Showing 54001 words to 57000 words out of 122554 words
Chapter 19 - MR. BELLO Complete Book Hausa Novels by Janafty .txt
ba Sai Da yayi Shafa"i Da Wuturi Har ya Kwanta sai ya Tuna bai Sha Mgungunansa ba Gashi kuma Cikinsa na Kiran Yunwa,Mikewa Yayi ya Zura Takalminsa na Bedroom ya Bude Kofa yaFito Falo nan yaga Aneesa Ta Dunkule Kan Kujera tana barci Har Dankwalin kanta ya Sabule,Kitsonta kanana 2 Step Wanda Anty Aisha Ta mata Suka Bayyana Awaje,kallo Daya yayi mata ya kauda kai kichen ya Shiga ya Dauko Madaran Hollandian Guda Daya da karamin Kofi kashe Wutar kichen din yayi kana ya Fito Har Ya Wuce Zai Shiga Bedroom Dinsa sai kuma ya Dawo Baya Ya Saka Hannu Daya ya Dauki Remot din A.C din Falon ya Rage mai Iska Lokaci Daya kuma ya Rage Wutar Falon Ya kunna mata Dumlight kafin ya Kada kai ya Shiga Bedroom ya Rufo kofarsa yana Sakin karamin Tsaki
Sai da yasha Madaran kana ya Balli magungunar yasha,ya maida Komai bisa Side Drower din gadon kafin ya Shige Cikin Blanket Lokaci Daya yana kashe Hasken Dakin ya Kunna Dumlight,sai da ya kashe Wayarsa kana ya Dora kansa Bisa Filo yana Lumshe ido,Tunanin Abunda Likita ya Fadamai,Ya dawo mai Fadamai Jininsa ne yayi sama Saboda Damuwa kuma baya barci kwana Biyu yayi kokarin Ya Dinga Samun barci Ajiyar Zuciya Ya Sauke kafin ya Runtse idanuwansa Lokaci Daya barci mai Nauyi ya kwasheshi.
Bai Farka ba,sai Wajen 5am Shima Kiran Sallan Mallam Inuwa ne ya Tadashi Domin Dama In bai kira ba Mallam Inuwa ke Kira Watarana ma Har sallah ma yana Badawa,Tashi yayi Zaune yana Mika Lokaci Daya Yana Salati,Wayarsa ya Dauka ya Kunna nan yaga 5 ta Wuce Kafafunsa ya Zuro Zuwa Saman Cafet din Dake Dakin,Takalminsa Dake bakin gadon ya Zura lokaci Daya mikewa Wutar Dakin ya Kunna haske ya Gauraye ko"ina kafin ya Fada Tiolet,Wanka yayi agurguje kafin yayi alwala ya Fito Wardrope dinsa ya Nufa yana Goge Jikinsa da Karamin Towel din Dake Hannunsa,Jallabiyansa Baka ya Ciro Ya saka Da Hula,gaban Dressing Mirrior Dinshi ya Isa ya Dauki Turare yana Fesawa Hanzarin Fita yayi jin kiran Sallah na Biyu Wayarsa ya Dauka Lokaci Daya ya Bude Kofar Bedroom Din ya Fita Yama manta da Wata Halltta Aneesa Shiyasa ya Fice kai Tsaye Daga Falon Batare Daya Damu ba.
Bai Dawo part Din Nashi ba Sai Wajen 6am na Safe Domin yau Mallam Inuwa ya bada sallah Shikuma ya Tsaya yayi karatu,yana Shigowa Falon Cikin Takunsa na Jarumta idanuwansa Suka Mai Tozali da Aneesa Dake Kwance Tana Barci Saboda Dadin Barci Tayi Rigingine Ta matse Lifayanta Awajenta Cikinta Gabadaya Cinyoyinta Suna Waje,Saboda Doguwar Rigar Tayi sama Saurin kauda kai yayi yana Tsaki Lokaci Daya kuma da Karfi Wanda ya Farkar da Aneesa Daga Barcin Datake sha.
