Showing 33001 words to 36000 words out of 83144 words

Chapter 12 - MATA'UL HAYAT BY SAKINAT USMAN-1.pdf

02 Aug 2025

11077

saboda
haka kada ka yi mamaki.
Ya jinjina kai alamar jinjinawa, yace: Lallai kam kina da kokari tunda har kika yi wannan bincike,
amma dai duk da haka kin san wani abu?
Ya nemi kawar da wancan zancen tunda ya lura 'yar barkwanci ce. Ta girgiza kai, tare da fadar:
Sai ka fada.
Yace: Kin burge ni, har na ji ina son mu-amala da ke.
Ta yi murmushi, wanda ya bayyanar da siririyar wushiryarta, ba ta yi magana ba don haka ya ci
gaba cewa. Da gaske sunanki shuhuda, kuma wannan kasar kike?
Ta jinjina kai. Tabbas sunana Shuhuda Ibn Khaddab, mu uku ne gurin mahaifinmu, ni da 'yan
uwana Abubakar da Yusufa, iyaye da kakanni dukkansu 'yan kasar nan ne, sai me bayan haka?
Yana murmushi, yace: da ita: Lambar wayarki, da adireshin gidanku.
Tace: Tabdijan, lambar waya? Yanayinsa ya nuna tuhuma, yace: Ban gane mamakin da kika yi
ba?
Tace: Eh, to ni da ba zama kasa daya nake yi ba, wace lamba zan baka idan ba so kake ka yi ta
nemana ba ka samu ba? Yanzu ma fa kasar sudan zan je, kuma daga can wata kasar zan je?
Yanayinsa ya sake nuna damuwa yace: Ke kam duk me ya janyo miki wannan yawo haka sai ka
ce 'yar kasuwa?
Ta yi dariya, tace: Haba dai? Ai duk yawona ban kai TANZIF ba, wanda yana iya zuwa kasa
goma a kwana goma. Bare ni da idan na je kasa nakan samu kwana goma ban barta ba.
Isah yace: Waye kuma TANZIF? Tace: Ba ka sanshi ba. Yace: To amsa min tambayata me kike
zuwa yi kasashe?
Tace: Yawanci ina zuwa majalisi ne na malamai. Sannan nakan ta6a kasuwanci.
Ya jinjina kai. Cewa zaki yi Ustaziya ce? Don haka ma daga yau haka zan dinga kiranki
USTAZIYA SHUHUDA.
Ta duba agogon da ke daure hannunta tace: Ka ga har mun ci lokaci da yawa, sai nace sai gani
na biyu ke nan?
Ya yamutsa fuska yace: To idan kin ce sai gani na biyu ta ya zamu sake haduwa, ba ki bani
adireshinki ba?
Tace: Haka ne, amma.......
yadda TSAUTSAYI ya hada mu yanzu, a gaba KADDARA zata hada mu.
Yace: TSAUTSAYI KO KADDARA? Ban gane ba. Ta yi dariya wadda ga dukkan alamu dabi'arta
ce, dariya ba ta mata wuya. Tace:
Idan na ce TSAUTSAYI, ina nufin tsautsayin haduwarmu bayan kuma zamu dade ba mu sake
haduwa ba, wata kila kuma har abada.
Sannan idan na ce KADDARA ina nufin KADDARAR ALLAH ta hadamu sanadin mai sunana,
idan na biyota har kasarta don........
Karar maganar da ke fita daga abin maganar da ke kafe a gurin ta soma bayar umarni ana
neman wadanda zasu SUDAN don yin setting dinsu ta katse maganar da shuhuda ke yi. Tana
dan hanzari tace da shi.
SAI WATA RANA!
Ya yi sauri yace:
Dan tsaya na ba ki lambata........

