Showing 111001 words to 114000 words out of 122554 words
Chapter 38 - MR. BELLO Complete Book Hausa Novels by Janafty .txt
bazata zama mallakinka ba.."Yafada yana Dukan Kafadarsa.
Cikin Mutuwar Jiki kasim ya Sulale kasa,zai yi mgana Hashim ya saka hannu ya Tsinkeshi da mari yana Fadin"Bama son jin bakinka anan wajen...Ka zama Dabba acikin Mutane,Bayan ka karbi Sakamakon anan zaka koma gida ka karbi Cikin Shigen da kama Budurwanka.."Yafada Daidai Lokacin da Zainab da Mahaifinta Alhaji isa suka Shigo Cikin Offishin kuma a kunnansu Mganar da Hashim ya Fada sun manta sam sun suka kira Alhaji isan Suka sanar dashi an samu kasim din a State C.I.D Basu taba zaton zasu iya zuwa ba.
Gabadaya sai kallo ya koma sama cikin Firgici zainab ta Dafe kirji Tana Fadin"Ciki kuma...? Tafada tana kallon Kasim daya kwalalo ido Cikin Karfi Hali Hashim yace"Kwarai kam...Kuyi hakuri mun Rufeku ammh azahirin batu Kasim bai chanchanci Auran yarku ba.."Yafada yana kallon Kasim din baya Zainab taja tana Kallon kasim Hawayen idanuwanta na Zuba
Cikin Kunar Rai Hashim ya cigaba da Fadin"Aisha Tsohuwar Budurwanka Daka yaudara kama ciki Ta haife maka Cikin kuma ta kawo Abunda ta Haifa yanzu haka tana katsina an ijiye maka Abunda ka Shuka,in kazo ka girbeta kai kadai..."Ido kasim ya waro kafin yace"Aisha...."Idanuwan Hashim sun kada yace"Eh Aisha maiduguri...Kuma Haruna ya Tabbatar da gaskiyan labarin..."
Kai kasim ya sadda yana Jin Nadama da danasani sun gama Lullubeshi wannan Shi ake Kira yau ma Tubulal sara"i...Ranar Tonin Asirinsa gaban iyayensa Gaban matarsa,da Danginta,Kaico kaico na kasim yake Fada acikin Ranshi kafin ya Daga kansa Yana hawaye ya fara Fadin.."N.....
Kibiya ki karanta cikin salama.
*Anitha...*
8/22/20, 10:25 AM - Ummi Tandama: *MR BELLO..!*
_(The young Teacher)_
*Wattpad:Janafnancy13*
*Littafina na kudi ne,kibiya ki karanta cikin salama,akan â‚?200 kachal,Vips â‚? 400 ne,kada ki karanta min littafi indai baki biyani ba,Domin neman karin bayani zaku iya nemana ta wannan Nombar 09069067488*
*🅿�38*
...."Na tuba nabi Allah...Don Allah Abba,ya Hashim kuman Aikin Gafara..."Yafada Hawaye suna kara zarya asaman Fuskarsa.
Ya Hashim ya kallesa cikin Raunin Murya yana Fadin"Kasim ba mu zaka nema gafara ba...Kanka ka cuta da Rayuwarka Bello zaka nema gafara domin shi kafi Cuta...Bayan ka mai Asirin zama cikin lalaura na tsawon wani Lokaci bai isheka ba sai da kabi matarshi har gida Da Niyyar keta mata Haddi...Yanzu ya kai karar ka Kotu sai kace bai maka adalci bako..?.."Yafada cikin Kunar Zuciya.
Kasim ya Dago kansa yana kallon Bello yana Fadin"Nasan Ni mai laifi ne awajenka..Kuma ban Chanchanci yafiyar ka ba....Karka ga laifina Sharrin Shedan ne Dana Zuciya da kuma Zugan mugun Aboki Don Allah ku yafemin Nayi Nadamar Duk Abunda na aikata na Shagalan Duniya banta Tsammanin akwai Ranar Da Asirina zai Tonu Lokaci Daya ba.."Yafada yana Gunjin kuka gwanin ban tsausayi.
