Showing 90001 words to 93000 words out of 191310 words
Chapter 31 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
waya kike fadan wanan maganan haka don duk abinda kike fada yana jin ki tun dazun don wayan sai yanzu aka kashe ta.
Sai jikin ta yai sanyi ta juya tana fadin ke ki bari don Allah dama wayan a kunne take ashe salma tace wallahi shi yasa nake fada maki ku fita harkan yarinyar nan ku kyaleta ba kuji.
Zeey yar mami kin gama wayan ki miko min muryan ya jalal ne daya dawo yake fadan haka daga kofa sai kuma yai shiru yana binsu da kallo lokaci guda.
Ina sharan hawaye nake miko mai wayan tare da fadin nagode duk suna tsaye suna kallon mu a wajen lami tace haka kawai kinzo kin dafawa yar mutane sata ba gaira ba dalili kina neman tara mata mutane ki kunyata ta.
Na fada maki shi ya kawo mata wayan yanzu muna aiki a wurin nan amma bakiji ba.
Ba dole in zargeta ba ta fada tana watso min wani kallon tsana daga inda take tsaye Rufaida kuma wani irin kallo mai nuna matukar tsana gareni take jifana dashi kafin tace.
Ya J din kike waya dashi a boye ashe shigiya mai bakin sihiri kin rantse sai kin sace mai zuciya a gidan nan ko to tsaya kiji .
Ya J ba sa, an yin ki bane gaja irin ki yar kauye idan ko ba aikin asiriba me ya gani a jikin ki yake wanan haukan haka akanki .
Jeki ki tambaye sa ai dan uwan ki ne don me zaku ga laifin yar mutane a banza ga mailefin daya nace mata hjy tsohuwa ta fada daga bayan su don layin jalal daya kira yake fada masu hankali tashe abinda suke min a kitchen din.
Hjy bashi keda laifi ba wanan dince mai laifin ita da batar aika mai da asiri ba ke rufaida ki shiga hankalin ki dani kada ki kawo min diban albarka a gaba wurin nan.
Ba kunya har kike maganan asiri haka a gabana yaushe kika san wani aikin asiri can idan ma shi kuke tunane ai da asiri tai masa daba hakan ba.
Da sauri ta dago ido tana kallon hjy din tace eh da idan ya zare a gidan nan baijin assh a kanta wanan ake kira da asiri.
Wanan ko kauna zallasa so da kaunane nata yaja hankalin shi har don sa ya rufe ya gama mutuwa a kanta ta yadda bai iya jin kiran kowa a yanzu.
Mami dake kwance salma ta kirata ta fito da dan saurin ta zuwa kitchen din ta samu hjy na yanka sababi a kofan shiga kitchen din.
Tsaye take bata san abinda ke mata dadi a wurin ba sai faman tunane take a ranta ita kan ta daukowa kanta jidali da hannun ta.
Ita kan dame wanan abin yai kama me jafar dinta ya gani gun wanan yar haka ya mace a kanta ya hanata sakat a zuciyar ta yan kwanakin nan kan wanan magana.
Wai me ya kawo wanan zace mami ta fada daga bayan mahaifiyar nata inda take tsaye.
Mami wanan munafukan ne na kama a kitchen yanzu da wayan su jalal a hannun ta shine na zata satowa tayi take waya dashi nake mata magana hjy ta taso.
Dawa kike waya zeey ya akayi wayan su ma yazo hannun ki har kike waya dashi.
Diyan ki zaki tambaya wanan don su suka bata wayam ba sata tayi ba a gurin su hjy ta fada a hasale ta juya wurina tana fadin fito mu tafi daki ba zan barki a nan ba tunda basu da imani.
Daga mami har yan matan dake tsaye su biyu suka dago ido suka kalli junan su .
Ina tsaye rakube a jikin bango ban ko motsaba don tsoro naji mami tace ba dake ake magana bane kinyiwa mutane tsaye haka.
Na dago matacciyar kafata daya gama sanyi da sarewa na fara dan tafiya nazo na ratsa tsakiyan su na fice daga kitchen din ina jin wani iri a zuciyata sosai.
Nazo wucewa gaban mami dake tsaye a kofan naji tana fadin ku fito daga kitchen din nan kuma da tada zaune tsaye kuke wallahi ina ruwan ku tunda ba wayan ku ta dauka ba.
