Showing 9001 words to 12000 words out of 122554 words
Chapter 4 - MR. BELLO Complete Book Hausa Novels by Janafty .txt
zagaye Wajen Duka Hannayensa Sarke Abayansa Fuskarsa Tana bayyana Damuwar Daya ke Ciki Duk da baya bama Hakan Muhallin Bayyana Cikin Wasu Dakikai Abubuwa Dadama Suka Fara Dawomai Cikin Kwakwalwarsa..
*How to pay....â‚?300 0552179550 JAMILA UMAR GTB, VIPS..â‚?600...or MTN card aturo ta wannan Nombar 09069067488 hade da Hoton Tracsation*
_akwai garabasanmu Na Sanyaya biyu,👠Matar Naseer Da Mr Belll guda 2 �500 ne,VIP �1000, Single one �300 ne zaku biya ta account Detail din sama,Mutanen Niger zasu tuntubi wannan lambar +22794775574 sai kunzo_
*Shakira...* *MR BELLO..!*
_(The young Teacher)_
*Wattpad:Janafnancy13*
_Mallakar:Janafty�_
      *🅿�4*
*#FLASH BACK...*
 🌟 *ALHAJI MUHAMMED HASHIM JIKAMSHI* Shine Asalin Sunan Mahaifin Bello Da Muktar Wanda ya Kasance Haifaffan Garin Jikamshi ne,Dake Hukumar Da'n Musa Dake Cikin Babbar Jahar Katsina.
  Alhaji Hashim Mahaifin Muhammed Ya kasance Ma"aikacin Hukumar Wutar Lantarki na Garin Jikamshi Yana da Rufin Asirinshi Daidai Gwargado,Matarsa ta Farko Hajiya Maryam Ta kasance Yar Dangi ce Auren Zumunci Akayi musu Ita yar nan garin Jikamshi ne,Wata tara nayi Ta Haifo Kyakyawan Danta Namiji Aka Sanya Masa Suna *KABIRU* Sai Haihuwanta na Biyu Ta karayin *ABUBAKAR* suna Kiranshi Garba,wanda Tsakaninsu shekara Daya ne.
Tana da Cikin na Uku Hashim ya kara Aure da Wata Yar Malumfashi mai Suna Aisha Auren Dayasha Mganganu Sosai Har Saida maryam Tayi yaji Zuwa gida Saboda Ta Tada Hankalinta kan Hashim bazai kara Aure ba Shi kuma yace Sai yayi Toh iyayensu mata ba Wanda ya Goyi bayanshi Saboda Maryam Iyayensu maza ne Suka Shiga Mganar Har Maryam Ta Koma Gidan Hashim Akayi Biki Lafiya Aisha Tatare Agidan Mijinta.
Tun Zuwan Aisha gidan bata taba Jin Dadin zama da Maryam da ya"yanta ba Saboda yadda Take Nuna mata Tsana Kirikiri Hakama Dangin Hashim Din Sun Koma bayan Maryam, Aisha ta Zama bata da Wani gata agarin Jikamshi Tunda Ita iyayenta Sunyi Nisa,Tana Shan Wahala Wajen Maryam da Dangin Hashim Ammh ko Sau Daya bata taba Furtama Hashim ba Sai ma Kokarin Farantamai Cikin Hanyoyi Dadama Wannan Shi ya Taimaka Wajen Bata matsayi mai Girma Acikin Zuciyar Hashim Uwa Uba ga Hakuri da Kawaici ga Sanin ya kamata.
Wannan Kulawar da Hashim ke Nunawa kan Aisha Har saida Maryam ta kai Karanshi Agida Wai yana Fifita Aisha Akanta Wanda Dangi Sukamai Chaaa Aka Tarasu Dukkansu Akayi Musu Fada Abun ya bashi Mamaki ammh Kuma baya jin zai Fasa Nuna Soyayyarsa ga Aisha ,Watan Aisha Uku da Zuwa gidan Ta Samu Ciki mai laulayi Sosai yana bata Wahala sai ya kasance ko Wanka Sai Hashim yayi mata yake Fita Wajen Aiki Wanda ya karama Maryam Wutar Kiyayyar Aishan da Kishinta Shikuma Hashim yace bazai Fasa ba.
