Showing 111001 words to 114000 words out of 191310 words

Chapter 38 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt

yana sauraren duk abinda ke faruwa lokacin.
Idanun shi ya runtse a cikin takaici da bacin rai why mami zata tsani yar mutane haka har su dora mata mugun tabo mai zafi hakan nan.
Ga kalman da baffan shi ya fada dazun cewa don zeey ya kama masu yara yai masu wullakanci don kawai yana takama shi mai arzikine ko yafi kowane yake gani.
Ya dade a zaune inda yake duk da dare ya soma sai yaji sam ba zai iya kwana bai fadawa wani daga cikin mutanen nan wanda baida wani aboki ko shakiki da sukafi mai yanuwan shi na jini.
Baida aboki ko wani amini a kasan daya wuce mai yan uwan haihuwan shi kasancewan shi wanda bai tashi a kasan shi na ainihi ba Nageria.
Haka yasa komai da zaiyi anan ya mamud ne mutum na farko da yake nema ga shawaran shi kamar yadda shima ya mamud din bai wasa da lamarin kanin sa don yana masa biyayya yadda ya dace ga kyautatawa ko yaushe a tsakanin su.
Sai kuma yan kannen shi biyu jamal da jalal sumafi dinkewa da jamal don halin su da yazo kusan daya sosai.
Bayan su akwai Bukar dan kanin mahaifinsu wanda kusan akwai dan shakuwa sosai shima don zai iya cewa shine mutum na farko ds ya yarda dashi bayan yan uwan nasa.
Don tun suna yara bukar din yake nuna ra,ayin shi akansu har wanan lokacin da suka kai hakan bai daina kula dan uwan nasa ba duk da yasan shi din mutum ne da baida saurin sabo lokaci daya.
Ya mamud dake shirin kwanciya tare da matarshi Nuriya yajo kiran dan uwan nasa ya shigo mai don yasa ba halin shi bane kira a cikin dare.
Furta suna shi da yayi ne yasa Nuriya dake gefen shi dan dagowa da sauri tana kallon shi da mamaki don ita a nata rayuwan ta tsani duk wani dan uwa mijin nata.
Tundai shi da take ganin yafi mijinta da komai a rayuwa kamar mijin nata, yana son mayar da kanshi a karkashin shi yanzu wanda ita kuma irun matan nan ne da basu son hakan.
Jafar ya akayine ya mamud ya fada lokacin daya dauki kiran na dan uwannasa normal ya fada saidai ina so zuwa safe ka bincika min meke faruwa a gidan nan don Aisha was telling that that girl ta saci kudin mami wanda nasan sheri ne wanan suke kokarin mata.
What sata kuma ya mamud ya fada da dan karfi wanda hakan yasa Nuriya dago kai ta dan kalleshi cikin mamaki don jin abinda ya fada.
No nima nasan da hakan wanan yarinyar ba zata taba haka ba jafar saidai idan wani sheri kuma ake kokari kulla mata yanzu which is bad .
Yanzu dare yayi sun rufe muma nan muna shirin kwanciyane da safe zan binciki hjy in fara jin abindaya faru.
Ya samu ya lalaba dan uwan nasa suka kashe wayan Nuriya take fadin wanan yarinyar ce tayi sata kowa ?
Ba sata ba kan yau take gidan nan tare dasu wani dai abinne kila yake faruwa a tsakanin su har haka ya faru.
Dama nasan haka zaka fada don har kai ina zargi akan wanan yarinyar da farko don kawai dan uwanka ya rigaka furta mata sone kaima nasan da hakan zakayi.
Da mamaki ya dago yana kallon ta tace eh na sani don yarinyar macijiyace babu namijin da zai ganta farat daya baiji yana sonta ba sai dai bakin tabo ya yanke mata kadari ai.
Don warin talauci da yake binta ita din kaskantatace a idon kowa don bakin talaucin iyayyenta har kasa riketa sukayi suka turota aikatau a birni.