Tace: A'a kada ka damu, sai ka jini.
Ba ta jira abin da zai kuma fada ba, ta yi gaba ta barshi galala da baki cike da alhini, wannan
yarinya da barkwanci ta ke.
Lokaci daya ya ji wani nishadi na kwarara a zuciyarsa, tunda yake a rayuwarsa bai ta6a yin
soyayya ba. Don haka ya kira abin da yake ji game da yarinyar SOYAYYA.
( Kai wannan gayen akwai shirme, yanzu dai naga ya nuna halin kanawa. Lolx)
Farad daya maganarta ta fado masa a rai, wai haduwarsu tsautsayi, abin da kuwa zai sake
hada su kaddarra, ke nan zata je Najeriya?
Mhm! Lamarinta gaba dayansa na barkwanci ne, don haka zuciyarsa ba ta aminta ita din 'yar
kasar Misra ba ce, ya fi kyautata zaton Najeriya ta ke, birnin kano, unguwar sallari tunda har
tasan sirrin ALAKA da ke tsakaninsa da Shuhuda, kuma ta yi ikirarin a sanadin kaddarar sunan
Shuhuda zata je Najeria unguwar Sallari wadda ta ke mu'amala da kanwarsa. Ba don haka ba, me ya hana ta kar6i lambar wayarsa tunda ita ba ta ba shi tata ba? Ai maganar
ji ma daban ta ke, kawai dai ita irin mutanan ce masu barkwanci da zolayar wanda Allah ya
hada su zama da su.
Yana nan zaune Dr. Outhman Ibn Abdulfatah ya iso airpot din, ba su wani tsaya ba suka
rangaya gidansa.
Duk yadda Dr Outhman ya so da Isah domin ya tsaya ya yi masa aiki, ya tubere sai dai ya ce
zai je Najeriya in yaso daga bisani idan mahaifansa sun aminta sai ya dawo. Kwanansa hudu,
Dr. Outhman ya sake masa visa ta zuwa Najeriya bayan sun je babbar kasuwar garin wadda ita
ce cibiyar kasuwar kasuwancin kasar, Isah ya duba zobe mai kyau na zallar azurfa ya sayawa
shuhuda a cewarsa wannan zobe shi ne babbar tsarabar da zai ba ta, tunda kullum suka yi
waya da ita ya tambaye ta abin da zai kawo mata tsaraba da shi, sai ta ce zobe. Wai ita a
rayuwarta babu abin da yake burge ta irin zobe, shi yasa ta ke matukar son a yo mata tsaraba
da shi. Burin Isah ya ganshi a birnin kano, ya ga yadda shuhuda ta koma. Yasan ta kara girma,
kyau da komai ma, tunda lokacin da ya bar kasar tana yarinya. Yana zaune a kujerar jirgin max
air ya tuna ranar da ya baro kasar shuhuda kuka ta ke kamar ranta zai fita, shi din ma har ya isa
kasar senegal kukan yake. Ya yi murmushi, rayuwa ke nan, komai mai cewa ne ban da ikon
Allah! Yau ga shi a cikin farin ciki saboda zai koma kasarsa ta haihuwa, zai koma cikin dangi,
'yan uwa, yarensa, addininsa gami da mu'amalolinsa da ya rasa su na tsayin wani lokaci, yau
duk zai cike wannan gurbin da ya samu gi6insu. Karfe bakwai na dare jirgin ya sauka a filin
sauka da tashin jirage na Malam Aminu kano, babu 6ata lokacin fasinjoji suka soma saukowa.
Alh sada, Alh Ahmad, Haj Asibi, Inna yaduwa da shuhuda su ne suka zo taryen Isah, saboda
haka yana fitowa daga cikin jirgin da su ya soma tozali. Wani yalwataccen murmushi ya saki,
yayin da shuhuda ta rugo da gudu ba zato ba tsammani Isah yaji ta rungumeshi. Wani irin tsau!
Ya ji a gaba daya sassan jikinsa, tsikar jikinsa ta tashi, amma ya kasa cire ta daga jikin nasa, shi
ma sai ya rungume ta tsam yana tuna tsananin shakuwarsu, yana tuna wannan rana da ta ki
goguwa a idanunsa da ma zuciyarsa gaba daya, wato ranar tafiyarsa Senegal. Sai da suka
dauki lokaci a haka, sannan Inna Yaduwa ta 6an6are shuhuda daga jikin Isah tana cew: Ke
sakar min miji kada ki karya min shi. Bayan an gama duk abin da ya dace, kai tsaye gidan Inna
yaduwa suka nufa don ta ce ita ce mai masaukin bako, shi ma dama gidan nata ya fi sha'awa
tunda a nan ya yi rayuwarsa kafin tafiyarsa Senegal. BAYAN WATA UKU Har su Shuhuda suka
kammala jarrabawarsu uncle hamza bai kulata ba, saboda a lokacin ya gama amanna ita din