Abba garba yace"Kana fadin Shedan...? Waye Shedan din in ba kai ba...Tsakani ga Allah ka Cutar da Rayuwarmu kuma ka Cutar da kanka domin ko D'aya bamu da Masaniya da Abunda Muguwar Zuciyarka ke kitsa maka."Kasim na Hawaye yana Fadin"Nasani Abba...Kumin aikin Gafara don Allah..".
Abba kabiru Dake kuka Hawaye na Zubar mai ya saka hannu ya Sharbe yana Fadin"Hakika Dama Haka Rayuwa ta gada..Duk yadda ka kai ga muguwar Zuciya,sai ka samu wanda ya shanyeka...Ni na kasance abaya bani da Zuciya mai kyau sam,wani Lokacin ni nake Dora Garba kan wata Cutarwa..Bayan mun tuba mun gane gaskiya bantaba tsamanin Watarana Abunda na aikata zai bibiyeni ba..Sai gashi ya bini Ta hanyar bani D'a irinka Kasim..Bazan maka baki ba sai da zan Roki Allah ya Sa wannan Abun ya zama Hanyar Shiriyanka,Kuma bana bukatar amaka afuwa a kaika kotu ta yankema Hukunci Daidai da Abunda ka aikata.."Yafada yana Kuka Sosai Abba garba na Dafa Kafadarshi Cikin Alamun lallashi.
Alhaji Isa Mahaifin Zainab dayayi Tsuru yana kallon Ikon Allah Cikin Ransa kuma yana kara godema Allah da Lokaci bai kuremai ba Jami"an tsaro kuwa sai Daukan Bayanai suke suna jiran Umarni Zainab ce Dake kuka ta karisa gaban Kasim ji kake Kau...kau..! Ta Daukeshi da Maruka Har biyu cikin kunar Rai Take Fadin"Dama Halinka kenan..? Dan Akuya ne kai Ko nace Bunsuru ne mai Haikema ya"yan Jama"a kuma kake Tunanin ka zama mijin Zainab..? Kayi kuskure kasim Har Abada ni Zainab Alhaji isa bazan taba Zama da Fasiki mazinaci irinka ba...Ka Bani Takardan sakina yanzu ko kuma ka Fada da bakin ka sakeni in ba Haka ba Wlh sai na Shigar dakai kara akotu mutumin Banza da Wofi.."Tafada tana Jifansa da wani Wulakantattacen kallo Lokaci Daya tana Zubar kwallah.
Dafe kuncinsa Kasim yayi yana Bin Zainab da kallo Alhaji isa Dake Tsaye yace"Kimin Daidai Diyar albarka...Koni ban goyi bayan ki cigaba da zama da Bara gurbi irinsa ba...Ka sakarmin yata ko ni nayi karanka akotu.."Yafada yana Kallon Hashim wanda ke kallonsa cikin Takaichin Abunda kasim din ya jazamusu..
Kafar Zainab Kasim ya kamo yana Fadin"Haba zainab taya zaki ce Haka.? In kika bar ni a halin Danake ciki Wazan kama...? Ki Rufamin Asiri Don Allah Whl nayi miki alkawarin Daga Rana mai Kama ta yau na Daina Shaye Shaye da Neman mata...Aneesa kuma bazan kara Shiga Sha"aninta da Mijinta ba Har Abada..."Yafada yahada Hannuwansa alaman Roko Da Sauri Zainab ta kwace kafarta tana Fadin"Au ashe ma kai Mugayen Halayyan naka basu da iyaka bayan Duk wadanan Harda Shaye Shaye ma kakeyi...Tab...? Wlh baka isa ba sai ka sakeni.! Ka sakeni yanzu ina Jiranka na gwamnace a sakani Layin Zawaran Layinmu da asakani Cikin Layin Da Auren Zainab gwara zaman gida ba..."Tafada tana Jifansa da wani Wukatattacen Kalo..
Kasim ya juya yana kallon Ya Hashim yana Fadin"yaya don Allah ka saka baki...In zainab ta rabu dani wazai sake bani yarshi..? Abba kabiru yayi Saurin Taran Hashim yana Fadin"Babu...Domin ka Riga gama yima Rayuwarka wani bakin Fenti wanda har Abada bazai Taba goguwa Daga Jikinka ba,Tana da gaskiya nima na goyi Bayanta..Maza ka saketa yanzu Tun kafin Dan gutun Kimarka Dake cikin Idanuwana su sake Zubewa.."Yafada cikin bacin Rai Kasim na Kuka yana kallon Ya muktar wanda ya so saka baki Bello ya Dafa Kafadarshi yana Dagowa ya girgizamai kai alaman Ba Ruwanka Dole ya Tsuke bakinshi.