Tana Mitsike Ido Ta Hango Wucewarsa Kamar Wani Sarki yana Wani Taku D'aid'ai da kallon Rainin Kallo Ta bishi har ya Shiga Cikin Bedroom Dinshi zai Rufo kofar kenan ya Waigo Suka Hada Ido da Sauri ta Kauda kai tana Sakin karamin Tsaki Ido ya Waro yana kallonta Cikin mamaki ya Fasa kulle Kofar sai ma Fitowa Dayayi yana Fadin"Ke Don Ubanki wa kika ma Tsaki yanzu.." ?Yafada Yana Sakarmata manya Idanuwansa
Saurin Mikewa Tayi tana Raruman Dankwalinta ta Maida Bisa kai Bakin nan ta Tura gaba cikin Ranta tana Fadin"Badai ubana ba Sai dai na Mutum Tunda Uba baifi Uba ba.."Tafada Tana Tura baki,Tsaye yayi yana kallonta Cike da Bacin Rai kafin ma ya Sake magana Ta Dauki Lifayanta ta Yafa ta kama Hanyar Fita Bakin nan kamar ya Fado Saboda Kunkuni ..
Cikin Kuluwa yace"Ke...ke...Bada ke nake Mgana ba..."Yafada yana Maida Hannuwansa Cikin Aljihun Jallabiyansa Ko Waigowa Aneesa Batayi ba ta Fice da Sauri,Numfashi ya Fesar kafin ya Kada kai ya koma Cikin Bedroom dinsa Aransa yana Fadin Yarinyar nan ta manta ni ne Sai na kara Tunasar da ita komai.
Ya Cire Jallabiyan kenan ya Kwanta Wayarsa ta Dauki kara yana Dubawa Yaga Principal din Mkrantam Kwatar-kwashi ce Dauka yayi Bayan Sun gaisa Take Tambayanshi Ashe ya Dawo yace mata Eh Cikin Dariya take Fadin Mallam muna Jiranka fa"Mirmishi yayi kafin ya Fara mata bayanin komai Duk da Bataji Dadin Rashin da GGUSS,tayi ba na Malami kamarsa ba Ammh Tasan ko bajima Dole Mr bello zai Tafi Sakamakon Ko Kudin da Suke Biyansa bai kai mtsayin Karatunsa ba kawai Ra"ayinsa ne Haka Har Sunyi sallama take Tambayanshi da Gaske lbrin Dataji Wajen Dalibai wai yayi Aure kuma Aneesa Bukar Bulama ya Aura.?mamaki yadda Lbrin yakai Mkranta yake bai mata Wani Dogon bayani ba ya Dai amsa mata da Hakane Fatan alheri ta mai kafin Su Yanke Kiran Ya barta Cikin mamaki Duk da Ta san Cewa Babu Abunda Zata samu Daga Bello Saninshi Marason Hayaniya,Daganan Kashe Wayarsa yayi gabadaya ya Kwanta bayason kuma Damu.
*****
Daada na Zaune Tana Lazimi Aneesa Ta Shigo Dakin nata Tana Tura baki Cikin Mamaki Daada Ta Dago Tana Binta da kallo Baki Bude bata samu Zarafin mgana ba Aneesa Tace"Daada ina kwana.."Bata amsa ba illah cemata Datayi.."Daga ina kuma Haka..? Kin manta yanzu ba da bane.."?
Tura baki Aneesa Tayi kafin tace"Yo Daada Nazo yin sallah ne da Wanka.."Dakuwa Daada ta Mika mata tana Fadin"Kinga naki Ja"ira Chan babu Wajen Yin Alwala da Wankan ne..?."Bata rai Aneesa ta karayi kafin tace"Toh wai ni Daada meye laifina Yafa Kulle Dakinshi kuma na Duba Falon ba Tiolet kuma ma ko Akwai bani da kayan Chanzawa..".
Tafada Harda Buga kafa kafin Ta Fice Daga Dakin Tana Tura baki Dayan Bedrrom Din ta Shige Tana Kunkuni,Da ido Daada Ta Rakata kafin ta Sauke idonta tana Fadin"Allah ya Shirya.."Cigaba Tayi da Lazamin ta bata kara jin Duriyar Aneesa ba sai da Tayi Wanka Tayi sallah TaChanza kaya Cikin Atamfa Riga da Sikat batayi Kwalliya ba Shiyasa Fuskarta Tayi Fresh Da Ita Dakin Daadan Ta Dawo Ta Haye gadonta tana Fadin"Allah ya isana Jiya A Kujera na na kwana Duk Wuyana ya Sage..."Tafada Tana Shafa Wuyanta ko mgana Daada Bata mata ba Tana dai Binta da Ido ..