What noses talking kike fada haka me yarinyar nan tayi maki haka wai kika tsaneta kema ina yanzu kika gama fadar dan uwana ke sonta da bakin ki .
Bazan taba lamunta hakan ba yarinyar nan abin tausayine bata da matsala da kowa a gidan nan ki duba yadda take kula yaran nan tankar ciki daya suka fito dasu duk da tasan ke baki son hakan da takeyi masu din.
Bai bata wani kafa da zata fadi wani abuba akai dole tayi shiru ba don taso ba ta kyale zancen a ranta.
Washegari na tashi da zazzabi mai karfi wanda har ya tayar da hankalin hjy a dakin ta nufi gurin mami tana fadin yar nan fa iyami zancen nan har zazzabi ya saukar mata jiya bamuyi barci da dadi ba.
Budan bakin mami sai cewa tayi wanan kuma ai matsalantane tunda nida taiwa laifin ban dauki wani mataki ba a kai balle ta zauna tanawa mutane ciwon banza a gida.
Anya ! Iyami kina da tausayi yanzu kuwa hjy abinne da ban haushi tun jiya nake ganin take taken yarinyar nan ita a dole gata mai zuciya ko.
Mikewa mami tayi ta ballo magani tana fadin ta sha wanan zai sauka idan na fito zan shigo in dubata.
Hjy dai ta karbo maganin cikin sanyin jiki dajin kuna a ranta yadda gaba daya yar nata ta sauya akidarta ga baki daya har yakai tsohuwar tana zargi a ranta kodai wani abu ya shiga kan mami din ne.
Nasha magani cikin ikon Allah naji daman jikin nawa gashi ina son zuwa inyi aikina a daki mami kuma ina jin tsoron shiga dakin yanzu.
Babu yadda na iya haka yasa na sauko daga kan gadon a hankali na dan zauna a bakin gado hjy data fitowa ban daki ta dauro alwala ta ganni a zaune take fadin.
Alhamdullahi sauki ya samu ke nan nace eh hjy ya fada min ina kokari tashi tsaye take fadin ina kuma zaki tafi yanzu.
Zan tafi in gyarawa mami dakine na bata amsa koma ki kwanta babu inda zaki yanzu kina jin jikin nan yarta ta gyara mata idan ta matsu.
Ban iya furta komai ba dole na koma na kwanta don bazan iya mussawa tsohuwar ba don nasan wanan tsakanin sune da mami kuma don nasan baida wuya hakan ya zama wani matsala kuma.
Kara rufa nayi har barci ya soma daukata naji hjy na fadin in tashi in kara karyawa kafin barci ya daukeki.
Zan tashi na fada ina gyara kwanciyana ya mamud yayi sallama a dakin ta amsa mashi suka gaisa ya samu wuri ya zauna.
Ina daga kwance ina jin hiran su a cikin ba, a kafin yace wanan da take rufe haka meya sameta ne kuma ?
Zazzabi ke damunta tunjiya gata nan a kwance yace subbahanallahi shine ba a kaita asibiti ba take kwance a gida haka.
Uwarku ta bata magani shine ta dan samu saukin nan Allah ya kara sauki ya fada kafin yace jiya da dare jafar ya kirani yake fada min wani zance mara dadin ji wai Aisha ta fada mai yarinyar nan ta satarwa mami kudi yaya zancen yakene hajiya ?
Dama nasan za a rina saidana gargadi uwarku kan zancen nan amma ta bari zancen nan yakai kunnen yaron nan.
Nawane kudin yaya jafar ya tambaya zaka biya mata ne mami ke fada daga kofan No mami ba wai zan biya bane kawai dai tambaya nakeyi don in sani.
Ka koma ka fadawa wanda ya aikoka cewa dubu dari ukune ina jiran inji alernt ta fada a cikin gatse ta juya inda nake kwance ina hawaye tana fadin ke zeey jikin bai saki bane ki gyaro min daki ni fita zanyi.
Nice nan na hanata zuwa don kowa yasan da ciwo a dakin shi ai don haka sai idan taji sauki.