Da kyat naga dakin don nisan da yai min lokacin ina shiga na zauna daga kofa na fara rera kuka a fili hjy na shigowa dakin tana mitan zancen.
Nace hjy don Allah don so da kikewa Annabi ki roki mami ta mayar dani gidan mu hannun iyayyena .
Ba sai ta rokeni ba ma zeey nima wanan abjn ya fara isata hakana don haka ki shirya gobe a mayar dake gida.
Mudai shirya a maidamu gida zaki fada don ba yar nan kadai zata tafi a gobe har dani yar kauyen uwar yan kauye zamu tafi kafanta kafana a gidan nan goben, har gaban iyayyen ta zan kaita in yaso dan naki yaje gurin iyayyen ta ya nemeta idan yafi maki sauki.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣7️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERI GARE KU YAN UWA MUSULMAI ALLAH YA BAMU WUNI LAFIYA AMIN, , , , ,
Jin abinda hjy ke fadi yasa dole na daina kuka don ba zanso nayi sanadin mami da mahaifiyar ta arayuwana ba don na samesu cikin so da kauna iri ta da mahaifi a tsakanin su.
Ni na bar shiri sai ga tsohuwar ita tana hada kayan ta wai ita gida zata bata kara kwana gidan mami.
Hakan ya tayar da hankalin kowa a gidan don mami har kasa take tana ba hjy hakkuri hjy ko sai fada take tana fadin.
Sam bazan zauna inga wanan cin fuskan da yaran ki kewa yar mutane ba haka idan ke kin kasa da ita ni zan tafi da ita can kauyen mu in yaso shi Jafari yazo gurina ya nemi auren ta.
Kin dauko amana dadi dadi kina riko tsakani da Allah ashe rikon naki ga yar baikai ciki ba da har dan ki zaiji shawan hada iri da ita ki fito kina fadin baki yarda ba don ita din ba diyar kowa bane a kasan nan.
Gasu nan birjit a gari dan naki yaje ya zabi daidai dashi a kadarta yau Aisha ce dan tallakawa ya fito nema ashe ba zaki iya bada aurenta ba ga wanda take so ?
Don kawai yanzu kudi ya bude maki ido kowa kuna kallon shi a mutumin banza koko samun abokai yan duniya dakikayi ne yanzu ya sauya maki yanayi.
Idan ma hakan ne sai kije ki aura mashi wacce duk kike son aure mai din ita kuma wanan din zan tafi da ita gurina in sakata karatu idan ina raye wata ran sai kince ba ita bace a gidan nan.
Kuma ki sani koda danki zai mutu ne idan yazo ba zan bashi yar nan ba muddin na bar gidan nan da ita.
Inda nake ta kalla tana fadin tashi muje yar nan nasan dai ko ban san kowa a garin nan bazan kwana a waje ba yau zan samu na Allah da zasu duba tsufana su tausaya min.
Tana kokarin sungumar jakkan kayan ta daga saman gado inda yake ajiye mami tayi saurin dafe jakkar tana fadin hjy don Allah ki rufa min asiri a garin nan kada kije ko ina gwiwa biyu nakai kasa tare da daga hannaye biyu sama ina fadin.
Hjy don girman Allah kiwa mami hakkuri karki fushi da mami ba laifin ta bane laifin zuciyane.
Da yau danta bai bijiro da wanan zancen ba da mami batai fushi dani ba har gobe mami uwace a gareni mai mutunci da kima a idona.
Bazan taba mance mutuncinta a gareni ba don Allah kiyi hakkuri ni in tafi ko mami da yaran ta zasu zauna lafiya.
Hjy ba zan biki ba zan koma gidan ubana in zauna duk abinda Allah yayi min mai kyaune a rayuwata Allah ne shedata wani kalami na soyayya bai taba hadani dasu yaya ba a gidan nan wanan yana daga cikin kaddaran rayuwata.
Don Allah hjy kiyi hakkuri ki zauna a cikin gatan ki kada ki fushi da mami sabodani kada laifin hakan nima yazo ya shafeni watarana.
Ina fadin hakan na fashe da wani irin kuka mai tsanani na mike tare da nufar wardrobe inda kayana yake cikin jakka a jere ina kokarin daukan jakkar.
