Showing 183001 words to 186000 words out of 191310 words
Chapter 62 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
yana kokarin kashewayan nasa lokacin.
Ki tafi ya bada amsa a dan hasale yana kashe wayan shi sai bin wayan nayi da kallon mamaki kamar shine a gabana.
Abin mamaki kwana biyu dayin wanan wayan dashi sai ga wani kiran nasa ya kara shigo min dauka nayi da mamaki ina bin wayan da kallo tare da tambayan kaina wani abu ya samu kuma yanzu yasa ya kira wayana.
Don dai na fahinci shi baya kirana sai idan akwai wani dalili magana da zai sa ya kirani din zai kira layin nawa ina dauka da sallama naji muryan shi yana fadin.
Ke ki shirya kuje asibiti ku gaida hjy samu,naka tana nan an kawota asibiti jiya tana tambayan ki .
Innalillahi nace kafin in tambaya cikin muryan dake shirin sake kuka ina fadin yaya meya sameta da sauki jikin nata ko ?
Idan kije zaki gani ya fada yana kashe wayan sai nabi wayan da kallo a rude don iya kacin maganan ke nan daya fada min.
Banyi sanyi a gwiwa ba na fada wa fadila muka shirya a gurguje don zuwa duba jikin hjy din duk da ina fargaban haduwa da mami a wanan lokacin.
Ba yadda zanyi don dole in tafi koda bai umurce da haka ba don hjy tafi gaban haka a wurina don nima a matsayin jika makusanta ta daukeni a zuciyar ta.
Abinci lafiyayye da mara lafiya zata bukata da sauran abin sha duk anty fadila ta shirya wanan muka fito driver yana waje suna jiran mu tare da wani security daya.
Dukkan mu uku baya muka shiga munsha kyau sosai damu duk da asibiti zamu tafi gaida mara lafiya din.
Ba wanda yai magana a cikin mu ido kawai muka zuba masu sai gashi sun kaimu har asibitin da aka kwantar da hjy din.
Bamu sha wani wuya ba don komai na zuwan mu kamar a tsare yake busa umurnin shi a wurin su din don yai masu bayanin komai kafin mu fito.
Gabana yana faduwa sosai duk da a cikin dan dakewa nake saboda zaunar dani da fadila tayi ta tsara min kkmai.
Dakin maikyau kamar mutum a gidansa yake fadila nagaba ina tsakiyan su muka shiga dakin da sallama a bakunan mu.
Mami ne saman gado zaune sai Aisha dake gefe da wayan ta a hannun ta tana duba har yanzu wanan bakar sana,an nata yana nan mata ashe Nuriya kuma da yaranta suna saman kujera suma suna nasu harkan na daban.
Amsa sallaman sukayi batare da sun san ko suwaye suka shigo ba a lokacin sai daga baya da suka gane mune naga mami din ta kawar dakai ga duban mu.
Gaida su mukayi a bisa al,adan bahaushe idan yaje dubiya ya samu mutane a gurin ya fara gaudasu tare da tambayan jikin mara lafiya din.
Ba yabo ba fallasa suka bamu amsa wanda Aisha ce ta iya amsa muna din a lokacin ba wanda yai muna nuni da wurin zama don haka muka tsaya a tsatsaye daga dan nisa kadan dasu.
Ba wanda ya kara bi ta kanmu muna tsaye saiga security din da mukazo dashi ya shigo dakin rike da basket din abinci da sauran tarkace.
Yana gaida su da tambayan mai jikin mami bata samu amsa mai ba take tambayan wanan kayan fa a cikin daure fuskan ta .
Yace madam ne ta zo dasu duba mara lafiya ku koma dasu ta fada a gimtse fuska babu sauki sai ga ya mamud ya shigo dauke da ledan magani mai tambari asibitin a hannun shi.
Daga kofa yaji abinda mami din ta fada ya cewa security din ya aje tare da fadin zainab ashe kun shigo yakuke ya gidan.
A dan rakube na amsa mai tare da gaida da tambayan ya maijiki yace taji sauki ko dazun da safe saida ta tambayeki ai.
Kai mamud nace a fita da kayan nan kace a ajesu koda matsiyaciya nake banga abinda zai kaini cin abincin yar yaudara ba ai.
Komai idan na wa yan nan ne bazan taba karban shiba ni haba haba mami haka bai dace ba wallahi.