aljana ce, amma duk da haka ya kasa samun sukuni, kullum tunaninta ne ke nukurkusar
zuciyarsa. Sai dai da yake shi din jarumin namiji ne haka ya daure yana ji yana gani har suka
kammala jarrabawarsu suka bar makarantar. Wanda hakan ke nufin rabuwarsu ta har abada
musamman wannan lokaci da abin al'ajabin ya faru. Lokacin da Goggo binta ta ce shuhuda
mayya ce, wanda shi kuma ya karyata hakan ya fi alakantata da aljana, to tunda dama
makarantar ce ta hada su yanzu kuma ta raba su. A 6angaren su shuhuda kuwa, shakuwar da
aka ginata a 6angaren su shuhuda kuwa, shakuwa da aka ginata a wancan tubalin na aminta
da kuma kuruciya an sabuntata ta dawo sabuwa dal! Don yanzu kam shakuwar da ke tsakanin
shuhuda da Isah har ta zarta ta wancan lokacin. Kullum suna tare, hira suke yi yana ba ta
labaran abubuwan da suka faru da shi a kasar senegal har tuhumarta ya yi ko tasan wata
shuhuda ibn khaddab, amma tace ita sam ba tasan wata shuhuda ba, ita ba tama ta6a jin mai
sunanta ba, don wani lokaci ma har tana tababan ingancin sunanta. To shi ma sai bai tsawaita
bincike ba, don dama shi mutum ne mara son shiga harkar da ba tashi ba. Ana gama sallar
isha'i ne yake shigowa dakin Inna yaduwa ya ci abinci tare da shuhuda, sannan ya zauna da su
hira har sai karfe tara da rabi sannan yake yi musu addu'a ya ja musu kofa ya nufi 6angarensa.
Wannan dabi'a ce da yake gudanarwa tun ranar da ya dawo, saboda haka babu wani guri da
yake zuwa da daddare. A 6angaren maganar aikinsa kuwa Alh Rabi'u yace:o sam bai amince
Isah ya koma wata kasa ba, shi ma ya tsaya ya amfanawa kasarsa, tunda ana bukatarsa. Bai
damu ba, don tunda ya dawo ya dora idanunsa ga shuhuda sai ya ji sam baya bukatar abin da
zai kuma janyo masa ya yi nisa da ita. Saboda haka aka soma nema masa aiki a kamfanoni da
dama, duk da an yi tunanin bude masa kamfani na kashin kansa, to amma sai aka dakatar da
wannan yunkuri saboda halin da ake ciki na karyewar tattalin arziki na al'umma. A haka har ya
samu watanni uku da dawowa, izuwa wannan lokacin yana cikin wani hali wanda shi kansa ba
zai iya kwatanta shi ba, domin dai ji yake kamar yana son ya auri shuhuda, kullum ta kawo
masa abin karin kumallo ko na rana ko kuma idan suna hirar dare, wani irin nishadi yake ji na
kwaranya masa. Idan ya gama yi musu hira ya koma dakinsa kafin bacci ya dauke shi,
tunaninta ne ke bijiro masa ya dinga ganin kamar tana yi masa gizo. Da gaske babu tababa
yana sonta, kuma yana son aurenta, amma ya kasa fada mata koda kuwa Inna yaduwa ya kasa
fadawa, hatta da Alh Rabi'u wanda duk bayan, ya kasa 6usa masa maganar. Daga shi sai
zuciyarsa, sai kuma Masanin halin da zukata ke ciki(Allah)
BABI NA TAKWAS .......... RUWAN ZUMA Inna yaduwa tana zaune a falo ita da dattijon mijinta
tana 6are masa gyada mai 6awo yana taunawa a bakinsa, shuhuda ta shigo falon cike da
murna kira ta ke. Inna! Inna kina ina? Tayi tsalle ta haye kan cinyoyin kakar tata, yayin da Isah
ya shigo shi ma fuskarsa dauke da fara'a. Inna yaduwa tana kokarin tureta daga jikinta, tace: Ke
ni daga ni shagwa6a66iya kawai, zaki wani shigowa mutane gida ba ko sallama. Alh Rabi'u ya
dubi Isah yace: Abokina ya dai na ga amaryar tawa tana murna tamkar ranar sallah? Isah yace:
Wallahi Baba takardunta ne suka yi kyau shine ta ke ta murna, tun fa a mota ta ke ta wannan
murnar. Gaba dayansu sai farin ciki ya kamasu.
a Hada Hausa Book stories
MATA UL HAYAT(JIN DADIN RAYUWA)
¤¤17¤¤
Alh. Rabi'u yace: Nima ba na shakka akan kwalwar amaryata, Allah ya sanya alkhairi.
Shuhuda ta washe baki tace: Amin Baba.

