Showing 159001 words to 162000 words out of 191310 words
Chapter 54 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
min alaman a,a tare da shan jinin jikin ta a yadda na bata amsa din cikin bacin rai don bansan zancen gidan mami duk da ina kwana ina wuni da zancen mami din a raina.
A hankali na zame na kai kwance daga inda nake zaune tsaban tunane sai kawai naji hawaye suna zubo min ba tare da nasan zuwan su ba.
Dafanin da akayine yasa na dago kai anty fadilace a tsaye kaina tana kallona yadda hawaye ya bata mun fuska lokaci guda.
Badai ciwon bane har yanzu ta fada a cikin kullawa tana zama a gefena tare da mayar da hankalinta gareni.
Kafin in bata amsa halimatu dake gefena take fadin yayan mu bansan ranki zai baci ba da bance muje gidan hjy din ba .
Wace hajiyan anty fadila ta tambaya da mamaki a fuskanta a hankali na amsa da mami mahaifiyar ya Jafar.
Anty fadila tace kan me kukai zancen ta har ya kawo wanan hawayen haka ?
Bazaki ba tunda tun farko ta nuna bata kaunar ki da danta kina garin nan kuma ta sani bata nuna kulawanta kan danta ya barki amana a gurin su ba maizube ke fadi daga bayan mu.
Don haka ki nisanci su kamar yadda suka nisance ki a yanzu saboda da talaucin ki ko rashin gata ta nuna bata kaunar danki dake dafarko .
Sai yanzu kuma ke zaki kwashi kafan ki zuwa gidan ta ko zaki kai kanki ne su kara wullakantaki a can .
Ki zauna a matsayin da Allah ya ajeki gidan nan ki bi umurnin mijin ki har sai idan shi ya furta zuwan ki gidan dan mahaifiya ba wasa bace ai amma yanzu kan babu inda zaku tafi gaskiya.
Maizube nima bance zan tafi gidan mami ba a yanzu don nasan mami har yanzu tana rike dani a zuciyar ta.
Duk da ba zan iya matawa da alherin ta a garni ba har gobe don ta dalilinta har na kai hakan a yau da sunan auren danta a kaina.
Maizube tace dani ato ki daiyi wa kanki fada don babu inda zaki tafi don ni bazan zama babban kwabo ba a cikin ku duk da muke matalauta muna rike da mutuncin mu a idon kowa.
Murmushi Fadila tayi tare da fadin hjy maizube ba a hakan ai idan ma har zasu tafi din aiba haka kawai zamu barsu su kadai din su tafi ba dole saida shirin hakan ko ?
Maganin dai kar ayi kar a soma dan ba a san da wace zata tare su ba abar zancen nan har wanda take zama don shi ya dawo kasan nan inma zuwan ne sai su tafi tare dashi din zaifi.
Jinsu kawai nake yi don sam ban amince da zuwan ba nikaina a lokacin don nagama tsiracewa da mami din yadda muka bar gidan tare da hjy a yadda tayi min koran kare a gidan ta harta amince da mahaifiyar ta tabar gidan donni.
Wanan zancen da akayi a gaban Fadila yasa ta dauki wani haske a cikin zancen sai da muka zauna daga ni sai ita take kara tambayana abinda ya faru a tsakanina da mami din.
Shiru nayi na dan lokaci kamar mai tunanen wani abu sai can naji tana fadin zanso nasan wani abu daga bakin ki duk dana dade da gano komai amma zanso ji dafa gare ki din yanzu.
Wani tsorone ya lullubeni lokaci guda na janye na dauki hannuna na dora a fuskana kafi in sauke na dukar dakai na kasa.
Karo na biyu ta koma kiran tana fadin kina jina kada ki boye min komai ki daukeni kamar yar uwa a gareki don ni din a yanzu mai taimakon ki ne zainab.
Wani sanyi naji a raina tare da yarda da ita lokaci guda duk da
Banso fada mata komai ba amma ya zama dole ta danji wani abu a gurguje na dan fada mata saidai ba duka ba don ban san yadda zata dauki zancen ba a ranta.
Bakina ta zubawa ido har na kare na kare fadan abinda zan iya fada mata na zamana da mami da haduwan mu da ya jafar din a gidan mami har na kare sai tace.
