Showing 57001 words to 60000 words out of 111817 words

Chapter 20 - 'YAR KARUWA Book 1 by Uwar Batoorl.pdf

Advertisement

16 Aug 2025

4092

Ko da
mahaifina na raye ko ba ya raye ai ya kamata ki haɗa ni da danginsa saboda su ne gata na, kuma su za su
shiga tsakanina da masu yi mini gori, Mami wallahi ko shegiya kika haife ni to haɗa ni da mahaifina ya fi
wannan hukuncin naki kamata, kuma ni na yafe muku ina ƙaunarki a haka ke da mahaifi na, in ma ba ta
hanyan da ya dace kuka same ni ba, na ɗauki ƙaddarata ta zamowa ƴar shege.........."

Tasss!!Tasss!Tasss!!!!, Shi kawai kake ji Mami ta kwashe Banafsha da wasu mahaukatan maruka, idanuwan
Mami jajazir kaman garwashin wuta ta ce, "Banafsha ni kike wastawa wannan kalaman? Banafsha har ni za
ki saka a gaba kina mini magana kaman ƴar cikinki? To wallahi kin ji na rantse ranki zai yi mugun ɓacuwa
akan rashin kunyan da kike mini, har kina ƙiran kanki shegiya kina faɗa mini kenan me nayi na haifeki?
Banafsha...." Maganan bakin Mami ne ya sarƙe sai ga hawaye a idanuwanta, saurin juyawa tayi dan kar
Banafsha ta gani, abinda bata sani ba kuwa duk da yanayin da nake ciki naga zubowan hawayenta.

Mami juyawa tayi tana ƙoƙarin danne hawayenta amma ina sun ƙi stayawa, ɗakinta ta shige kawai ta kulle,
kan gado Mami ta faɗa tare da sakin sabon kuka tana jin duk abinda ya faru shekaru ishirin baya yana
dawo mata sabo dall kaman yau abin ya faru, cikin kuka ta ce, "Duk wanda ya aikata wannan mummunan
tabo gareni in har da son ransa ban yafe masa ba duniya da lahira, in kuma shi ma bai yi da niya ba na yafe
masa, amma duk mai hannu a faruwan wannan mummunan ƙaddara gare ni Allah zai saka mini, ban yafe
ba, ban yafe ba, ban yafe ma ko waye ne ba, astagfirullah Ya Rabbi!..." Haka Mami ta dinga sumbatu tana
kuka, saboda duk maganan da Banafsha take faɗa mata baya damunta sosai, amma maganganun yau ya

soketa sosai, ya tuna mata da abinda bata son tunawa a rayuwanta, ya tuna mata da lissafin da ta jima da
cire shi a rayuwanta, ta stani baya bata son tuna baya domin bata ji daɗin baya ba, haka Mami ta dinga
kuka har sai da kanta ya fara mata mugun ciwo.

Banafsha kuwa Mami na barin wajan ita ma ta ɓarke da nata kukan mai cin rai, ga ciwo a zuciyanta ga
ciwon mara, ita ji take ma ta Mami ta bugeta har ta kasheta da ya fi mata daɗi, ko kaɗan bata ji zafi ko
raɗaɗin marukan da Mami ta mata ba, kuka take kaman ranta zai fita, gaskiya ce ta faɗa wa mahaifiyarta,
amma kuma ba wai dan ta sanya ta a damuwa ta saka ta zubar da hawayenta ba, lallaɓawa Banafsha tayi a
dudduƙe ta ja jikinta ta ƙarisa ƙofan ɗakin Mami, tana turawa ta ji a kulle, a hankali da muryan kuka ta ce,
"ki yi haƙuri Mamina, Allah ya huci zuciyanki, ba niya na saka ki a damuwa ba, niyana tunatar da ke da
kuma baki shawara a mastayina na ƴar ki, Mami auren Abbaa Insha Allah alkairi ne gare ki Mamina, ki yi
haƙuri ki auri Abbaa, shi cikakken me ƙaunaki ne Mami, wallahi ni nasan Abbaa zai fi Alhaji riƙe ki da
amana, ki yi haƙuri Mami."

Mami bata yi niyan yin magana ba, amma jin abinda Banafsha ke faɗa sai wani abun ya ƙara tokareta,
stawa ta daka mata ta ce, "Banafshaaa! Ki ɓace mini a ƙofa kamun na fito na saɓa miki, shashashan
yarinya wacce bata gudun ɓacin ran mahaifiyarta, duk haƙurin da nake akan rashin kunyan da kike mini, ke
burinki kawai ki sa na miki baki ko? To ki cigaba kada ki dena zan miki bakin da kike so na miki, ɓace ki bani
waje."

