abu kaza dauki wanan kici hakan yasa na manta da komai dake a raina a lokacin.
Wa,alaikum sallam na fada don hjy ita dariya yaci karfin ta a lokacin itama dai cikin dariyan take amsa mai haka yasa ya turo kofan gaba daya ya shigo.
Saye yake a cikin farar jallabiya mai laushi sai wani maiko takeyi ashe jallabiyar ma suna suka tara sabanin da danake masu bugu daya don duk jallabiya da farko daya nake daukan su sai zuwa gidan mami ne na fara bambanta jallabiya yanzu.
Yakaraso yana tako kamar wani balarabe dashi har zuwa kujaran da hjy take zaune sama a cikin hausan shi mai kama dana dan koyon hausa din.
Yana fadin wanan dariya haka hjy kamar an gafarta maki yau fa don nidai badon nasan iyayyen su ba sai ince su din jinin labawan asaline .
Don hasken jikin su yafi kama dana larabawa a gidan ga tsayi duk dadai shi yaya jafar din ya fisu tsayi sosai a cikin su sai jamal da jalal saidai basu kaishi tsayi ba su zan iya cewa su din kamar mahaifin su suka kwaso don ko ban sanshi a fili ba na san shi a manyan photunan shi dake falon gidan.
Don shi mutum ne fari dogo ga tsayi ga kyau kamar shi yayi kansa wurin halitta duk da ya manyata a photunan lokacin dayayi su hakan bai hana kyau shi fita ba a fili.
Hakan yasa nake kasa bambanta tsakanin su da dan nasa ko a cikin su wayafi kyau haka.
Shi yaya mamud duk da farine sol baikai yan uwanshi tsayi ba yana dai da nasa gwargwado sai Aisha da ta biyo mami sak wurin kama.
Don ba inda ta rage mahaifiyar tasu sai dai idan halin mahaifin su ne ta kwaso na rashin hayaniya dason motsa jiki don mami kan ita da alama ba mai yawan son jikibane ita don wani lokaci zan samu tanayin abu da kanta sai nazo in karbe ta.
A cikin dariya hjy ke labarta mashi hiran mu tana kwasan dariya fuska a daure ya dan dago ya kalleni tare da kawar da kanshi duk lokaci guda.
Ina tsugune nake gaidashi da kwana tare da mikewa don barin dakin duk da ina tunane a raina ina zan dosa idan na fita don gudun haduwa da yan matsalan gidan mami din yan kafi mai abu iko.
Don ni sai daga bayane ma nasan ba mami ta haifesu ba a wurin anty Aisha yadda nazo gidan na samu sunayin abu a gadarance da yadda mami ke nuna kamar itace ta haifi abinta.
Ina kuma zaki muna hiran mu kin dauko ban labari ina sauraren ki indon wanan ne ai shi nasan yanzu fita zaiyi a dakin don ba zama zaiyi ba ko kunya fada a gaban shi kikeyi.
Dawo ki zauna muyi hiran mu kinji jikata ta kaina aini kin ganni nan ina son jin irin labarin nan sosai wallahi don nima kinga daga karkara na fito ai.
Idon shi a waya kamar mayen waya ko computer dana sa mai yake fadin wani No kuyi hiran ku ni nawa nakeyi nan .
Tace dada Asabe kowa kikace sunan ta nace a sanyayye don kasancewan shi wurin nake fadin Asabe ne.
Ta nuna min bakin gado tana fadin zauna mana a tsaye zamuyi hiran haka na kai zaune a dan takure.
Yanzu mahaifiyar ki dai tana tare da Abban ki ko ta tambaya take yanayi na yacanza a hankali nace suna tare da Abbanmu har yanzu.
Saidai ba a cikin dadin raiba don Asabe tasa Abban mu yai wani auren wai don innan mu diya mata take haihuwa ita kuma bataga amfanin diya mace ba.
Shima dalilin turoni birni wurin mami da Asabe da lantana sukayi wai nazo inyi aikatau a nan don hakane kawai za a morewa diya mace na karasa ina share hawaye.
Kai ya dago ya kalleni a cikin mamakin jin abindana fada din na zancen Asabe ga innan mu da muka bude ido dashi a gidan kullun sai tayiwa inna gorin shi.
Haba haba yar nan kada ki kuka mana nasan wanan zancen yana da ciwo sosai don baku ai kukayo kanku diya matan ba wasu ma nacan suna son diya matan kamar suyi hauka basu samu ba ita tasan baiwan da Allah yai maku dayayo ku diya mata a garesu.