Zainab fa tana da daman zuwa nan ta kawowa hjy a bu don yanzu itama she is part our family ai tunda danki ke auren ta nagani.
Zainab din tazo ne hjy dake barci ta fada kamar a mafalki lokaci guda shi ya amsa mata da eh hjy ai gata a tsaye ma akanki.
Hannu hjy ta miko min tana fadin yar nan ashe da rabon kara ganawan mu zo kusa dani ki zauna tana kokarin yunkurawa daga kwancen da take.
Da sauri na karasa bakin gadon ina fadin hjy ashe baki da lafiya hakane wallahi ban sani bane sai dazun nake ji.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
5️⃣6️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAR UWA UBANGIJI ALLAH YA KARA MUNA IMANI YASA MU CIKA DA KALMAN LA,ILLAHA ILLAH MUHAMMADAN RASULLILAH ALLAHUMA AMIN, , , ,
Hannuna ta rike na wani dan lokaci tare da sauke idanun ta gareni tana fadin ance mijin naki baya kasan nan ashe ya koma inda yake ke nan.
Ganin gani kusa da mami a inda take zaune har kamshin jikina yana dukan hancin su daga ita har Aishanta.
Yasa mami jin wani irin tsana na ya kamata tundai data dubu yabayina gaba daya na canzawa sanin da tayi min a baya can.
Hakan yasa ta mike dan barin dakin ga baki daya ranta kuma a bace da abinda idonta ya gane mata game dani din lokaci guda .
Don a kullun zata ganni sai taji tsana da take min yana kara karuwa a zuciyata duba ga yadda danta ya gyarani cikin dan kankanin lokaci kadan.
Ina kuma zaki hjy ta tambaya a cikin yanayi zafin ciwo har lokacin hannuta ya rike da nawa take fadin.
A zuba min abincin da zainabu ta kawo min inci tana rufe baki Aisha da kanta ke duke saman wayan ta tace kai amma hjy nan dazun nan fa aka gama fama dake kici abinci kika ki ci.
Yanzu kuma kice wai a zuba maki wanan da baki san ma komeye a cikin sa ba don gulma da iya yin ki na tsofi.
Uwarke ce gata gabana yar iyayi a zuba min abuncin gidan jikana in ci inace dazu da abinfa mamuda yakawo min na karya dashi.
Sam basu ji dadin wanan maganan tsohuwar ba a lokacin babu yadda zasuyi dole aka bude abincin a lokacin sai kamshi ya bude dakin lokaci guda.
Ya mamud ne ke fadin zako taci ko don wanan ganyen da akai amfani dashi don alaihu ne da anty zanci kaidai da albarka hjy ta fada a hankali.
Ina kallo don keta Aisha ta zubo mata da yawa tana wani toshe hancinta kamar maijin warin abincin a hancinta.
Da sauri anty fadila ke fadin kai ina zata iya cinye wanan abinci haka mai yawa ai saidai dan kadan yanzu tunda bata jin dadin jikin ta.
Ban iya bawa mutum abu kadan ba ta fada a dan hasale tare da nufar hjy da abincin bayan ta gama fadan bakar magana ga anty fadila din.
Da kyar hjy ta dan tashi zaune tare da taimakona a daidai lokscin da mami ta fake ga waya ta fice daga dakin ke ban.
Fitan ta yasamu sakewa don har ajiyan zuciya na dan sauke a hankali don naga ta fice daga dakin hankalina ya koma a kan tsohuwar dake jin jiki a lokacin karfin hali kawai takeyi a yadda take din.
Mun dade a zaune kafin mami su shigo tare da kawayen ta su uku dakin wani kallon banza suke bina dashi hakan yasa na kara shan jinin jikina sosai.
Sannu sukaiwa hjy din tare da fatan samun lafiya a gareta daga nan suka buge da hira wanda yai kama da haibaici a gareni.
Muryan hjy ne daga kwance take fadin kowa dai ya iya wanke allonsa sai bangon ya tsage kadangare ke samun wurin labewa.
Kai mutum bakai kayi kanka ba balle kayi wani shi dan mutum dama ba abin rainawa bane a duniya wata dan hakin nan daka raina wata rana yazo ya tsone ma ido.