Bello kuwa Hannuwansa ya Harde Bisa Kirjinsa yana Watching din komai cikin Nishadi Domin Harga Allah Zuciyarsa bata samu wajen da Zata Tsausaya musu ba...Uncle Aminu ma yana gefe akasan Ransa kuma yana jin Tsausayin su Abba kabiru da Kasim.
Kasim ya Sadda kai yana Kuka kasa kasa yace"Na sake ki zainab Saki Daya..."Cikin Farinciki Tace"Madallah nagode...Ko kaga kayi D'aya karka saka acikin Ranka zan iya Dawowa gareka...Nagodema Allah da baka Doramin idda ba.."Tafada Lokaci Daya Tana Share Hawayen Idanuwanta Ta Fice daga wajen da Gudu Alhaji isa ya mara mata baya,cikin Tsausayin Halin Da ya jefa yarshi Shima Rashin Bincike ne yajamai haka saboda samun Tushe mai Asali,Suna hanya ya Kira gida yace maza atura mota ta kwaso kayan Zainab Daga gidan kasim,Bai tsaya Neman Yayi karin Bayani ba ya Datse kiran.
Gabadaya Kukan kasim ya cika wajen ya muktar ne yayi gyaran Murya yana Fadin"Duk abar wannan mganar...Bello ka saka hannu abada Bellin kasim..Koma miye in muka karisa gida sai mu Cigaba Da Tattaunawar.."Bello bai yi gaddama ba aka bashi Takarda ya saka Hannu Shima kasim ya saka Bayan kuma an yi Takardan iyaka wanda in aka kara kamashi da irin Wannan laifin ba Shakka sai yaje gidan yari......
Tun kafin agama cike Takardun Abba Kabiru ya koma mota saboda Jirin Dake kwasarshi,Basu Dauki Lokaci ba Aka bada Belinsa,Bello dai Tawagar ya Muktar yabi suka koma Abuja Uncle Aminu kuma Daganan ya koma kano,Su kuma su Abba kabiru suka iza keyar Kasim zuwa katsina,Tun da suka shiga gidan yake ta Rufe Fuska Saboda Kunya Umma kuwa Haka ta zauna gabanshi tana kuka mai Cin Rai tana Fadin"kasim meyasa ka kunyatani a idon Duniya...? Kacutar da Zuciyata kuma kabama yardata akanka Kunya.."Take Fada Tana kuka Su mama Sahura suna nan basu koma ba Hakama Wasu Daga cikin Dangin Umma,inna Rukayyah ma tana nan ita ta karbi Jaririyan Dake Hannun mama Sahura wacce Duk ta Koma wata karama Saboda Rashin Nonon uwa ta Ijiyema kasim bisa Jikinsa
Kura mata ido yayi yana kallonta yana Hawayen Tsausauyin Kanshi Da kuma Nadama mganganun Aisha na Karshe suna mai amsa kuwa acikin Kunnuwansa,Runtse ido yayi yana Fitar da kuka mai Sauti bama wanda ke Tsausayinshi Domin Komai ya Faru Shine Sila,Kasim yadda yaga Rana Haka yaga Dare kwana yayi kukan Zucci dana Sarari,Allah ma ya taimaka Mama Sahura na Kula da Jinjiran da ko suna ba"a saka mata ba,Da Farkoma Inna Rukayyah Cewa Tayi abashi ita ya kwana da Ita bamai wahalan Iskancin daya aikata Daga baya yazo ya bar Mutane da aiki.