Na buɗe baki zan bai wa Mami haƙuri, ta kuma sake mini wani gigitaccen stawan da ya saka ni barin ƙofan
ɗakinta ban shirya ba, marana mugun murɗa mini yake ga kukan da nayi, tuni zazzaɓi yake son mini
mugun kamu.

Umaima bayan ta je tahfiz an tashi, Malam Abbo ya ƙara ba da saƙon gaisuwa zuwa ga masoyiyarsa
Banafsha, Umaima ko da ta dawo bata shiga gidansu ba sai ta yi hanyan gidan su Banafsha, kuma dai-dai
lokacin Umma ta fito a gida kenan, wani irin mugun kallo Umma ta bi Umaima da shi, tuni Umaima ta sha
jinin jikinta tare da fara yarfe hannu dan tasan yau sai dai ɗan buzunta, Umma fasa fita tayi ta juya cikin
gida, Umaima haka ta bi bayan Umma tana faɗin, "Ƙulya ƙulle bakin Ummana".

Ummu tana zaune a palour, tunda ta ga yanda Umma ta shigo sai ta girgiza kai kawai dan bata san me
kuma ya faru ba, Umma dakinta ta shige tana ƙwafa dan yau ba mai hanata daka Umaima sai ikon Allah.

Umaima haka ta shigo tana raɓe-raɓe kaman wacce ta yiwa sarki sata, Ummu tana ganin Umaima tasan to
da wani abun, kamun Ummu ta buɗe baki Umaima ta ce, "Ummu ki bawa Umma haƙuri kada ta dake ni,
wallahi saƙo na je kai mata malaminmu ne ya aike ni wajanta."

Ummu da ba ta gane ba ta ce, "Wajan waye kuma aka aike ki, kin dawo makaranta ba za ki taho gida ba,
ina kika bi har Ummanki ta haɗu da ke a can."

Umaima kaman za ta yi kuka ta ce, "Ummu wallahi ba inda na je, gidan su Banafsha ne kawai, kuma ban
shiga ba da naga Umma."

Ummu shiru tayi kawai ta rasa me za ta ce, dan tasan muddim Umma za ta daki yaranta, to bata isa ta ce
ƙala ba, in ma ta saka baki to yanzu kuma faɗan zai dawo kanta.

Umaima ta yi rau-rau da ido ta ce, "Dan Allah ki bata haƙuri Ummu."

Ummu ta buɗe baki za ta yi magana sai suka jiyo muryan Umma tana faɗin, "Dan ubanki, kin staya a wajan
uwarki ta biyu ko ba za ki zo ba ina jiranki."

Umaima baya-baya ta fara za ta juya, sai Ummu ta girgiza mata kai ta ce, "a'a kar ki gudu Umaima, kije ki
bata haƙuri, babban budurwa da ke Ummanki ba za ta dake ki ba, faɗa za ta miki kuma ko me ta ce ki bata
haƙuri, ki ce kin ji kin daina."

Umaima ɗaga kai tayi tana tafiya a hankali kaman wanda ƙwai ya fashewa a jiki, har ta shiga ɗakin Umma
da sallamanta, Umma kuwa ko amsawa bata yi ba ta miƙe ta saka wa ƙofanta sakata, mugun kallo ta
jefawa Umaima ta ce, "Me na ce miki ranan? Wato sai dai na stine miki ki lalace nine da asara ba uwar
kowa ba ko? To kuwa ko ban stine miki ba zan daka ki sai na sauya miki kamanni, idan tare aka haifo ku da
ita za ki faɗa mini yau."

Umaima ta buɗe baki za ta bawa Umma haƙuri, amma ina sai sauƙan bulala ta ji a jikinta ko ta ina,
Umaima na ihu, Umma na dukanta kaman an aiko ta bata fasa ba.

Ummu na zaune a palour, tana jin ihun Umaima ta taho da sauri duk da bata shiga ɗakin Umma, amma ta
tura ƙofan da niyan shiga, sai ta ji da gam a garƙame da sakata, magana take tana faɗin, "Dan Allah dan
Annabi SAW ki ƙyaleta ki yi haƙuri Maman Kabeer, ki bar dukanta haka nan...." Magiya Ummu ta dinga yi
amma Umma ko jin ta bata yi ba, balle ma ta saurareta kawai jibgan Umaima take yi.
Umaima tun tana kuka da ƙarfi har ta zube a waje guda muryanta ya dishe, ba abinda take faɗi sai, "ki yafe
ni Umma, ki yi haƙuri ba zan ƙara ba, wallahi Abbaa ne ya ce muje, ki yi haƙuri Umma ki mini rai, zan
mutu, wayyoooo! Ummuna!!!" Umaima na faɗan haka ta sume.