ZAINAB IDRIS MAKAWA








🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅


ZAINAB IDRIS MAKAWA




3️⃣3️⃣




BARKA DA WARHAKA YAR UWA UBANGIJI YA BAMU WUNI LAFIYA AMIN.




Tana tafe a fusace don ranta daya riga ya baci da yaranta a dakin hjy data shiga sallama da ita ta samu ya mamud suna zancen da hjynta ta ballashi ta fito da fushi ranta a bace cike da tunane.
Tun kan ta iso bakin motan security din ta suka mike tsaye tare da bude motar suna jiran isowan ta wurin.
Tsayawa tayi gaisawa da masu gadi da wanki da mai kulla da komai dake gudana a gidan massege ne yashigo wayan ta tayi niyar shiga mota ta diba sai kuma ta dakata a yadda take tsaye.
Kafatan daya na a motan yayin da dayan kafan nata yake waje ta dafa motan ta bude sakon da mamakin ko sakon meye ya shigo mata a wanan lokaci.
What ta fada da dan karfi, bayan ta karanta sakon dake a fuskan wayan nata a fusace ta juya zuwa cikin gidan tana shiga a kofa suka hadu da ya mamud.
Gaba daya yanayin fuskanta duk ya sauya ranta ya gama baci tanajin zuciyan ta bakikirin a lokacin.
Wani sakon ne ya sake shigowa a lokacin a hasale take duba sakon take idon ta ya kara kankancewa ga baki daya.
Mamud da suka hadu a lokacin ganin yanayinta mami lafiya ya ya fada a dan razane ?
Wani kallo tayi mai kafinta ce biyoni muje ciki kawai ta fada tana gaba yana biye da ita a baya.
Dakin namu suka shiga wurin hjy da sallama cikin wani irin yanayi hjy dake zaune take fadin lafiya dai ko iyami ?
Hjy yaron nan me yake nufine, me yake tunanen ya taka da har zai rainani ko ince su rainani.
Wai me ke faruwane haka iyami ya mamud daya karasa shigowa yake fadin .
Wai mami wani abune kuma akayi yanzu rufa min baki ta fada a cikin tsawa wallahi ka zama babban banza a gurin kannen ka mamud.
Wani kallon mamaki ya jefowa uwar don baisan dalilin wanan fada ba a sanyayye ya furta a cikin mamaki mami ni kuma me nayi yanzu kuma ?
Hjy wai ki duba yaron nan dan baida wayau kullun shi dan maganan nan danayi yanzun nan yaron nan ya kwashe ya fadawa dan uwansa.
Wai sai gashi jafar ya turo min kudi masu yawa haka har yana fada min ga kudin aikina nan tun lokacin dana dauko zainab a gidan ya biya.
Shike nan ta faru ta kare dan nan ya fashi yarinyar nan a gidan nan yanzun kuma sai ki samo wata.
Hjy me kike fada haka kuma sanda na dauko yarinyar nan nayi shawara da shine ko yasan su waye iyayyen ta?
Wallahi wallahi mami ga hjy nan idan nayi magana da Jafar a yanzu kan na fita dakin nan wurin ta ya mamud ya fada rai bace hankali a tashe.
Hjy tayi wani shu,umin murmushi a fuskanta kafin takai zaune cikin tagumi tana karkada kafan ta a cikin mamaki.
Hannu takai ta cire glass din dake sanye a idon ta na fadin ni jafar zai nunawa yanzu wuyan shi ya isa yanka.
Har zai turo min miliyoyin kudi waishi a dole ya fanshi zeey a hannu na to dashi da kudin nasa duk sun, , , , ,
Kai kai kai iyami karki soma furta wani zance mara dadi ga danki dan yau ne fa ke kuma uwar zamani kinga kuna kamanceceniya a wurin hali.
Ba yadda banyi dake ba a gidan nan tun kan zancen nan ya kainan na baki shawara da ki zuba masu ido ki kyalesu suyi soyayyan su.
Wasan gobe banda Allah iyami Allah kadai yasan meya tsara ga hakan kince ba hakan ba kin tsaya kina jayayya da hukuncin ubangiji.
Iyami ina ji maki tsoron irin abinda zaije ya dawo baya a kan wanan jayayyan da kikeyi a yanzu.
Yaron nan idan dai ba alhakinshi zaki dauka ba a banza wallahi baiyi waya da dan uwansa ba a dakin nan yanzun nan ya fita.
Hjy dan Allah bari lokacin da zai aikata hakan kina ina zai iya tura mai sako.
Mami baki yarda da rantsuwana ba kenan ya fada a dan mairaice yana maijin wani iri a ransa ba dadi duk yana jin mami ta muzantashi a lokacin.
Ya dubi mami fuska a daure yana fadin ki kira jafar din yanzu aji wanda ya fada mai don ni wanan abin gaba daya mami kin jefani a cikin zargi .