Washegari Wajen sallar Asuba Abba kabiru ya yanke jiki ya Fadi Aka kwasheshi Ranga Ranga zuwa Asibitin Federal medical Center Katsina Suna zuwa bayan gwaje gwaje suka samu Jinin Abba kabiru ne yayi mugun Hawa Hawan Jini ya Fadeshi,ya fadi Dalilin Haka ya samu Shanyewar Barin Jikinsa Guda Daya,iyalai sai kuka Kowa kasim yake gani aSilar Faduwar Abba kabiru, Abba garba kuwa Tuni Duniya ta Fitarmai Bisa kansa ganin Daki Daki Abunda ke Faruwa da Rayuwar Abba Kabiru kafin Ta Juyo kansa Domin yana da Tabbacin Shima Allah bazai barsa ba...Hakkin Rai da kuma Cin Dukiyr marayu bazai taba barin Ahalinsu su Zauna lafiya ba sai Abunda suka aikata ya Bibiya Ahalin nasu.
*******
Labarin da su ya Muktar suka zo mana Dashi bamai Dadi bane Naji na kara Tsanar Kasim Jin Shine Silan Laluran Mijina Kuma Gwarzona,Wanda naga Tunda suka Dawo ya Kule kanshi Cikin Shashenshi Ranshi bace Mutuwar iyayensu Ta dawomai Sabuwa har sai da ya Fitar da kwallar,ammh sai wata Zuciya ta Tausheshi da Fadin Ka karka damu Bello ka Zurama Sarautar Allah ido kabarsu da Hukuncin Allah kamar yadda ka Fada Tun afarko kadan suka Fara gani.
Da Labarin ciwon Abba kabiru ya samemu ba wanda ya Tsausaya musu sai Ya muktar Daya kwashi Jiki yaje Dubashi kuma ya Zubemusu kudi masu yawa na Hidimar Asibiiti Shikanshi Hashim din bawai Kudin Yake dashi ba,Gabadaya Albashinshi Dashi yake Hidimar gidanshi Data iyayenshi,kasim kuwa bai san komai ba sai Shanshanci da Neman matan Banza babu Abunda yake Tsinanama iyayen,Abba garban ma Ta wajen Hashim ne yake samun Wani Abu domin kaf Dukiyar da suka hamdama ta Riga Ta kare ci tayi tayi kamar gara kafin su ankara ta kare,Taimakonsu Allah Aikin da Muktar ya samoma Kasim da Hashim Shine Rufin Asirinsu,Hatta karatun Zulfa da Zubaida duk Hashim din ne ke Daukan Nauyin komai Bawan Allah Duk ya Rame Lokaci Yana ta karban Laifin iyayensa ba laifi yana ji acikin Jikinsa.
Kasim kuwa sai ka Tsausayamai in ka ganshi Saboda yadda ya koma,kwana Hudu da Faruwar Abun Sakon Takardan Korar Shi Daga wajen aiki Wanda Haruna ya kawo mai har gida,Tare aka sallamesu saboda an diba Sabbin ma"aikata sai aka Rage Malalata wadanda basu da wani amfani,Zama sukayi suna ta kuka Lokaci Daya Da nadamar Rayuwarsu...
Jaririya kuwa An sakamata Suna Fauziya,ba wanda yabi takan Yimata Shakika,Mama Sahura da iyalanta Tuni sun koma gida sai dai tana zuwa Asibiti Kullum Tana Taya Umma zama wacce ta zama mara mgana sai dai Sharan kwallah,ita kanta Mama Sahura jikinta yayi sanyi ganin yadda Komai yake Faruwa Daki Daki Tana cikin Fargaban Su menene nasu sakamakon,Tunda shi kam Abba kaburu yafara kirban nashi Tun agidan Duniya,Shi kanshi Hashim shida iyalansa sun koma shi kuma ya koma bakin aikinsa,Zubaida ma ya Tafi da ita saboda karatunta ita kanta Duk Tayi sanyi Inna Rukayyah ma ta koma ita dasu Hamdiya,Abba garba ke kwana Dashi Su Umma na Wuni Dashi Kasim kuwa na gida yana Fama da Rayuwa Shi ke Rainan Fauziya wacce ake bata madara ya tasata yana kallo yana kukan Tsausayin Rayuwarsa
*****
Sati Daya mukayi a Abuja muka koma Kano Saboda Bello zai koma bakin aikinsa,tare da Hibba na Taho Tunda sun samu Hutun Makaranta,mun samu gidan duk yayi kura Dani Dashi muka zage muka Tsabtace ko"ina ya fita yayo mana sabon Cefane Tunda ya wanci Wadanda muka bari sun lalace sai muka Fitar muka Zubar,Salihu megadi sai Murnan Dawowarmu yake,yana ta Tambayan Modibbo muna munyi kewarsa sai dai muna mgana Lokaci bayan Lokaci Dashi ta waya,yana chan yana cigaba da karban Hora a makaratan Military Sch Jos.