Zainab yau zan baki shawara kamar yarda ya da diyarta zata bata shawara ya amfaneta.
Tagumi nayi ina sauraren abunda zata fada min din a lokacin ita kuma taci gaba da kawo min misali na zamantakewa da mutane a duniya.
Yadda mama maizube take nufin kiyi danzun nake ganin bashine mafita ba gareki zainab don ko yaya suka samu matsala a kanki da mahaifiyar shi ki tunafa uwa uwace a gare shi.
Duk yadda kika dauka da zafi ko iyayyen ki suka dauka hakan ba zai taba mashi dadi ba a ranshi duk ko yadda yake sonki.
A sake na ce yanzu yaya zanyi anty don mami ba zata taba yarda dani ba a cikin a halin ta ni kuma na sani auren nan namu nadan lokaci ne dashi.
Tsaki taja tana fadin ki bar wanan zancen do Allah kefa mace ce zainab duk wani abu da ake bukata a mace kina dashi zainab lokacine kawai zai nuna hakan akan ku.
Kedai kawai yanzu duk abinda nake koyar dake ki maida hankalinki ki koya do zama daku na dan lokacine da zaran contrac dina ya kare daku tafiya zanyi in barku a gidan nan.
Yanzu lanbanta zamu nema zaki dinga tura mata sakon gaisuwa da girmawa tare da nuna mata ke din yace a gareta har gobe.
Ya zama dole ki koyi halin kissa da kisisina irin na mata masu son kama gidan su a hannun su yanzu .
Ta yadda zaki iya tunkaran kowa da wanan kalubalin dake gaban ki domin yanzu sai da wanan akan samu riban rayuwa mai dorewa wanan sanyin ba zai kaiki ko ina ba a rayuwa.
Rashin wayen ki ko sanin duniya zai iya haifar da komai a kanki har aci galaba akanki a cikin sauki don wanan shirun da kike ganin tayi irin su hjy da abinda take shiryawa a hakan.
Da sauri na dago kai don jin abinda ta fada din nace amma anty ta yaya kamata zan iya ja da mami matar da ta kafu da komai akan danta dama kowa ?
Murmushi tayi tare da fadin kina kwankwanton hakan ne zainab ai tun damazo gidan nan na fahinci akwai wata a kasa tsakani ku.
Naso tafiyan ya tafi a hakan inyi aikina in wuce saidai ke din yarinyace mai saurin shiga ran mutum a lokaci daya saboda halinki na sayi da girmamawa ga kowa don baki dauki duniya da zafi ba a yadda na fahince ki.
Don hakane ma kike ganin har abinda ba a ssni na koyar dake ba nake kokarin koya maki don na taimakawa rayuwan ki.
A sanyayye nace anty nagode da wanan taimakon naki gareni in Allah ya yarda zaki sameni da amfani da duk abinda kika koyar dani insha Allahu.
Tayi murmushi tana fadin ya zama dole in taimaka maki zainab don nasan wata rana hakan zai min dadi nima a rayuwana.
Kin ganni nan nasan halin maza kamar yunwar cikkna ina da yara biyu na barsu badan naso ba saboda halin da namiji a yau.
Don haka ba zanga wata mace yar uwana zata fada a halaka ba in barta ta dandani irin ukubar dana sha a baya.
Sau nawa ya kiraki a waya tun bayan tafiyan shi ta jefo min tambayan da ban zata ba a lokacin da sauri na dago kai ina tunanen hakan ?
Bai kirani ba anty na bata amsa kai tsaye do babu zancen boyo yanzu a tsakanin mu kuma tunda ta fahinci komai.
Zai kiraki naji ta fada idan mun fara dana masa tarkon muna mata ai idab yasan wata baisan wata ba zamuyi mai karya baki da lafiya zai zo idan har kina da muhinmanci a rayuwan shi .
Saidai zaki bani goyon baya zaki koma ki kwanta ciwon na kwana biyu do wanan kanwar taki mai shegen surutun tsiya zai iya tambayan ta idan hakan gaskiyane kin sani.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
4️⃣8️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERIN GAREKU TARE DA BAN HAKKURI RASHIN SAMUN UPDATE KO DA YAUSHE DA FATAN ZAKUYI MI AFUWAN HAKAN YAN UWA, , , , , , ,
Ina kwance tun safe kamar yadda ta umurceni da yi hakan din sai dai tunane ya addabi rayuwana yadda wanan wasan da take shiryawa zai kaya muna.