Shiru dakin yayi na wani lokaci kafin dayar matar da tun dama na santa a gidan mami din ta fara mikewa tare da fadin babba Allah ya kawo sauki tare da aje mata kudi gefen gadon ta ta bar wurin.
Kusan duk haka sukayi suna ficewa daga dakin kafin mami ta mike tana bi bayan su a can waje suka tsaya suna gulmana .
Ba komai suke fada ba sai cewa da matar nan ta farkon fita da tayi daga dakin kai hjy wanan yar ko zaki iyata nan gaba ?
Sai dayan tace aini imani duk ya kasheni gani wanan yarinyar gaskiya hajiya danki yaki sauraren ki a kanta don gaskiya wanan yar matar manyace sak.
Ki duba lokaci guda yadda yarinya ta sake a baki daya kamar wata da wani a kasan nan ina ga ta kara nan gaba don ba iya nan zata tsaya ba.
Humm bari kedai hjy dada ni kaina abin yana ban mamaki sosai a raina canzawan wanan yar a cikin kankani lokaci haka kamar abin hadin baki.
Don yanzu ma baya ko saurarena akanta dana dauko mashi zancen zai nuna min baya so shifa matar shi yake so .
To ba,a barshi banza ba hjy ina kuwa zai saurara maki akanta yana ganin wanan a tare dashi ai ba zai saurare ki ba.
Ni ai yanzu matsalata hjyce don naso yi masu koran kare a asibitin nan sai dan bakin nan hayaniyar shi ya tayar da hjy daga barci da yau na nuna mata iyakana a wurin nan.
Kai da kin barsu dayan matar da batayi magana ba tun fara zancen gaba dayan su kallonta sukayi lokaci guda.
Taci gaba da fadin aurene dai ya riga da yayi shi don haka nidai naga kiyi hakkuri kawai ki bar yara nan su zauna lafiya a tsakanin su tunda kinsan halin wanan yarinyar tun farko.
Ki duba fa ita matar namuda fa bata gaida kowan mu ba har muka fito dakin nan yanzu ina laifin wanan din da har kasa ta gaidamu tunda tasan mu din yaya muke dake.
Amma dai hjy karima zancen nan naki baimun dadin ji ba wallahi akan me zaki wani ce ta barshi da matar sa wa zata nuna a matsayin mahaifin matar shi ranan da hakan ya taso.
Kai hjy saudat kina wani zance wallahi yaushe har haka zai taso din kowa fa da ubansa yake tunkaho komai lakacewan shi kuwa .
Nidai a wanan zancen hjy maryam hakkuri zan baki kiyi hakkuri ki zauna lafiya da yarinyar nan kada aje har girman ki yakai ga faduwa a wurinta wata rana don zuciya bata da kashi.
Daga haka ta fara takawa zuwa wurin motar ta inda driver ke jiranta su tafi ba tare da ta tsaya koda yin sallama dasu ba.
Muyi sallama dasu don ba fuska a garemu da zamu dauki lokaci a wurin su don haka muka fito don mu tafi bayan hjy din ta dan samu barci a lokacin.
Ashe da daren ranan batayi barci da dadi ba haka yasa washe gari ya jafar yanke shawaran zuwa Nigeria din don hankalinshi ya tashi da yadda ake fada mai ciwon nata.
Ban san da zuwan shi ba saidai nayi sa,a mun aika da breakfast da abincin rana asibitin duk da mami tayi magana da aka kai na safe din amma bamu fasa aikawa dashi ba.
Don ko washegarin da jikin nata ya rikice mun tafi asibitin mun duba jikin nata duk da mun sameta tana barci a lokacin.
Har muka fito kuma bata falka daga barcin ba sai ya mamud ne yace zai fada mata munzo idan ta tashi kuma ya fada mata din don da aka kai abincin dare take fadin tana gaidamu gobe akawo mata abinci da wuri don abincin gidan mu take iyaci nasu mami yana da yaji sosai.
Can cikin dare muke jin ana dokan kofa kusan tare muka fito lokaci guda da fadila saida ta tambaya yake fadin shine ta bude kofan.
Ta bude da sauri ya shigo muna mai sannu da zuwa ya karba muna yana kokatin shigewa part din shi yar jakkar hannun shi aka shigo mai dashi ciki na karba don in kai mai daki.
A tsaye na sameshi a dakin yana kokarin cire kayan jikin shi sama sama na gaiyar dashi na fito saida safe ne ya fice zuwa asibitin .