Anty Rahila ce ta Shigo Ita da ya Muktar wanda ke Dauke da Junior Gefensu kuma Hibba ne,Dukkansu sun sha gayu gwanin Ban Sha"awa,Daga gani yau Ya Muktar din bazai Fita ba,Sanda Suka Shigo basu lura da Aneesa ba sai da Suka kariso Tsakiyar Dakin Cike da Mamaki Anty Rahila ke Kallon Aneesa Kafin Ta maida kallonta ga Ya Muktar Shima Wanda ke kallon Aneesa Harda gyara Kwanciya tana lumshe ido ..
Baki Anty Rahila ta Rike kafin Tace"Daada wa nake gani kamar Anee.."Daada tace"Nima Haka nagani na mata mgana tace Tazo yin Wanka ne da Saka kaya,daganan kuma aka Hau gado sai Tura baki take bansanin mata ba Don ko Tankata banyi ba.."Haushi yakama Anty Rahila ta Isa bakin gadon ta Dagamata Duka Lokaci Daya Tana Fadin"Tashi Don Ubanki ki koma Shashen Mijinki kiyi barcin achan.."Mikewa Tayi tana Soshe Soshen Wajen Tana Fadin"Kai Anty Rahila.."Tafada Harda Matse Kwallah.
Daada Tace"Wai ni kayan ma Datake Sakawa ba Maidama yaron chan za"ayi ba..? Ya muktar yace"No Yanzu da Safe Hashim ya Kirani yace Kasim yace Ya barma Aneesa Duka kayan..."Daga Daada Har Anty Rahila Hada baki Sukayi Suna Fadin"Allah Sarki.."Aneesa ko Kuka ta Fashe Dashi Tatashi ta Fita tana Fadin"Allah Sarki My Kasim Allah ya saka maka.."Da kallo Suka Bita kafin Anty Rahila Ta Daga Murya tana Fadin"Karki Dawo Nan ki Wuce ki koma Shashen Mijinki yanzu Jummai zata Hawo muku da Breafast dinku.."Aneesa na Jinta ta mata banza sai da ta koma Dakinta ta gama Kukanta kana ta Dauki Mayafinta ta Fita Bayan ta Kwalama Hibba kira tazo Suka Fita Tare...
Wannan Koran Bai Rufe Kofar Falon ba,Shiyasa Suka Shiga Diret,Ita da Hibba Suketa Hiransu Ita cema ta mtsa Shiyasa ta Kunna mata Cartoon,gefe ta kuma ta kwanta Har Jummai ta Hawo musu da Faranti Cike da kayan karyaewa Dama Yunwa Takeji nan Suka Baje ita da Hibba Suka karya kafin ta tattara komai na maida Kichen,Suna nan Zaune sai ga Anty Rahila da Alheri Sun Hauroma ta Akwatunanta,ko kallonsu batayi ba sai ma Tura baki da take Tana gani Anty Rahila ta Kwankwansa Kofar Bedroom din Bello Sai da ya bata Lokaci kana yataso ya Bude domin ma ganin Anty Rahila ce da kanta in ba Haka ba bamai Shigar mai da Tarkace Daki,Haka ta Shigan mata Dashi Har chan Kurya Wajen Madubin dakin ta Jeramata su Bello dai na gefe yana bata rai bata Tsaya ba ta mishi sallama ta Fice Daga bedroom din tana Fita ya maida kofa ya saka key yana Sakin Tsaki Shi kadai.
*****
Sati Daya kenan da Auren Bello da Aneesa Ammh babu Abunda Ya chanza na Zamantakewarsu,Kullum Aneesa Bata Wuni Acikin Ashashen Bello Daada da Anty Rahila Sunyi fada har sun gaji sun zubamata ido,Wani Lokaci sai yammah take komawa Shashen Sai ta tafi da Hibba da Junoir Kayanta Kuwa Baya barin ma Bedroom din Abude Sai ta mamayeshi ne sai tayi wuf ta Shiga Ta Debo kayanta Kuma,kullum Shashen Daada Take wanka da Cin Abinci Sun Gaji da mata mgana Sun saka mata ido...