Takwara ina yanzun kika gama bani hakkuri akan uwarki idan nayi hakkuri ke kuma ina zaki a cikin daren nan .
Ko so kike in fasa hakkuri da uwar taku mu tafi tare kafata kafarki mubar gidan nan a yau din nan basai gobe ba.
Hjy ba Anchau zan tafi yau din ba zanyi kokari in kai kaina gidan anty safiya har kashe gari ta sakani mota in koma gida nufina ke nan muddin barina gidan mami zaisa ta samu sallama tsakanin ta daku.
Ba zaki bar gidan nan ba koda bana raye sai idan aure ya rabaku da uwarki kamar yadda aure zai rabata da yarta Indo.
Muryan mami ke fadin ke zeey mayar da kayan nan ki fice daga nan ki ban wuri da hjy kije gun su kande ko dakin Aisha ki jirani.
Mami ta bani umurni da hakan da sauri na juya na bar dakin nan na barsu tare da mahaifiyar ta na nufi gurin su mama kande na zauna.
Sun dade da mami da hjy a dakin har bayan magariba san nan salma tace dani hjy tana kirana a daki.
Na mike na tafi ina addu,a a raina Allah yasa sun yake hukuncin in koma gidane gaban iyayyena zaifi min wanan zaman rashin yancin kai da banda shi a gidan mami yau har ni zainab Nazifa ta dafawa satan waya.
Hajiya ta idar da sallah har isha,i ina shiga da sallama fuskan tar a kaina tana son ta fahinci halinda nake ciki take tambayana da nayi sallah na bata amsa da nayi tun dazun hjy.
Zauna ki zuba muna abinci ta fada kai tsaye dai umurni ta bani babu daman yin mussu gareta ke nan.
Itama ba wani cika mata nayi sosai ba na dai zuba kadan kadan sai dai nawa din yafi zama kadan don nasan ba zan iya cinye wanda ma na zuba din ba.
Sai faman cakulan abincin nakeyi cikin sanyin jiki itama dai hjyn haka dai take kokari tura abincin a bakin ta can naji tace kada ki yarda in hada nawa baki karasa cinye wanan dan abincin da kika zuba ba kamar za,abawa yaron goye.
Dole na fara tura abincin da sauri ds kyat nake hadeshi gaba daya raina babu dadi a lokacin har na samu na gama kamar yadda ta umurceni dayi.
Ba zancen hira garemu sai kowa yayi shiru a dakin dan dama hjy ma takan dan jefo min magana jefi jefi.
Washegari aka tashi da shirin tafiya kamar in dora hannu akai ince wayo ni Allah don banson inyi nisa da gida kuma.
Dan dama nan na rike sunan unguwar da muke dana su anty safiya don bam manta da sunan unguwar ba har yanzu a raina.
Ina ji ina gani har aka fara fadin a fito da kayan da za a wuce dashi a mota don masu mota zasu rigamu tafiya nake gani.
Jakkunan kayan mu gaba daya an labta su a mota hakan yasa naji raina ya kara baki nasan yanzu kan zuwa ba fashi gareni.
Hjy ta aikeni dakin mami don in tuna mata zancen maganin ta da za a saya mata nan kaduna.
Ina gab da shiga dakin nake jin muryan mami na fadin saida nace kada ku sayo ticket da zeey mota zatabi ita dasu kande baku maganata ba sai da kuka sayo.
Ba laifin mu bane mami ya J yasa mu saya mata kinga ko ba zamu ce masa a a ba tunda kudin sane.
Gulman ku zai ciku daku har jafar din in dai akan wanan yarinyar ne ido na zuba dani da jafar din a gidan nan za,aga waye zai sare a karshe.
Jikina ya sake yaraf kamar kayan wanki inaji kamar in juya kada in shiga dakin a lokacin sai dai na ba zuciyata sanyi na fada dakin da sallama.
Duk suka juyo suna amsa min shigowana ya basu daman sulalewa daga dakin suka bar mami tare dani ina fada mata sakon da hjy ta aikoni.
Naji ki fada mata za a saye na daga don barin dakin sai naji ta dakatar dani ta hanyar kiran sunana.