Ya dade a can har muka aika da abin karyawa kamar yadda muka saba bawa driver ya kai ko anty fadila taje da kanta.
A can aka sameshi tare da hjyn da sauran yan uwa da sukazo daga kaduna don duba jikin tsohuwar da suke jin ya matsa mata ana fama da ita yana son zai wuce da ita can a dubata taki yarda.
Wai ita tafi son a barta ta mutu a dakinta idan mutuwa ya tashi zo mata ana dai ta fama da ita taki yarda har lokacin da ya dawo gida don ya huta saboda gajiyan dake jikin shi din na tafiya.
Barci sosai yayi daya dawo sai yamma ya tashi don kansa tunda dai mu ba shiga part din mukeyi ba sai idan wani abu ya taso yake kaini part din nasa.
Har mun gama abinci da za a kai har fruit's salad mun hada mata ko zata sha duk wanan dabaran anty fadilace don kawai a burge mami dama wanda ke wurin lokacin.
Fitowan shi sai cewa yayi in shirya mu tafi asibitin a tare duk wanan yana cikin hikimarshi na kawar da idon mutane ne a kan mu.
Hakan bai zama min bako ba a wirina don nasan yakan yi mun hakan idan yana son fita tare dani wani lokaci kafin ya tafi.
Dakin makil yake da yayan hjy din da sukazo zasu kuma kwana a nan kashe gari su koma wurin su biyar ne mata sai maza ukku.
Ana faman hayani da dararaku kamar ba mara lafiya a dakin ya shigo ina biye a bayan shi fuska murtuk don halin daya samesu din a ciki.
Suna gaidashi yana amsawa sama sama bai tsaya ba sai bakin gadon da hjy take kwance mama Ramaru tana kusa da ita suna da magana.
Yake fadin hjy na fada maki ki yarda mu tafi a kaiki asibitin can a dubaki ki daina wanan wahala haka don Allah.
Budan bakinta sai cewa tayi bazan tafi ba sai idan da matarka zamu tafi nima wanan kafan yana damuna wallahi.
Dakin ne yayi tsit sai mami da tace aiko tare da Ramatu zaku tafi hjy tunda dai Ramatu tafita sanin komai ai .
Ta yaya zamuyi tafiya zuwa gidan shi matarshi na nan idan ba da ita zamu tafi ba saidai a fasa wanan tafiyan kuna abu kamar baku da lissafi a zuciyar ku.
In dai wanan ne ai mai sauki ne har in kin yarda din zaki tafi yaya mamud din ya fada yana dan dariya.
Ya juyo gareni yana fadin zainab ko ba zaki rakata ba tunda hankalinta yafi kwantawa da tafiya dake din can ?
Dan murmushin yake na sake a fuskana mami tace dama ai burin ta ke nan ita tunda iyakarta kaduna Abuja dama.
Yanzu ko abin nema ya samu ga ba saban ba ai sai tafiya hjy rigima kawai kike son dorawa mutane kan tafiyan nan.
Wani iri naji kamar hawaye zasu zubo min lokaci guda don yawan muzantanina gaban mutane da mami din ke mun .
A cikin dakewa na daure Allah ya taimakeni hawayen bai zubo min ba sai dan dukar da kai danayi kasa sauran mutanen dakin duk sun zubo min ido a kaina.
Ji nayi ya riko hannuna yana fadin mami yarki ai ta waye yanzu ba kaduna ba ko Abuja ba ko inama zata iya shiga yanzu ai ya fada yana kokarin rugumeni a jikin shi cikin rashin damuwa da duk wanda ke dakin a lokacin.
Kai jafar a gaban mu kake kokarin rugume matar ka don ka saba da dabi,un ku na turawa a can mama Ramatu ke fadin hakan tana mashi dakuwa.
Mama ai matatace ko ina ina iya rike abata wanan shike nuna irin son da nake mata ai kuma ku sheda koba haka ba besty na ?
Ya dan rugumo kafadata zuwa jikin shi yana dan murmushin da shine iya dariyan shi a hankali na lumshe idanuwana don irin abinda naji a lokaci guda.
Kada ka bata muna yarinya din nasan zainab na da kunya ita mama ko kin mata ita din matanane a yanzu ?
Kai jafar kaikan a Allah shirye ka yanzu kan sai a barka inda