Cikin Aisha na Wata Biyar Maryam Ta Haifi yarta mace Wacce taci Sunan Mahaifiyar Hashim Wato *RUKAYYAH* Ita Kuma Aisha Sai da Cikinta yakai Wata Goma kana aka mata Operatin Ta Haifi katon Danta Namiji Yaci Sunan *MUHAMMED* Wanda Dangi Sukayi ta Ceceku Game da Haihuwar Saboda Yadda Hashim ya Kashe Kudi Sosai ga Hidimar Aisha Tundaga na Asibiti har Zuwa na Hidimar Suna,Duk da Haka bai kulasu ba Kuma Itama Aisha bata maida kai ba Duk ko Da mganganun da Maryam din Ke Jifanta Dashi.
 Watan Muhammed Goma Sha Tara Aisha Ta kara Samun Wani Cikin Wanda yazo da Sauye Sauye Dadama Domin An Sallami Hashim Daga Wajen Aikinshi batare Dayasan Laifin Daya Aikata ba Kuma Sallama babu Biya kowani karin Bayani Abunda ya matukar Tadamai Hankali Shida iyalanshi Gabadaya Gashi Lokacin Kabiru da garba Asanyasu A mkranta Harda Rukayyah Muhmmed ne kadai ba'a Sakashi ba,Abunda yafi Dagamai Hankali Shine Lokacin da Zai Auri Aisha yana gidan gado ne To Shine yaci bashin Banki,ya Siya Fili ya gina gida Duk Wata yana Cire Wani Abu Daga Cikin Albashinshi yana Biya Toh gashi An Sallameshi Kuma Banki bata Jira Dole ka a Biyata Kudinta.
Lokacin da Dangin Hashim Sukaji Wannan lbrin Shikenan Sai Aisha Takara Shiga Gararin Rayuwa na Cewa Itace mai Farar Kafa,Itace Tunda Hashim ya Aurota Karayar Arziki ta Kamashi Sai dai Ta Shige Daki Tayi ta Kuka Tana Rumgume da Muhmmed ga Cikinta ya Tsufa Alokacin ne kuma banki Suka Nema Kudinsa Shine Dalilin Saida Duka kaddarorinsa da Motocinsa Harda Gidan Da Suke Ciki Suka Tattara Suka koma gidan Gado.
Aisha ta Shiga matsi da gararin Rayuwa Domin ba Inda Takejin Dadi Sai Ta bangaren Hashim Kuma Koda yan"uwanta Sunzo bata Nuna Musu Wani Abu Sai Dai Su Tafi Suna Zencen Ramarta Acikin Wannan Halin Ta Haifi yarta Mace mai Suna *HIDIYA* wanda Tunda Lokacin Da Aisha Ta Haifeta bata kara Lafiya ba Harta Koma ga Mallicinta ta bar Marayin ya"yanta Hannun Matar Hashim Wato Maryama.
Hashim yayi kukan Rashin Aisha Sosai ga Talauci ga Kewar Aisha Sai Suka Taru Suka Sanyamai Hawan Jini,Dangin Aisha Kuwa Sukayi ta Kokarin ko Hidiyan Hashim ya basu Su Tafi da Ita Ammh yan"Uwanshi Suka Hana Wanda ba Kowa bane ya Kitsamusu Haka sai Maryam Domin bataso Adauke ya"yan Tafison Abarsu Tayi ta gana Musu Azaba Domin bata taba Son Uwarsu ba Suma bazata Taba Sonsu ba
Haka ko Akayi Dangin Aisha Sunaji Suna gani Suka Tafi Suka bar Muhammed Dan Shekara Uku da Wani Abu yayinda Hidiya Keda Shekara Daya da Rabi Abun Tsausayi Ammh Sun Sanar Dasu Cewa Lokaci bayan Lokaci Zasu Dinga Zuwa Dubasu Suka Amince,Bayan sun Tafi Aka Dauki Amanar su Muhammed Aka Damkama Maryam Wacce Ta karbesu kamar Gaske nan ko Cikin Ranta Mugun Nufi ne
Tun kafin Rasuwar Aishan Dama Ta Dade da Karantama Duka ya"yaanta Cewa Su Muhammed ba yan"uwansu bane Abokan Gabansu ne Saboda Babansu yana Fifitasu Fiye dasu Tayi ta saka musu Mugun Nufi acikin Zuciya Abunga ga yara nan da Nan Suka Haddace Karatun Nata Shiyaasa Muhammed Da Hidiya Suke Shan Wuya Ahannuta Ita da ya"yanta In Hashim yayi mgana ta Fashe da Kuka tace ya Raina Kokarinta,Data Fahimci Yana Damuwa da Halin da Suke Ciki Sai Koma yi musu Mgunta Aboye Abinci ma Kanzo Take basu,Ga Wahala Akasa Suke Kwana Cikin Sanyin Kasa Kafin Arufe Shekara Daya Yara sun Chanza Kamanni Tun balle ma Hidiya Wacce Bata da Lafiya Saboda Kwanan Kasa Nomomiya ta kamata Hashim baidata Cewa Domin Da yayi mgana yan Uwashi Zasu Tasomai da Fadin Uban me yake Tsinanawa Banda Zaman Banza,Yanaji yana gani sai dai yayita Kuka Shikadai Saboda Tsausayin Muhammed da Hidiya.