Idan bakai bane waye ko yarinyar nan ne zeey gata kuma a kwance tun dazun sai dai idan daga kwancen ta kulla wanan sherin ba abin mamaki bane kuma.
Haba mami ji wanan don Allah bai dace ba meye laifin yarinyar nan a yanzu kuma don Allah ?
Kai ke na ka fadamai saka fito fili kafada sukaji muryan Jafar na fadin hi bro ya akayi ne ka fito ke nan naji duk abinda mami ke fadi a waya dazun so na tura mata da kudin sai tai set din yarinyar free by now.
A samo wata daga yau ta dinga wanan aiki ita kuma tayi facing din karatun ta final.
Eehhee mara kunya beran tankwa nayi shawara da kaine da zan karbo ta yaji muryan mami tana fada a cikin tsawa.
No mami bakiyi ba saidai tunda abin har yakai wanan irin zargin yana shiga tsakanin ku let her set free by now tayi karatunta kawai.
Mami yanzun kin daina zargina a wanan zancen me zaisa na fadawa jafar wanan magana tunda nasan a cikin fushi kika fade shi.
Ni kuma ba zan so inga wani abu na tashi hankali haka ya faruwa a tsakanin kuba ko yaushe Jafar fa dankine mami.
Yau yace ga abinda yake so a rayuwan shi mami ya kamata ki sasauta zuciyan ki don in kin kula jafar yayi nisa a wanan zan, , , ,
Kaga dai yanzu na gane yadda zancen yake don haka katafi kawai kada ka makara a wurin aikin ka ta fada kuma a dan hasale.
Toh mami na gode ni zan tafi ya fada yana mikewa daga bakin gadon da ya zauna da farko a gigice.
Yama manta a kusa dani ya kai zaune a lokavin don haka bai kara waigowa ba ya fice daga dakin.
Idona biyu duk zancen da sukeyi yana a kunne na ina sauraren su ban yarda na motsa ko kadan ba don kar mami ta gane a falke nake duk da bana tantama da tasan a falke din nake a lokacin.
Mami naji ta mike tsaye tana fadin ni zan tafi hjy sai dai idan na dawo shi kuma ai zai dawo gidan nan zamu hadu dashine ai ni zai nunawa kudi har yaushe yai kudin nasa shi .
Ko yau din nan yayi dai ya wuce raini a garesa da kayan sa hjy ta bata amsa murmushin karfin hali mami ta sauke a fuskan nata ta fice daga dakin.
Nasan idon ki biyu yar nan bayan wuya sai dadi insha Allahu wata rana idan an daure sai labari.
Dagowa nayi ido shabe shabe da hawayen wahala ga ciwo ga tashin hankali a lokaci daya ya dameni.
Don ranan gaba daya wanan zancen ya hanani shakat a rayuwana don ko makarantar ban samu zuwa ba a ranan ke nan.
Kamar yadda hjy ta fada na mike tsaye da kyat na nufi bandaki ruwan zafin dana samu a heater na kunna ya dan taru na wasa a jikina.
Na fito na shirya a cikin wani blue din dongon rigan English wear mai adon stonen fari a gaban shi.
Fuskana ya koma fayau a dan lokaci guda bana jin karfin jikina ko kadan zama nagi gaban abincin karyawan dake gaban hjy na zuba ido .
Kici abincin mana ta fada a daidai lokacin na dago fuskana dake zubo hawayen dana kasa tare su a lokacin.
A bazata naji muryan hjy na fadin ki daina kuka nima wanan abin ya fara firgitani a gidan nan ki shiya kayan ki kaf zuwa gobe ki koma gaban iyayyen ki kowa ya huta.
Kada azo matsalan yazo yafi wanan abu ya taru ya rikice a lokaci guda ta yadda ba za a iya gyaran sa ba har idan kina da rana a gareta zata gani nan gaba.
Shi kuma ya tafi ya nemi wace uwarshi ke son ya aura din mu gani yanzu kici abinci ba a ciwo da rashin ci ko kadan ne.
Hakana na daure ba don ina so ba na tsakuri a bincin zuciyana yana cike da damuwa kala kala don a gaskiya naso duk wani cin fuskan su mami gareni in daure in karbi kwalin karatuna.
In yaso daga baya in nuna ni gida nake bukatan komawa gaban iyayyena yafi mun kwanciyan hankali.
Sai dai a yanzu kan banda sauran zabi fiye da barin gidan mami din gara in hakkura da karatun nan tunda abin har yakai ga dafa min sata abinda ban taba yi ba a rayuwana.
Gobe kafarki kafata a garin nan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login