Shiko Tundaga Ranar Wata Mgana bata kara Shiga Tsakaninsu ba,Afalo take kwana ko kallo Bata Isheshi ba Shiryan Shiryan Tafiya Kano yake tayi Shikadai batare Da Sanin kowa ba,Ita ko Aneesa Ko Waya ma Dakyar ta samu Ta Kira Su B.kaita Sau daya suka gaisa tayi musu bangajiya Wayarta kuma Tun achan Anty Nafee ta karba Hannun S.jibiiya Sai da Sukayi Waya Take Fada mata batayi Mamaki ba sanin Halin Anty Nafee Mirmishi kadai Tayi Acikin Ranta Tana Jin bakin Ciki Toh Ta Hakura da mai Wayar ma Ballatana Waya,Taje tayi ta kaya...
Ranar da zai Tafi kano Shi ya Tuka Kansa Cikin Daya Daga Cikin Motoci Guda Biyun da ya Muktar ya siyamai ammh basu Taba Dadashi Da Kasa ba,Direct Cikin Mkrantan BUK ya isa Ya karbi Appoiment Letter dinsa yayi Report,Sun bashi gida nan Cikin Mkranta ammh Baya Sha'awar Zama Cikin Makaranta Dat Way ya kira Ya muktar ya sanar mai Shi kuma ya Turamai Address din Gidanshi Dake BUK road, Wanda ko Shekara baiyi Da Siya ba katon gida ne ammh ba Sosai ba Sai dai baida sama flat ne mai kyau mai Dauke da 2 floor da 3 Bedroom sai kichen,kowani Daki yana Dauke da Tiolet dinsa sai Haraban Gidan mai girma da kuma Dakin me Megida,Wanda Ke Zaune yana Tsaran Gidan,Bello ya yaba da Gidan Sosai Bayan sun gaisa da Megadin ya Shiga Ciki Nan ma ya kwana Saboda yayi yammah Da Safe bai Wuce ba sai da ya Leka gidansu Uncle Aminu Suka gaisa da Amminsa kana ya Dawo Abuja Da Shirin Jibi In Allah Ya yarda zai yo parking Zuwa kano,domin ya kosa ya Daina Shakan Numfashi da Aneesa Yana Cikin Takura Sosai.
Ki biya ki karanta cikin Salama.
*Anitha..*
8/19/20, 8:03 AM - Ummi Tandama: *MR BELLO..!*
_(The young Teacher)_
 Â
*Wattpad:Janafnancy13*
_Mallakar:Janafty�_
Â
*Littafina na kudi ne,kibiya ki karanta cikin salama,akan â‚?200 kachal,Vips â‚? 400 ne,kada ki karanta min littafi indai baki biyani ba,Domin neman karin bayani zaku iya nemana ta wannan Nombar 09069067488*
   Â
*🅿�19*
*KATSINA*
"Achan katsina kuwa Haka Biki Ya Tashi Zuciyiyo Babu Dadi Dangin Umma sai maganganu Suke na An Tozarta Dan yar"uwansu Abba Kabiru yajama Umma Kunni kar karyaji Wata Mgana,Bayan Shida Abba garba Sun Kira Ya Muktar Suna mai Rantsuwan basu san Abunda Kasim ke aikatawa ba kenan da bazasu Taba Fara Shigemai gaba Aneman Aure ba,Sunyi Haka ne Saboda Suna Tsoron Bello Domin Ko Ranar Daurin Aure A bornon Tsoron Nashi ne ya Hanasu Wani Motsin Kirki.
Kasim kuwa Kwana Hudu Tsakani ya Tattara ya koma Kaduna,Shi Haruna Tun Washegari ya koma Kano,dama chan yake sun Rabu da Niyyar sai Sunyi Mgana ta Waya,Da zai Tafi Abba kabiru Yayi mai Fada Sosai kuma yaja kunnansa kan ya Fita Harkan Bello Kar ya Kuskura yace zai Dauki mataki Yaga dai Suma basun Fita bane Duk Ranar Daya makasu kotu yana da Hujjan da Za"a Dauresu har Igiya Tayi Rara bamai Sakawa a Sakosu.