Amkrantar Gwannati Aka Sanyasu Sakamakon Kabiru da garba Dasuke na Kudi Tunda yan"uwan Hashim Sunfi Son So,Muhammed Tun yana Yaro yasan Gwagwamaryan Rayuwar Duniya,Sau biyu Dangin Mamansu na Zuwa Dubasu Suna Komawa da Kuka Saboda Tausayin Halin da Suke Ciki Tun Bama Muhammed ba Wanda Ke Karami Ammh Wahala ta Zama Cikin Jikinsa.
Tun yana Aji biyar yasan In An Tashi Mkranta ya Kama Hannu kanwarsa Su Shiga Cikin Kasuwa Yaringa Dako yasamu Abunda Zai Siya musu Abinci Domin Ko Sun Koma Gida Mama maryam bazata basu ba,Toh Ahakan ma basu Tsira ba In Suka Dawo sai ta kamasu Ta Masu Duka Hidiya Kuwa Kullum Cikin Kuka Take garba ya Daketa Kabiru ma Haka Rukayyah ma Sai dai in Muhammesd ya Ramata Mama ta kamashi Tayi mai Dukan Tsiya basu da Wajen da Suke Jin Sanyi sai Wajen Abbansu Wanda Shima Hawan Jini ya Kwantar Dashi.
Muhammed Dana Shekara Goma Aduniya Ita Kuma Hidiya Bakwai Allah yayima Hashim Rasuwar Mutuwar Data Raunana Zukata Dadama Babu Uwa ba Uba Maraici ya Lullubesu Dama Ganin Abban Nasu ba"a musu Wani Abun Ammh yana Fadi ya Mutu Shikenan Wahalansu ya Karu Hidiya ta zama Jakar Aiki Itace debo Ruwa,Share Share,aike aike ,Wanki ne da Guga Ammh Rukayyah na Zaune Jangal batayi Muhammed Kuma Fita yake Tun Safe yana yawon Dakonsa Sai dare yake Dawowa Ya Siyoma Hidiya Abunda zataci Domin yasan Duk Wunin Aikin Da Zatayi bazata Bata Abinci ba.
Da Farko Adaki Suke Kwana Tare da Su kabiru Ammh Sai Mama ta Kullama Muhammed Sharri Akan ta Kamashi yana Turama Rukayyah Ahannu Awando Wanda Iyalan gidansu Suka Hadu basu Duba kankantar Shakarun Muhammed ba Sukamai Dukan Mutuwa Suka kuma Koreshi Agidan,Haka yafita yana Kuka Itama Hidiya tana Kuka Wannan Shine Silan barin Muhammed gidansu Ya bar Hidiya Cikin gararin Rayuwa Bai yi Nisa da garin Jikamshi ba,Cikin kasuwa yake Wuninshi Sai Dare ya Tafi Tasha ya Kwana yana Tara Kudinshi Kuma kullum Daddare zai Siyan ma Hidiya Doya da Kwai yazo Zauren Gidan ya Tsaya ta Sadado ta Fito ya Bata bayan ya Zaunar da Ita taci Tasha Ruwa Haka Zasu Rumgume Juna Kukan Tsausayin Kansu Hidiya tasha cemai Su gudu Wajen Dangin mamansu Ammh Muhammed yaki Saboda Shi kanshi bazai iya gane Gidansu Maman nasu ba Don yana Karami Sosai Lokacin Da ake Zuwa Dashi.
 Muhammed bai bar Zuwa Mkranta ba Hidiyace dai Mama ta Kashe mata mkranta Bashi da yarda Zai yi yanaji yana gani Rayuwar Kanwarsa Tana lalacewa Su kabiru ko Suna Haduwa Dashi suda Abokansu Haka zasu dingamai Dariya Suna Tofamai Miyau Shiyasa ko ya gansu yake Saurin Chanza Hanya Hidiya Kuwa Tagama Wahalan Amfanin da Ruwa da Rana Daddare kuma ta Kwana Akasa nan da Nan Ciwon Nomoniya Takaramata Yawa Sosai Kullum Cikin Mura take Kwana da Sanyi Ammh ko Muhammed yazo bata Sanar mai Saboda Karta Tadamai da Hankali Koda yaushe yazo Jikinta yayi Zafi sai ya Tambayeta tace bakomai.