Da sauri na koma na tsuguna a inda nake tare da dukar da kaina kasa ina sauraren abinda zata fada min a lokacin.
Mami ta dan dade tana kallona na dan wani lokaci kafin ta bude baki ta soma magana dani.
Zeey ina son ki saurareni dakyau kiji abinda zan fada maki kaina gyada ina wasa da yan yatsun hannuna dana hade a wuri daya ina saurenta.
Ba zan taba bari ki bar gidan nan ba koda hjy bata nuna hakan ba don in taimakeki ki taimakeni na raboki da iyayyen ki zuwa nan.
Saidai zanso kiyi nisa da duk wani dana bawai jafar ba kwai a a ina nufin gaba dayan su muddin kina son mu zauna lafiya dake a zaman mu.
Zancen karatu kuma da mun koma abuja zan sa a nema maki wani makaranta gwaunati ki karasa karafun naki a nan.
Saboda haka in kinyi abinda na fada maki kiji dadina idan kuma kinki to ina mai fada maki zeey zaki kwammace dama baki sanni ba a duniyan nan.
Na riga nagiwa jafar mata amma saboda ke yana kokarin ya bijire min kan umurni na don kawai ya nuna min shi dan zamani ne.
Mami kiyi hakkuri in Allah ya yarda zan kiye ni ban taba magana dashi ba kuma bazan taba ko a bayan ki mami.
Shike nan zeey zaki iya tafiya mami ta fada ba sakin fuska a tare da ita zuwa gareni a yanzu haka na mike na fita daga dakin.
Karfe biyun rana muka fito mami tana makale da yan matan ta dake mata sallama mu kuma muna guri daya dasu ya jalal da hjy sai Aisha dake daga gefen mu tsaye tana sana,an ta da waya.
Ba wanda ya kula da yai min sallama kamar yadda suke sallaman su hjy da su jalal dan dama salma dace zeey za a tafi ke nan na danyi dariyan yake ina fadin sai mun dawo anty salma tace ko sai munzo ba.
Haka motar mu ya daga kamar su jawoni su fidani daga cikin motar yadda suke watsa min harara daga sama har kasa kuma kowa ya kula da hakan.
Karfe hudu duk muna cikin gidan mami na Abuja da farko mami taso raba muna daki ni da hjy don tace naje daki daya zamu zauna dasu kande a nan.
Sai hjy tace ni kuma na zauna dawa idan kin kaita can kinsan ko a gida da yaran yayan ki nake zama ai.
Don haka barmin ita mu zauna tare kawatace ko banza tare muke kashewa mu bisa a dakin mu daga ni sai ita.
Haka yasa na koma da zama a dakina dana bari da farko kafin mu wuce kaduna don yanzun ma a nan zamu zauna da hjy din.
Mami bata da lokacin zama gida tare da mu karfe taran safe baya mata a gida don hakane nake tashi da sassafe nai mata aiyukan dana saba mata a dakin ta harta shirya ta tafi.
Kamar yadda mami ta canza min hakan nima nake canza don a gurguje zan karasa aikina kafin ta fita na bar mata dakin sai idan ta gama zata rufo dakin ta kawo makulli gurin hjyn ta ta fice.
Satin mu daya da zuwa wani yammaci muna zaune da dare a falon dukan mu ya mamud ya shigo muka shiga gaida shi da dawo yana amsa muna.
Ina zaune kusa da kafan hjy naji yana fadin mami monday fa yarki zata fara shiga school don na samo mata makaranta a nan garin.
Da bakin wa kayin wanan mami ta fada a daidai lokacin da nake murnan hakan ina kuma gode masu a raina sai naji wanan furcin nata a bazata.
Gabana ya yanke ya fadi lokaci guda naji taci gaba da fadin ko akwai wanda ya kawo min ita gidan nan ne a cikin ku da kuke nuna min gaba gadi game da yarinyar nan.
Meye gaba gadi cikin wana zancen iyami ina taimaka maki yayi kan abinda baki samu lokacin yin sa ba kuma nautin kine kiyi hakan.
Ko haka yar taki zata zauna a gida ita bata karatu ta taimaki rayuwan ta nan gaba tunda a zamanin nan kome ka zama idan ba wanan karatun baka cika cikkaken mutum ba a idon jama,a..
Hjy kikan so