Abin mamaki sai naji ya saka muna baki a hiran mu yana tambayana ku nawane a wurin mahaifiyar ku da har take fadin hakan ?
Mu bakwai ne nice babba a dakin mu sai kanne guda shidda dana bari tare da innar mu a gida.
Babu ma wanda aka wanke a cikin ku ke nan tunda kece babba ashe kai wasu mutane da shishigin tsiya suke har da Allah sukewa izzigili.
Shi mahaifin ki fa yaya ya tambaya sai na dago na kalleshi don ban fahinci mai tambayan shi ke nufi ba.
Saidai na basu amsa da fadin yana nan kawai yace No ina nufin wani mataki ya dauka kan wanan zance
Da Abba baya daukan zancen Asabe amma yanzu tunda ya auro lanta kuma ta haifi na miji sai ya sauyawa innar mu damu ga baki daya a gida yanzu ba ruwan Abba damu kamar da can baya na fada idanuwana suna kawo ruwan da ban iya controling din su a lokacin.
Haba yar nan ki daina kuka kada nima ki sakani kukan don wanan labari naki akwaicin zuciya gaskiya.
Do me bataga laifin danta ba dashi yake ba uwarki diya matan sai uwarku kadai zataga laifin su ta fada a hasale.
Muryan mami ne data dawo take kwala min kira daga waje yasa na mike tsab na fita dakin da sauri na barsu a zaune da hjy.
Duban hjy yayi yana fadin hjy ashe har yanzu akwai itin mutanen nan masu halin dabba a kasan nan yadda yanzu addini ya zagaye kasan nan.
Yo jafari mai za a fasa a wurin kishin muna mata wasu matan fa kishi suke da matan diyan su kila irin hakane ya ke faruwa a gidan har wanan tsana ya shiga.
Amma idan bashi ba menene laifin haihuwan diya mace a duniyan nan ni ba gani ba kai bani kadai ba har kowa ai yanzu moriyan diya mace mukeci kaf zuriam mu ga baki daya.
Don uwarkuce tsaye da gidan ni kaina da kaganni nan na fuskanci itin wanan matsalan lokacin dana jera haihuwan iyayyen ku mata har su hudu a lokaci guda ban haifi namiji ba.
Sai dai ni kishiyace ta goranta min hakan bawai uwar miji ko wani irun wanan zancen yana da shiga zuciyar bawa don yanzu Allah kadai yasan halin da uwar yarinyar nan take cikin dan bakin ciki kan tana ganin sa.
Amma idan tayi hakkuri wataran sai labari yau ba gani danayi hakkuri na shanye hakan ba uwarku sai Allah ya daukaka muna ita ta zama muna zakara a cikin mazan.
Yau zeey mami ta fada ki dauki wanan kikai dakin ku na hjy ne ki kula da bata tana ci lokaci lokaci kinji.
Nace to mami ina daukan ledan da ban san ko na meye ba a cikin sa har na juya zan tafi take fadin zeey na juyo da na,am mami sai kuma ta kasa fadin abinda zata fada tana kallon fuskana da mamaki ta furta.
Zeey kinyi kuka ko zancen jiyane har yanzu a ranki ko kuma wani ya kara tabaki gidan nan yanzu kuma ?
Kai na girgiza da sauri alaman a, a tace to me akai maki fuskan a haka ko gida kika fara tunane kuma.
Nace a a a sanyayye ina juyawa sai ta bini da kallo mikewa itama tayi ta biyoni baya ban san mami na bayana ba sai dana shiga dakin da sallama naji mami na fadin a a ashe kana nan tare da hjy ne yanzu fa nake shirin zeey ta kira min kai a waje na kira layin ka bakai picking ba.
Yacs OK mami nabar wancan wayan daki da zan fito ai nazo gaida grany ce da kwana sai kuma na zauna muna hira.
Wanan yarinyar na gani kamar tayi kuka ai shine na biyota in tambayeta ko wani abin kuma akai mata na ganta haka ?
Ba wanda ya tabata tun safe muna dakin nan tare da ita nasan kukan da tayine kan labarin yan gidan su da take bani yanzu.
Ta labarta maki jahilcin kakarta ke nan ko don shine damuwan ta a zuciya kullun Asabe ta tsani mahaifiyar su don kawai ta haifesu a diya mata.