A gogon dakin na bango na duba da karfe sha daya saura na safe tun bayan sallah asuba nake kwance ni ba barci na koma ba don tunane ina kwance a falke ina faman dakon tunane a zuciyana.
Wayana dake gefen gado wanda tun daren jiya na ajeshi da zamu kwanta ban kara bi ta kansa ba ya dauki kiran agaji.
Hannu na mika daga inda nake kwance din na dauko wayan da zuman ganin wanda ke kira layin don ban taba zaton kiranshi bane a lokacin.
Lanba ce ta kasan waje aka kira layin dashi na kurawa kiran ido ban daga ba ina nazari a raina har kiran ya gaji ya katse lokaci guda .
Wani kiran ne ya sake shigowa lokaci guda ina kallon wayan na fitar da sautin kida na kasa dagawa don na farko ban sheda ko lamban waye ba a lokacin.
Na biyu kuma idan na dauka shine mai kirana me zan fada mai don bamu riga da mu aje magana abinda zan fada mai ba.
Jikina gaba daya yayi sanyi a lokacin a cikin daurewa kiran na gaf da tsukewa na kai hannu na danna dauka.
A hankali na kara wayan a kunne na lokaci guda ina sauren mai kiran nawa hello din daya fada a gadarance yasa na fahinci ko waye a layin shidin dai ne ya kira wayan a lokacin.
Ya kara fadin hhy ya kuke me faru dakene dazun fadila ke fada min baki da lafiya tun jiya ko fita daga daki bakyayi.
Saida na tattaro wani karfin hali a tare dani kafin in iya budan bakina nace a hankali cikin yanayin wanda ciwo yake damun sa na furta banda lafiya ne da kyar.
Baki sa lafiya ita fadila me take jira dake a gida bata kaiki asibiti ba ko bata san aikin ta bane wai ?
A hankali na lumshe idona tare da fadi a marairaice cikin sanyin murya ta sani ita dince ma take kula dani yanzun haka na basa amsa.
Ta kaiki asibiti ya kara tambaya ta kaini jiya da yamma na samu kaina da fadin hakan duk da nasan komai karyane shirin hakan mukai masa.
Zan turi maku da sako idan wanan bai isa ba aimin magana ya fada kamar a kage yake da ya kashe wayan shi a lokacin.
Yaci gaba da fadin idan har kuna da matsala da ita zan iya canza wata a samo wace zata kula dake fiye da ita.
Ban san lokaci danace a rude laifin me tayi koda mahaifiyata ce ita ai iya kar taimakon da zatayi min ke nan .
Naji ya saki ajiyan zucuya tare da fadin ta kyautawa kanta don bana son wasa da aiki a rayuwana.
Idan ma laifi ne ai ba ita bace mai laifin don ba itace ta rabani da uwata ba na fada can kasan makoshi na a hankali na dauka ba zaijini ba.
What me kike fada ?
Shiru nayi tsayin lokaci babu amsa daga bakina bai kuma kashe wayan nasa ba a hankali na runtse idona ina sauke numfashi da kyar don gabana sai faduwa yake daurewa kawai nayi a hakan.
Ba zaki magana ba naji ya fada a cikin dan daga murya nace to ai kaine ka rabani da mami kuma ka , , , ,
Look ina wasa dake ne zainab yaushe har raini ya shiga tsakanin mu haka dake ko so kike na bar aikina nan na dawo na zauna Nigeria daku ?
Kit na kashe wayan tare da maida nufashin dake sauka min na tsoro da sauri don ban zaci zan iya fadan hakan ba ni kaina.
Aje wayan yayi daidai da shigowan anty fadila dakin cikin sauri na dago kai a firgice ina fadin anty wallahi shine ya kirani yanzu din na fada ina kallon ta kamar mara gaskiya.
Na sani ta fada tana zama a gefen gadon da nake kwance nima mikewa nayi ganin ta zauna din a dakin.