Ta ci gaba da zuba shagwa6ar farin ciki, Isah yana kallonta, yau hakurinsa ya kare, yana ganin
rana ce da ya kamata ya yi amfani da ita ya sanar da shuhuda matsananciyar kaunar da yake
mata. Ko ba komai ranar za ta zamo ta kafuwar tarihi masu dama a kundin rayuwarsa. Misali:
Yau ranar ta kasance ta LITININ takardar shaidar tabbatuwar aikinsa da kamfanin NUEFI'A
IRONIC METAL da ke jihar Ibadan ta same shi.
Ranar LITININ shuhuda ta dubo jarrabawarta Waec da Neco duka ta cinye, tana A1 a wasu
darussan B3 a wasu.
Sannan ranar LITININ zata zamo cikin jerin abubuwan tarihi idan ya furta mata KALMAR SO.
Shuhuda ce ta katse masa tunani lokacin da ta mike tsaye. Inna bara na yi wanka tukunna na ci
abinci ko? Ba ta jira amsa ba ta nufi hanyar daki don sauya kayan wanka.
Isah ya bita da kallo, tafiyarta ma dagwas-dagwas gwanin sha'awa. Shi ma sai yace: Bara na je
daki na huta.
Alh Rabi'u yace: Anjima idan an gama sallar magriba ka zo zan aike ka gurin mahaifinka ka kai
masa wasu kaya da a ka kai masa aikin hannu.
Isah yace: To. Sannan ya koma dakinsa yana ta kissima yadda zai tunkari shuhuda da
bukatarsa ta soyayya, shin ko za ta amince ko ba zata amince ba?
Karfe hudu da rabi na yammacin ranar ya tarar da shuhuda zaune akan farar kujerar roba tana
sanye da dorawar shadda shar da ita, dinkin fitted, rigar ta matse ta sai dai ba yadda al'aurarta
zata bayyana ba, sannan zani ce aka yi mata don haka kwalliyar tata dai babu makusa.
Fuskarta narai-narai, har yanzu da akwai wannan murnar ta cinye jarabawa a tare da ita tana
makale a fuskarta.
Kafin ya karasa gare ta ya yi tsaye yana kallonta, lallai idan ya sami nasarar auren shuhuda ya
dace da kyalkyawar mace, wadda zata haifa masa kyawawan 'ya'ya. Sannan kamilar mace ce
idan aka yi la'akari da yanayin shigarta.
Dubi dai yanzu yadda ta ci ado ta kame akan kujera, yadda kasan wata babbar mace ce ita,
bayan duka-duka shekarunta sha takwas.
Kamar an ce daga kai! Ta dago kanta saboda kamshin turaransa da ya buwaye ilahirin gurin,
suka yi tozali da juna. Sai ta sakar masa murmushi.
Ya tako a hankali ya ja kujera ya yiwa kansa mazauni, ta gayar da shi sai duk suka yi shiru shi
da ita bayan gaisuwar, kanta na rusune a kasa yayin da shi kuma gaba daya ya dauki idanu ya
daura mata.
Shirun dai ya dauki 'yan mintoci kafin Isah ya katse musu shirun da yin gyaran murya yace:
Shuhuda!.
Ta dan dago kanta kadan tana satar kallonsa. Yace: Kin san me? Tayi shiru ba ta ba shi amsa
ba. Ya ci gaba da cewa:
Wata magana ce mai muhimmanci nake son mu yi da ke, amma ina bukatar ki tattaro hankalinki
da nutsuwarki zuwa gare ni. Kuma ina son ki fadan gaskiyar abinda ke cikin ranki.
Ba ta dai tanka ba, amma yanzu gaba daya ne ta ke kallonsa sa6anin dazun da kadan ta daga
kai.
Ya kuma saka nutsuwa a tare da shi sannan muryarsa kasa-kasa kamar ba ya son wani ya ji.
Yace:
Ko kin san me ye SO?
Yanayinta gaba daya ya sauya, 6acin rai ya bayyana a fuskarta, ta yi shiru ba ta tanka ba, kuma