Kasim Jin Abba Kabiru kawai yake kawai Don Mganarsa na Shiga Kunnansa ne tana Fita Domin yaci alwashin Daukan Fansa Akan Bello Domin Bazai kyale Wanda yayi Sanadiyar Kwacemai Aneesa ba,gashi sai kiran Wayanta yake Ba"a Dauka Ranar Dai da aka Daga Anty Nafee ce tamai Zazaga tace karya kara Kira domin Aneesa Tana Gidan Mijinta,Kwana yake Cikin maye Saboda baya Jure Tuna ya Rasa Aneesa Ko ya Hashim kafin su koma Abuja Shima ya Sameshi yayi ta mai Nasiha Ammh kasim Jinsa kadai yake bawai Domin maganganun Suna Shiga kansa ba.
Umma kuwa Da Abba Kabiru kemai Fadan ma yadaina Abunda yake Cewa tayi ya daina ma Danta Fada Ita yaronta baya Neman mata Sharri bello ya Kullamai kuma Allah ya isa Bata Yafe ba,Sai da Abba kabiru Ya Daka mata Tsawa kana ta kama Bakinta Mama Sahura kuwa Duk da Abun bai mata dadi ammh ko Jaje batama Umma Aranta ma Allah ya kara take mata Domin Tafi kowa Nuna son ya"yanta kafin Inna Rukayyah Ta koma kano sai da Sukayi da ita kan Zubaida Kwata Kwata Umma bata iya Siyasar Duniya shiyasa Ko Abba kabiru yake Girmama mama Sahura don ko da Take matar kaninshi Bata iya Gardama Dashi ammh Umma gaban Ya"yansa ma Tsinka sa takeyi
Zubaida Dai Ya Hashim ya Tarata suka koma Abuja Saboda Makaranta ammh Tayi kuka kamar Ranta Zai Fita Jin Aneesa ta Auri Bello Domin Ita harga Allh Haryanzu bataga Namijin Daya Riga yagama Tsari da Rayuwarta Irin Uncle Bello ba,Hakura tayi ta lallashi Zuciyarta ammh Tana ji Aranta bazata Hakura ba,zata Cigaba da Gwada Sa"arta Domin Aneesa babu Abunda Zata Nuna mata Daga Bangaren Jiki Zuwa na Fuska.
Zulfa ko sai da Tayi Zazzabin kwana Biyu Mama Sahura ce Tayi ta lallashinta Tana Nuna mata Gwara da Kowa ya Rasa Tsakanin ita da Zubaida,Ko da Bikin nan Da Suka Hadu haka Dinga Jifan Junansu da Mugun kallo kan Wanda baisan ma Suna yi ba, kuma kana uwa uba kuma Kowa na Bin Tsakin Uwarshi Ballema Mama Sahura da iya Kissa bata nuna Akwai Takun Sa"a Tsakaninta da Umma gaban Mutane Shiyasa sau Tari ko Taro ake Umma tafi Bada kanta Don Ita Zatayi ta yada Habaici Tana Zagin Mama Sahura Mutane suyi ta yabon Mama Sahura Domin bata Biyemata sai dai ma tadinga Fadin"Yaya kiyi Hakuri.."Kowa kuma Awajen sai ya bama Umma Rashin Hakuri Saboda ita Haryanzu batayi karatun Duniya ba.
****
Tunda Kasim ya koma Kaduna ya Cigaba Daga Inda ya Tsaya yan Wajen Aikinsu suna ta mai Jaje,Sani kuwa koda Suka Hadu shi yama kasim din Sallama ammh yaki amsashi,Tunda ga Lokacin Shima ya Fita batunshi,Domin kowa ya ganshi yasan bashi da Natsuwarsa Duk ya susuce ya lalace bawani gayu sai Tarin kasumba Wajen aikin ma Bai Cika maida Hankali ba,Kwana Biyu da Dawowarsa Haruna ya Biyo masa Suka Tafi Chan Wani Kauye Cikin Niger Delta Wajen Wani Boka Wanda kwana Sukayi Suna Tafiya kafin Su iya Sumai bayanin Abunda ke Tafe dasu Shi kuma yace Su koma su Sati daya tak..Komai zai kamallah basu bashi komai ba Domin ka"idan Aikinshi sai ya kamallah Ake biyanshi Haka Suka Juyo Cike da Farinciki basu damu da Wahalan Tafiya ba Haka Suka Sake kwana Suna Tafiya kafin su Dawo Hankalinsu kwance Suna Jiran Sakamakon Aikinsu.