Adaddafe Muhammed ya kamallah Jss3 sai ya Ijiye Karatun ya Maida Hankalinshi kan Dakonshi hade kuma da Jari Bola Kwata Kwata Zuciyarsa ta Kekahe Neman na Kanshi yake ba Domin Shi ba Sai Domin Tilon Kanwarsa Hidiya,yayi kwana Biyu yana Zuwa Baya ganin Hidiya na Fitowa sai Hankalinshi yatashi Ranar dayazo na Uku Azauren Gidan ya kwana yana Jiranta Ammh batazo ba,Tundaganan Jikinsa ya bashi ba Lafiya Gudun kada Wani ya ganshi ne ya sanya ya Koma kasuwa Hankalinsa Duk Atashe Wajen Karfe 1 na Rana yana Kasuwa yana Sana"ar Dakonsa Wani yaron Kawun Abbansu yazo yake Sanar Dashi Wai yazo Hidiya zata Mutu Cikin Fitan Hayyaci ya Watsar da Abunda Ke Hannunshi Suka Rumtuma Zuwa Gidansu.
Sai dai Suka ganshi Kwatsam ya Shigo Har Shashensu Alokacin Wajen Shekara Biyar Bai kara Shigowa Gidan ba,Hidiya tana Kwance Akasa Siminti Hancinta ya Toshe da majina Numfashinta baya Fita Ta Rame ta lalace Kasa ya Zube gabanta yana Kuka Hannu Ta Mikamai Tana Fitar Da Hawaye Daidai Lokacin kuma Kawun nan nasu Suka zo Dama mama ganin Hidiyan ta Kusa Mutuwa ne Shine taje ta Kirasu Wai Suzo Su gani Ita bama tasan Bata da Lafiya ba Alhalin Tana sane Itama kema Kara Saka Ciwon Tashi Domin Wanka take Zuwa tamata Da Ruwan Sanyi Kuma Ta Hanata Sauya kaya Har sai Sun Bushe Ajikinta.
Muhammed ya Rude da ganin Halin da Hidiya ke Ciki ko Ta kan Kawunsu Dake mgana baiji ba ya Ciccibi Hidiya yana Kuka Ya Fita Da Ita Waje,yana Ihun Mutane su Taimakamai Ana Cikin Wannan Halin ne Allah ya jeho Alhaji lawal Acikin Motarsa Zai Wuce Katsina Alokaciin ganin Muhammed Dauke da Hidiya yana Kuka ya sanya ya Faka Motarsa ya Fito baima Tsaya Tambayan Muhammed ba ganin Halin da suke ciiki ya sanya ya karbi Hidiya ya sakata Abayan Mota ya Umarci Muhammed Daya Shiga Su Tafi Agaban Idon Dangin Mahaifnsa Suka Tafi Asibti da Hidiya ammh ba Wanda yayi Tunanin Binsu.
Babban Asibtin Garin Sukaje sai dai Suna Shigowa Get din Asibtin Hidiya tafara Wani kakari Muhammed ya Rude ya Rumgumeta yana Kuka yana Kiran Sunanta ganin Idanuwanta na Kafeewa ne ya sanya ya Kuramata ido hawaye na Fita Daga Cikin Idanuwanshi Yana ji yana Gani Agaban Idanuwansa Aka Zare Ran Hidiya Abunda ya kasa barin Zuciyarsa Kenan Har Shima ya koma ga mahallincinsa.
Muhammed yayi kuka Tamkar zai Zauce Saboda Mutuwar Hidiya basu Juya ba sai da Suka Shiga da Ita Cikin Asibitin Aka Tabbatar da Mutuwar Hidiya Kafin Alhaji Lawal ya Daukosu Zuwa Gida ganin Kukan da Muhammed Ke Yine yasa ya Tambayesu ina Mahaifinsu nan Muhammed yana Kuka yana bashi Lbrinsu Wanda ya Matukar bama Alhaji lawal Tsausauyi.