Shine fa yanzun nake mata musali dake kika kirata irin wanan mata da yawa suna haduwa dashi a rayuwan su in Allah ya hadasu zama da mace mara imani ga ubangiji har ma a cikin masu ilimin akwaisu sosai har gobe .
Na fada mata ta kwantar da hankalinta muddin ina raye a duniyan nan sai tayi ilimin data tallafi gidan su insha Allah .
Asabe zata gane diya mata ma mutane ne kamar kowa ba abin wullakantawa bane a gida.
Mikawa hjy ledan dake hannuna nayi ina fadin mami ne tace in shigo maki dashi nan nakine na fada ina ajewa gaban hjyn nata a cikin ladabi.
Me muka samu kuma nan ta fada tana kokatin budan ledan dake gaban ta lokaci daya ba komai bane sai goron ki da sauran tarkace dazaku bukata a nan dana san kina amfani dashi mami ta fada.
Mami goro kuma ya kamata ace ta bar cin goron nan a yanzu fa don jikin tsufa daya kamata zai iya mata illa wanan goron haka.
Ungo naka da zai mun illa da tuni yayi min tun kan a haifeka nake cin goro na a duniyan nan gani ko garau kana ganina.
Allah baki hakkuri ya fada tare da mikewa tsaye yana gyara rigar shi hjy tace tafiya zakayi kuma muna zaune muna hiran mu ?
Na gama hiran ai ku karasa hiran ku damani ai ba dani aka fara ba ya fada yana ficewa tace miskili kafi gaban gayya wanan wanan zan so naga macen da zata iya zama dashi haka.
Mutum kuna zaune kalau ya birkice maka lokaci guda kuma ya hana ayi magana don tsaban miskilanci.
Fita yayi daga dakin ba tare daya kara mata magana mami na gefe tana murmushi mama kande ne ta shigo dakin da sallamanta muka amsa take.
Fadin mama ga abinci an gama na kawo maki da cewa hjy tana fadin sannu sanu yarnan sannu da kokari har kun kare na rana ban dade da cin na safeba ai.
Ai kande akwai kokari shiyasa nake son daukesu mu koma Abuja don gwarawan nan sun isheni basu iya irin cimar muba nan sai kalar tasu abincin.
Saidai kuma ina tunanen wanda zan bar yaran nan dasu a gidan nan don baka barin ya mace ita kadai a gida.
Yo da kin fada tun bamu taso ba ai da anyiwa ladidi magana me take a gidan banda yawon bin makwata sai tazo ko ta zauna dasu nan kinga an rage mata ma wahala ai.
Mami tace indai ya ladidin zata yarda hjy ai mata magana kafin mu wuce in sani don in tura su kande gida suyi sallama da mutanen su asan zasu tafi.
Zan kira yayan ku in sheda mashi yai mata magana aji me zatace wanan ai ragewa ladidi nauyi ne babba.
Kande ko baku zuwa mu koma Abuja mami ta tambaya sai kande din tace yo hjy ko ina kikace mu tafi aini mai bin umurnin ki ne.
Yafi mun zama nan da yaran nan naki da basa jin magana na gara dai ina kusa dake yafi dadi ta fita tana murna tare da fatan Allah yasa a tafi da su din.
Lokacin sallah yayi mami ta bar dakin aka barmu dagani sai hjy sai bayan mun idar ne muka zauna cin abincin rana lokacin ne kuma anty Aisha ta shigo gaida hjy da kwana.
Tana wani daure fuska don tasan hjy zatai mata tsiya nan dai sukaita barkwancin su kafin Aishan ta juyo tana fadin .
Zainab yanzu ba a ganin ki tunda hjy tazo na hadiye abincin dana saka a bakina ina fadin dazun na lekaki har sau biyu in gyara maki daki kina barci.
To ai yanzu na tashi ta fada nace bari gama naje na gyara maki sai hjy tace ke arr ke kan anyi malalaciyar yarinya a nan sam baki biyo halin uwarki ba ke kan.
Don Allah hjy ki rufa min asiri kafa mami ta shigo ta sakani gaba banda abinki don kawai ta gyara min daki shine wani abu.
Yanzu ke haka za a kaiki aure ko gyaran daki baki iya ba kina haka tace wai hjy wa ya fada maki ban iya ba kawai dai ban samun lokacin hakane a tare dani.
Haka rayuwan ke gudana yanzu zan iya cewa na samu sauki sosai iyakata in shiga dakin mami in gyara sai na anty Aisha sai bayan kwana biyu kuma a ce in gyarawa yaya dakin