*****
*Abuja*
Tuni ya gama Duka Shirinsa Na Tafiya kano agobe,Bai Sanar da Ya Muktar da Daada ba sai Daren Washegarin da Zai Tafi kana ya Shiga Shashen Daada inda ya Tarar da Anty Rahila da ya muktar nan yake Sanar dasu gobe zai Tafi kano,Su Hibba Suna Wajen Aneesa Sune Dama abokan Hiranta.
Cikin Murna Daada keta saka albarka Kafin tace"Daga kai Har Aneesa zaku barma na kewa ko,Zaku tafi lokaci Daya..".
Tamke Fuska Bello yayi kafin yace"A"a Bada ita Zani ba Daada Ita tana nan..."Wani kallo ya Muktar ya Jefeshi Dashi kafin yace"Bangane anan Zaka barta ba kabarma wa kenan..? Yafada Fuskarsa ba alaman Wasa ganin Haka sai Anty Rahila ta mike tace bari tazo Ta fice ta basu Waje.
Tattaren naman Saman Goshinsa yayi Waje Daya kafin yace"Me zataje tayi achan bafa zama zanje yi ba,Shima kamar wanchan ne Koyarwa Ne.."Harara ya Muktar ya Makamai kafin yace"Ok wannam Dalilin ne,zaisa ka Tafi kai kadai ka barta karfa ka kamanta Yanzu ba Da bane Kai Mijin Aure ne Aneesa kuma matarkace kuma Tana da Hakki akanka,Dole ka Tafi da Ita domin Babu amfanin kabar Matarka anan kuma kai ka Tsallake katafi Wani gari..".
Shuru Bello yayi kansa na Kasa Ji yake kamar yayi Bindiga Saboda Fushi Hura Hanci kadai yakeyi Zuciyarsa na Tafasa banda Tauye Hakki da Son Atakuramai ya Tafi da Aneesa tamai Uban mene..? Bai gama Tunani ba Daada tace"Ai mganar banza ma yakeyi...Dole ya Tafi da Ita in ta Zauna anan mezata mana,Kai Bello ka Tafi da matarka kajima na gaya maka.."Tafada kai Tsaye Haushi ya kamashi ya Dago yana Fadin"Daada bai zai yuyu ba...Nifa ba Wani Abu Takemin ba Da Zuwanta da Rashinta Duk Dayane plz karku mtsamin Na Tafi da ita zaku karamin Nauyi da Takura.."
Dakuwa Daada ta Makamai kafin Tace"Kaga Naka nan Bello mu kake Fadama Da Rashin Zuwanta da Zuwanta Duk Dayane Awajenta..? Bama son Mganar Banza Tafiya dai dole ka Tafi da ita kamaji na gayamaka bana son na karajin Wata mgana.."Rage girman Idanuwansa Yayi yana kankance su cike da Fushi a Harzuke ya mike zai yi mgana Ya Muktar ya Dakatar dashi da Hannu Lokaci Daya Shima ya Mike yana Fadin"Da Matarka zaka Tafi mallam...Dis is our Final Desicion..."Daga Haka ya Fice Daga Falon Daada.
Numfashi Bello ya Sauke yana Shafa Suman kanshi kamar ya Fashe da kuka Daada dake mai Mgana yamata Banza shima ya Fice Daga Falo cikin Fushi da kallo Ta bisa tana Tabe baki,Haraban Gidan ya koma ya Zauna Bisa mota yana Shafa Sumar Fuskarsa Yana Tunanin yadda Rayuwarsa Zata kare akano Shida Aneesa,Wacce Tun bayan Aurensu banda Sau Daya da suka taba mgana bai kara ko kallon inda take ba,kullun afalo Take kwana babu Ruwanshi da Ita,Sau daya itama Tataba Gaisheshi bai amsa ba,Daganan bata kara ba,Mganar Shiga Bedroom dinsa kuwa Sai da Daada ta mai Zazaga Domin kullun Aneesa nan take Zuwa Tayi Wanka kaya ma Tabar mai Sabbin Ta koma