ba ta dauke idonta akan kwayar idonsa ba. Ya lura ba tasan so ba, wata kila ma ba ta ta6a yin
katari da wanda yace yana sonta ba.
Shi kam hakan ya yi masa dadi sosai, saboda hakan zai ba shi damar kafa soyayyarsa a
zuciyarta. Sai yayi murmushi mai kayatarwa ga wanda ya san sirrin murmushi, sannan yace da
ita.
So wata kwaya ce da ke kafuwa a zuciya ta sababin wasu abubuwa masu muhimmanci, na
farko KYAU, Idan mace ko namiji na da kyau, yana iya haduwa da masu sonsa ta sanadin
wannan kyawun da Allah ya yi masa baiwa da shi.
ADDINI:- Idan mace ko namiji suna da addini ana iya sonsu saboda addinin da suke da shi.
Ma'ana sun kasance masu yawan yin sallah akan lokacinta, kyautata addininsu da sauransu.
NUTSUWA:- Ita ma tana kawo a so mutum saboda ita.
KWARJINI:- Akwai mutanen da kwarjini ke sa a so su, ba don kyau ko addini ba, kwarjininsu zai
sanya kawai idan aka gansu aji ana sonsu.
ASALI:- Nagartaccen asali yana sa a so mutum saboda an san asalinsa, tun daga nasabarsa
zuwa mu'amalolinsa.
SHA'AWA:- Akwai mutanen da Allah ya yi su da raunin sha'awa, ma'ana idan za su ga mace ta
yi shiga ko tafiya mai kyan tsari zasu kasance cikin sha'awar yin tarayya da ita, ba don asalin
son ko kauna, illa sha'awar ce ta yi jagoranci.
A mafi yawan mutanen da suke soyayya sha'awar ce ke yi musu jagoranci, shi yasa ake yawan
samun ma.......
Maganarsa ta katse sakamakon kwalla da ya gani shar a idanuwan shuhuda. Hankalinsa ya
tashi, cikin rawar murya yace:
Sh....u.....hu......da........?
Ta rusunar da kanta kasa, ya matso kusa da ita cikin tausasawa yace:
Me ye na kuka? Ki fada min maganganuna ne suka 6ata miki rai?
Ta yi shiru tana shesshekar kuka, hankalinsa ya sake dagulewa, sai yake tunanin wata kila ta
ta6a yin soyayyar, ko saurayin ya sota ne akan turbar SHA'AWA. Yanzu da yayi mata wadannan
bayanan ta samu tabbacin sha'awar ce tsakaninta da shi.
Ko kuma ta yi soyayya da wani saurayi da yakan zaunar da ita ya yi mata kwatankwacin
wannan bayanai, daga bisani Allah ya yi masa rasuwa.
Idan kuwa wannan zargin ya zama gaskiya, yana da yakinin ba karamar wahala zai sha ba
kafin ya rushe wancan tubalin ya kafa nasa tubalin soyayyar ba.
SO RUWAN ZUMA, dole ne sai ya yi amfani da sanyayyen kalamai masu nutsar da zuciya gurin
kawar mata da tunanin duk wani da namiji a rayuwarta, saboda haka ya ciro hankici daga
aljihun rigarsa da nufin goge mata hawayenta.
Amma koda ya nufo fuskarta da nufin hakan, sai ta yi sauri ta kawar da kai gefe guda.
Ya yi murmushi yace:
To ki daina kukan idan ba kya son na goge miki hawayen.
Ta sa hannu ta goge hawayen, yana kallon kanta don fuskarta na rusune, yace: Shuhuda ina
sonki!
Mikewa tsaye ta yi da sauri tana girgiza kai, muryarta na fitar da wani irin yanayi.
Bana soyayya saboda hatsarinta a gare ni. Bata bari ya yi magana ba ta ci gaba da cewa:
Bana soyayya saboda amsa tambaya, ita kuwa soyayya tana tafiya ne da amsa tambaya.

Bana soyayya saboda ban cancanta da ita ba.
Bana soyayya soyayya saboda ba zata sama min MATA'UL HAYAT ba, illa bankado da TASHIN
HANKALI, wanda zai iya shafar duk wanda ya shafe ni.
Wani hautsinannen kallo yake mata na tuhuma, amma ba ya son tuhumarta tunda ya ga akwai
mikin tabon soyayyar wani a zuciyarta, hanyoyin kafuwar tashi soyayyar ita ce a gaban shi.
Na ji, amma na tambayeki mana?
Ta daga masa hannu.
Na fada maka bana iya amsa tambaya, don ni kaina, ina da tambayoyin da zan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login