Kwana 2 da Dawowarmu Bello ya Fara Attending Lectures dinsa,Murna wajen Sauran Daliban da malaman ba"a gama Student din Daya Fara Dauka Har suna Ug 2 Abun ba Wuya sai ya koma yana Daukan Tunda ga Ug1 zuwa 4,Tamkar baya komai nashi bai chnza ba Tuni Sunanshi ya Dawo yan mata suka Fara Rubibinsa kamar Baya da Tsoffin Wadanda Suka sansa Tun baya da Sabbin Shigowa,Tun bana ganewa har nafara ganewa Tunda wani Lokacin sai muna tare naga ana kiranshi ko Turamai sako baya maida kai,Nima ban wani Damu ba sanin Halin Mijina na taka tsantsan da Aji bazai iya Kula wata mace ba.
B.kaita ita tazo har gida ta ankarar Dani Domin kaf Buk ta Dauka da Zencen kyawun mijina da ajinsa Yanmata basa Jin kunyar Fadar Suna son Mr Bello ko kuma yana Burgesu Daga masu Fadin ya iya Wanka sai masu Fadin Dreesing dinsa ke Daukan Hankalinsu suna Fatan koda gaisawa suka Rinkayi dashi masu Burin Auraansa kuwa suna da yawa Harda masu Shan Alwashin koda boka da mallam ne,Sai sun Aure shi Akwai wadanda ke Fadin in yana Turanci kamar su saceshi sukeji.
Ranar da B.kaita tabani labarin nan Kamar zan mutu Saboda Kishi,domin akan Abunda ya Shafi Mijina Bani da Wasa Dama ga cikin jikina Wanda ya Shiga Wata na Shidda na lura ba karamin Sakani Fada yake ba Abu kadan za"amin yanzu zan Hau sama nayi ta fada wani Lokacin baya Biyemin sai dai ya kyaleni yamin Banza na gaji na bari wani Lokacin kuma ya toshe bakina da nashi ya shiga yimin Salonsa wanda bana iya Juya baya Saboda matuka gwarzona yasan Hanyoyin da zai sakani natsuwa Lokaci Daya Duk Fitinata na nemeta na Rasa sai ma kara kwakwumarsa Danake kamar wata mage.
Koda ya Dawo Bayan Sallar Isha"i bai Dade ba yace mu Shirya muje Waje muci Abinci Duk da ina jin Fitinata ban musamai ba na Shirya muka Fita Zuwa wani Restaurant Cin Abinci Ni dashi da Hibba wanda Dukkanmu muka Sha Kwalliya sosai,Tunda yaga Take take na sai bai Tankani ba Har muka isa wajen yamana Odar abunda muke so,An kawo mana ko Faraci bamu yi ba,wata budurwan mace Daga bayanmu tataso cikin Fara"a tana Fadin"Wow...So masha Allah Happy Family Mr Bello..."Tafada tana Shafama Hibba kumatu....
Dagowa nayi ina Kallonta cikin Takaichi na Hade Rai ina Hararanta Shi kuma sai ya basar dan yake yamata kafin yace"Thanks..."Daga Haka ya maida kanshi yafara cin Abinci Kamar baisan da Zamanta ba,Kallonsa ta karayi tana Fadin"Am Nadra Famtami Ur Student Mathematics Depertement...Level 1..."Bai Dago kai ba ya Gyada mata kai ammh kamar mayya tanace har tana kallona tana Fadin"Hy....Madam.."Ko kallonta banyi ba sai ma naji kamar zan saki kuka ganin yadda take kure Mijina da manyan Idanuwanta ko Taba abincin banyi ba Na mike na Fizgi Hannun Hibba muka Fice Daga Wurin bai Dago ba sai ma Mirmishin Daya saki Lokaci Daya.....