A haka zamu kamo shi sannu a hankali har hankalin shi ya karkato zuwa gare ki don maza a yanzu sai da kisa da iya zama dasu a cikin dabara.
Na bude baki da zuman magana ke nan aka turo kofan inda nayi shiru maizubd ce ta shigo tana fadin wai nikan jikin ne yau ta hanaki leko waje yar nan ?
Fadila tace jikin ne nima yanzu naji shirun yai yawa na leko ta na same ta a kwance sannu ta fada tana kallona a cikin damuwa da nuna kulawa a gareni.
Na amsa a cikkn daurewa ina kokarin yaye bargon dake saman jikkna wanda ya dameni a lokacin don dole nake kwance dashi.
Ki tashi ki karya fadila ta fada a cikkn kulawa nace zan watsa ruwa kafin na fita yasa suka bar dakin don na samu kintsawa hankali kwance.
Dogon riga mai laushi green mai adon dawisu a gaban rigan zuwa kasan shi na saka a jikina sai gyalen shi danayi dan kwanlin dashi a kaina.
A falo na same su zaune suna kallo na fito daga yanayi tafiyana ya nuna ban cikin dadin rai a tare dani.
Dining na nufa kai tsaye abinci na nan a gurin na diba kuma sai na kasa cin komai don hankalina yana gun yadda mukayi a waya dashi.
Da ido Fadila ke warning dina a yadda nake cin abincin da sauri na gyara sallon cakulan abincin a hankali cikin yanayin yauki da yanga kamar yadda ta koyar dani.
Muna falon har lokacin da halimatu ta dawo daga school tashigo da murnan ta tana kokarin fada min ajiki.
Anty fadila ta daka mata tsawa tana fadin kada ki fada mata yinin yau bata da lafiya gaba daya da sauri ta juinda inda nake zaune ta dan langabe kanta tana fadin.
Yayan mu sannu ya jikin na dan gyada mata kai alaman amsawa gareta ta zauna gefena tana fadin kinga yau tare da yaran gidan hjy din nan muka yi yawo a school.
Wanan akwai ki da iyayi har sai kin daukowa mutane zance a garin nan yaushe har kika sansu da kike kokarin cusa kanki garesu maizube ta fada.
To ba saboda yayan mu nake kula suba ta fada tana turo baki gaba alaman zancen da maizube tayi bai mata dadi ba.
Halimatu tashi ki shiga ki cire kayan ki na fada cikin bata umurni ta mike da sauri zuwa dakin kamar yadda na umurce ta tayi.
Alwala na dauro na gabatar da sallah tare da mika kukana ga sarki Allah wanda yafi kowa sanin dumbin damuwan dake tattare dani a rayuwana.
Kafin na mike na koma na kwanta dan banjin fita falon da ya zame muna wurin fita kawai a gidan don ko haraban gidan bama fita idan ba fita ya kama yi ba.
Amma kuma sai barci ya gagareni a lokacin sunayen Allah mai girma na dinga kira don na samu natsuwa har barci ya daukeni a hakana.
A cikin barcin nake mafalki da ya jafar yana tsaye ya harde hannayen shi yana kallona na tun karo inda yake tsaye.
Saiga wani yazo ya tsaya a tsakanin mu ya bani baya don haka ban samu ganin fuskan maishi ba .
A haka ina kalon su ban samu karasowa inda suke tsaye din ba ina kallo wanan mutumin ya jayeshi gareni ya tafi yana waigena a inda nake tsaye.
Sunan shi na kira da karfi wanda hakan yai daidai da bude idanuwana daga barcin da nakeyi din na falka a razane na gannin a cikin gumi.
Zainab wanan ihun fa Anty fadila ta fada daga kofan tana tsaye kai na dago ina kallon ta a tsorace take fadin nazo zan wuce naji kamar kina ihu na shigo.
Anty mafalki nayi na bata amsa take fadin barci a wanan lokacin baida kyau gashi har biyar na yamma yayi yanzu kina kwance.
Dago kai nayi na kalli lokaci sai na tuna da zancen sallah na mike don zuwa nayi alwala bayan fitan ta na samu fashin sallah yazo min a lokacin don haka na tsaye kawai na gyara jikina na fito daga bayin.
Naso na manta da zancen mafalkin nan danayi saidai abin ya tsaya min a raina sosai har