Abun Mamaki da Suka Dawo da gawan Hidiya ba Wanda ya Nuna Jimami ko Damuwa,Taruwa kawai Sukayi,Abun Takaichi Muhammed Shi yayima Hidiya Wanka Gawa Yanayi yana kallon Cikin Idanuwanta yana Kuka Ahaka Har Aka kaita gidanta na gaskiya A makabartan Aka Watse Aka barshi Alhaji lawal shi ya rikoshi Suka Fito ya Sanyasa Cikin Mota bai Zarce dashi ko"ina ba sai Katsina.
Alhaji lawal shi da Matarshi Hadiza basu Taba Haihuwa ba Gashi yana da Tarin Dukiya Ta Dalilin Kamfanonin Dayake Dashi kama daga na Robobi kanfanin Sarrafa Atamafa,na Takalma ne da Sauransu. ya Tara Kudi masu yawa Tunda yazo da Muhammed yabata lbrinshi Shikenan Tsausayi ya kamata ta kama Muhammed Ta Rumgume tana Kuka Kuma Sukaci Alwashi Zasu Rike Muhammed Tsakani ga Allah.
 Bayan Rasuwar Hidiya ba Dadewa Dangin Aisha Suka zo ganinsu suka Iske bakin lbrin Rasuwar Hidiya da Lbrin wai Muhammed ya Gudu ya Shiga Duniya Haka Suka Koma Malumfashi Suna Kuka Sosai na yadda Rayuwar ya"yan Aisha suka lalace Acikin Duniya,Shikuma Muhammed ya samu Chanjin Rayuwa ya koma mkranta,bayan ya gama Secondry Sch Suka Tafi Dangin Alhaji Lawal A malumfashi Alokacin ne kuma Aka gano Ashe Shi Alhaji lawal Abokin Wasa yake ga Marigayiya Aisha Mahaifiyar su Muhammed nan fa Sabon Kuka ya Tashi Ana Ta Rumgume Muhammed,Wanda koda da Rana Daya Mutuwar kanwarsa Hidiya bai Taba Bacemai ba.
 Â
Akasar England ya Hado Digree dinsa na Farko Akan Harkan Kasuwanci Haka kuma ya Wuce Kasar Calponia ya Hado Master dinsa Akan Accouting da Hada Hadar Kasuwanci Koda ya Dawo Nageria sai Ragamar Dukiyar Alhaji lawal Ta Dawo Hannun Muhammed,Shi kuma Alokacin A England yayi Aiki da Wani Kamfanin Turawa na Sarrafa Takalmam Maza so sai Suka Hada Huldar Kasuwanci da Kamfanin Alhaji lawal Dake Nageria kuma Alhamdulillah Lokaci Kadan Huldar ta kawo musu Kudi Sosai Suka Cigaba,.
Muhammed ya Wuce Duk Tunanin Mai Tunanin jin haushinshi ko Hassda Daga Danginshi Kuwa Suna da Lbrinshi Domin Alhaji lawal na Matsamai Lokaci bayan Lokaci Yana Zuwa Dubasu Rukayyah Tayi Aure Akano Su Kabiru kuma Angama karatun Ana Zaune ba Aikin Mama maryam kuma girma ya Kara kamata da Kuma Hakkin Hidiya da Muhammed Domin Taga yarda Allah yake Maida bawanshi Lokaci Daya.
Kafin Rasuwar Alhaji lawal Sai da Tabbatar ya mallakama Muhammed Duka Dukiyarsa bayan Ancire na yan"uwansa,Wannan Abun yabama Mutane mamaki da kuma Girmama Soyayyar da Alhaji lawal Kema Muhammed Su Kabiru kuwa Hasaada da kyashi bai bar Zuciyarsu ba,Sai Sukayi lambo Suna Shigema Muhammed Harda Rokonsa Gafara Saboda Suma Su Shiga Jikinsa Su Samu Arziki Sun kuma yi Nasara Domin Daga Kabiru Har Garba ya Daukesu Aiki A kamfanonin Alhajin lawal Duk da Abun da Suka Aikata gareshi bai Taba bacemai ba Ammh in yayi Duba ga Yadda Allah ya Daga Darajansa sai ya Godema Allah.
  Mutuwar Alhaji lawal Da Matarsa Sakamakon Hadarin Mota Shiyakara Fito Da Sunan Muhammed Aduniya Domin ya Samu Dukiya mai yawa Yawancin Kamfoninin Alhaji Lawal Shi ya mallakesu Gashi Shima yasan Kan Kasuwanci Kafin Ya Rufe Shekara Daya ya Mallaki *Jikamshi shopping mall* Jikamshi Store* Jikamshi And Sons Nageria Limited..* Lokaci Daya Sunanshi yayi Suna A nageria Gefe Daya ya jawo Yan Uwansa Da Dangin Mahaifinsa yamusu Gata duk da Abunda Suka Aikata garesa Dangin Mahaifiyarsa kuwa Dama Sune Ahalinsa.