Cikin Mota muka koma Sai Da yadau Lokaci kafin ya Fito niko kafin ya Fito na cika nayi Fam Abun Haushi Tare suka Fito da wannan mayar yarinyar kuma suka Jero har wajen Motarmu Bakinciki kamar nayi Bindiga,Ina kallonsu ta cikin Mota har yana mata mirmishi Shiyasa koda ya Shigo Bangaren Direba na Kara Tamke Fuska Harda kau da kai Kallo Daya yayimin ya Dauke kai Cikin Ranshi kuma yana Mai Jin Dadin yadda nake nuna Kishi akanshi.
Har muka karisa gida ba wanda ya Tanka Dan"uwansa,Ban Jira ya Fito ya Budemin ba kamar kullum na Balle murfin Mota na Fice Hibba ma Datayi barci Shiya Daukota,yakaita har zuwa cikin Dayan Bedroom Din Datake kwana Koda ya Shigo namu Bedroom din na Fito Daga wanka ina Daure da Towel gaban Dressing Mirrior ina Tura baki Kallona yayi baiyi Mgana ba ya Sabule Rigar Jikinsa na Kamfanin DKNY,da wandon Ina kallonsa ban Tankashi ba ya Fada Tiolet Tsaki naja ganin yadda yayi Biris Dani Sama sama na Shafa mai na Saka wata Rigar barci Doguwa mai Taushi yana cikin Tiolet din na Bude na Shiga Yana tsaye Cikin Shower yaga Shigowata Cikina Daya bayanna yake kallo sai karamin Bakina Daya kusa Tabo Hancina saboda yadda nake Tura bakin,ko Barayinsa ban kallah na Sagala Towel na Shanya cikin Hangers dinsa na Fice da Kallo yabini yana Fadin yanzu zan yi maganinki nasan Abunda kikeso.
Kichen na Shiga na Hada Tea nasha Domin Yunwa nakeji,wajen Hibba na Leka na Ciremata kayan Jikinta na saka mata na barci na mata addu"a na Sake Lullube ta da Blanket,ban damu ba Saboda Dazu kafin mu Fita Tasha Tea so nasan Batajin Yunwa bedroom dinmu na Koma na iske ya Fito yana goge Jikinsa da karamin Towel din Dake hannunsa,gadon na Haye ina Kara Dunkulewa cikin Bargo lokaci daya ina Juya Baya
Yana saka Wandon kayansa na Pjms,yace mata"Haka zaki kwana da yunwa..."? Tana jinsa ta masa Banza,Mirmishi ya saki kafin yace"Ok...Bari nazo nayi Lallashin My Anee..."Yafada yana yar Dariya bai saka Rigar ba ya Hauro gadon ina Jinsa ya Shigo Cikin Bargon ya Rikoni nayi Saurin Zamewa ya kara Rikoni Sai na Fara Kokarin kwacewa,Da Sauri ya Saka Duka Hannuwansa ya Rikoni yana Fadin"Wai ni Duk miye Haka ne...? Kinfa san bana son Fushin Ba Dalili.."Yafada yana kara Tsananta Rikon Daya yimin ganin na kasa kwace kaina yasa nayi lamo ajikinsa,Lokaci Daya na sakamai kuka kaina ya Shiga Shafawa yana Fadin"Shi..iii...Gayamin Laifina Matata ni kuma zan nemi afuwarki.."Cikin Jan kukan Shagwaba nace"To..ba...ba kai bane kowa sai cewa yake yana sonka ance achan Jami"a kamar mata su cinyeka kuma naga Shaida Dazu da muka Fita cin Abinci.."Nafada ina Kara Sakin kukan Shagwaba Da Tabara.
Kara Rumgumeni yayi Lokaci Daya yana Kasa Da Hannunsa Zuwa Cikina yana Fadin"Karma ki Fara saka wannan acikin Ranki my Anee...Mijinki Is a Teacher kuma Dole zai yi Harka da Cakude cikin Mata da Maza Buh karki Taba Zaton Ni Bello Wata macen zata Taba burgeni Bayan ke...Bansan sunayi ba Kema kin sani Tun muna Zamfara...Kina da Shaida akaina Mata basa gabana Tunkafin nayi Aure balle yanzu Da kika zama uwar D"anq ko y'ata Dake cikin ki...Ki Rubuta ki ijiye Bello Muhammed Jikamshi is For Aneesa Bukar Bulama...Only U...Only U Aneeesaa....."yafada Cikin