Tuni ya Tattara Kabiru da Garba da Mama Suka koma Katon Gidan Daya gina A Katsina Komawarsu Wannan Gidan Mai kama da Aljannar Duniya Shiya kara Saka Zuciyoyin Su Kabiru Gudirtan Cewa Ko Ta Halin kakane sai Sunga bayan Muhammed Sun mallake Duka Dukiyanshi Ita ko Mama Maryam ta Saduda Ance magaji mafiyi Domin Su Kabiru ya"yanta ne Ammh Sun Fita iya Kulla Makirci da Sharri Duk da Muhammed na Kanninsu Haka Suke Sadda kai Suna mai Biyayyah Duk Don ya Saki Jiki Dasu.
Cikin Shekara Uku ya Siya Musu gidaje da Motoci ya kaisu Makka Kuma yayi Musu Aure Kabiru Akaduna ya auro Karima sai Garba dayayi Aure a Kankara Ya Auro Sahura Dukkansu Sukazo Suna Cin Arziki da Dukiyar Muhammed Wanda Suka Wulakanta Rayuwarsa da Farko Mama maryam bata Rasu ba Sai bayan Auren Muhammed,ta rasu ta kukan Neman Gafaransa kan Abunda ta aikata garesa Shida kanwarsa,muhammed anso a tusamai auran Dangi A Ammh yaki Domin Allah ya Hadashi da Hassatu Wata Bafullata ne Daga Jahar Yola
Hassatu marainiya ce Bata da Uba sai Mahaifiyarta Data ke cema Daada Farar Bafullatana ce Kyakyawa da Ita Dangin Mamansa Suka yi komai na Auran Cikin Lokaci Hassatu Ta tare Agidan Mijinta Dake Katsina,Tun kuma Daga Lokacin Sai Abubuwa Sukayi ta Cigaba Arayuwar Muhammed gefe Daya Kuma su Kabiru da Matansu Suna ta Ta Hada Tuggunsu A boye Ita kanta Hassatu ta sani Domin ba kyashin Da basu Nuna mata Ammh bata taba Nuna ma Muhammed Ba bataso ta Rabashi da yan"uwanshi.
 Karima matar kabiru wabi Takeyi In ta Haihu sai anyi Suna Su koma ga Allah Ita kuma Sahura matar garba Shuru Haihuwan, Itama Din Shuru Kwatsam Hassatu ta samu Ciki Su kabiru ba Kulle kullen da basuyi ba kar Hassatu Ta Haihu Ai kuwa hakansu bai Cimma Ruwa ba Domin A Babban Birnin India Delhi Hassatu Ta Haifi Kyakyawan Danta Namiji Wanda yaci Sunan *MUKTAR* Basu dawo Ba sai da Sukayi Wata Biyu Suna Dawowa Kuma ya kaita yola Wajen Daada tayi Wata Daya kana Ta koma Katsina.
Lokacin da Muktar yazo Duniya yazo Cikin Gatan Rayuwa Sosai Saboda Mahaifinshi na kan Samu Hassatu Ta Fahimci komai Shiyasa Take ta Kafa kafa da D'anta bayan Tana Sanar da Daada Duk Abunda Ke Faruwa Ita ta Haneta da Karta sanarma Muhammed Ammh Dai Ta Kiyayi Kanta ta Kuma Dinga Lura Saboda Hakama Dukkansu Suka baro Gidajensu Suka Dawo Gidan Muhammed ke zaune Shida Hassatu katon Gidane mai Dauke da part part da Zuwan Wai Sunfi Jin Dadin Zama tare Dashi Shi kuma bai kawo komai ya Amince Suka Tattaro Suka Dawo nan da Zama.
Inna Rukayyah ma Dake Kano Babu Abunda Muhammed baya Mata tana Kuma Zuwa Akai Akai Sai dai ita Tunda Tayi Aure Allah bai bata Haihuwa ba Sai da Muktar ya Shekara Bakwai Aduniya kana Karima matar Kabiru Ta Haifi Danta Namiji yaci Sunan kakansu *Hashim* Lokacin Tuni Ansaka Muktar A mkranta *International Community School Abuja* Cikin Gata da Soyayyah mai Tsanani Wanda Ke Kara Wutar