Umma duk da Umaima ta sume amma dukanta take zuciyanta kaman zai faso ƙirjinta ya fito, magana take
kaman zararriya, "Ni za ki mayar ƴar iska bansan me nake yi ba, wato kin faɗawa ubanki sai ya saka ki gaba
kuka je, ban isa da ke ba, to gwanda ma na kashe ki na huta da ki kasheni da naki takaicin, har da ke ubanki
zai je zance, duk munafurcinku ne ya ja in ba haka ba, me za'a yi da karuwa a kishiya, ai sai ta addabi kowa
ta ishi kowa ta nemi ɗaga mutum akan yaransa..." Umma tana magana tana dukan Umaima tana haƙi, har
sai da ta ji kaman za ta sume ita ɗin ma, sannan ta jefar da bulalan ta jawo ruwa ta kwankwaɗa ta wastawa
Umaima, wani wawan ajiyan zuciya Umaima ta sauƙe tare da sakin marayan kuka tana numfashi a
hankali-hankali.

Ummu kuwa da ta gaji da magiyan, ficewa tayi ko ta duba samarin gidan amma ba kowa, Abbaa ma bai
dawo ba, haka ta dawo cikin gidan lokacin Umma ta gama jibgan Umaima, Ummu kaman za ta yi kuka haka
ta koma ƙofan ɗakin Umma, amma har lokacin bata buɗe ƙofan ba, ƙarshe Ummu ɗakinta ta koma.

Umaima na zube a wajan, Umma ko ta kanta bata bi ba, ta shige bayi ta wasta ruwa, ƙwafa tayi tare da
kallon Umaima ta ce, "tashi ki fice mini a ɗaki, idan kin so gobe na hanaki yin abu ki yi, idan yayanki ya
dawo kuma na faɗa masa ya ƙara miki, kinsan dukansa kuma sarai."

Umaima ko yastanta ta mosta raɗaɗi take ji, dan ta daku sosai ba ƙarya, Umma tsawa ta mata, dan dole
Umaima ta ja jikinta tana kuka ta shige ɗakinsu, ga shi Ummu bata san ta fito a ɗakin Umma ba, haka ta
zube a stakar ɗakinsu tana kuka har baccin wahala yayi gaba da ita.

Ummu kuwa tana ɗakinta, bata san Umaima ta fito ba, har Abbaa ya dawo a palourn sa na cikin gida ya
gama komai ya tafi wajan Mami, har ya dawo duk bai san wainar da ake toyawa ba a cikin gidan, sai da ya
shigo ciki ya ji gidan shiru kaman ba kowa, ɗakin Umma ya fara shiga sai ya sameta tana sallah, juyawa yayi
ɗakin Ummu, samunta yayi ta haɗa hannayenta ta tallafe kuncinta, Abba ƙarisawa yayi wajanta ya zauna
tare da cire mata tagumin da ta yi, Ummu ɗagowa tayi ta kalli Abba sai kawai ta faɗa jikinsa tana faɗin,
"Dan Allah kabar maganan auren Mamin Banafsha, ka yi haƙuri, kuma ka ce Umaima ta bar shiga gidan,
komai ya wuce, zaman lafiya ya fi zama ɗan Sarki."

Abbaa kallonta yayi ya ce, "Me ya faru? Me yasa kika ce haka? Bayan ke kika kawo shawaran kuma na
amsa, meyasa?"

Ummu kaman za ta yi kuka ta ce, "nidai dan Allah ka bari, nasan ni na bada shawara amma kuskure nayi,
dan Allah ka mance da batun ka ji Alhaji."

Abbaa miƙewa yayi ya ce, "Ba zan zamo mutumin banza ko kuwa mijin da ake juyasa ba, ke kika yi magana
ba ni na ce ba, dan haka bakin alƙalami ya riga da ya bushe, na samu Ramla na faɗa mata abinda ake ciki,
yanzu haka amsanta nake jira, kuma ina da tabbacin amsan nata eh ne" yana gama faɗa ya nufi hanyan
waje fiska ba sassauci, ta ya za ta ce abu kuma yanzu ta ce a'a idan ba ta renasa ba, to shi ya riga da ya
sakawa zuciyansa son Mamin Faɗima, kuma idan har bai aureta ba Allah ne kawai bai nufa ba.

Ummu jiki a sanyaye ta ce, "ka yi haƙuri Abbaansu ba nufi na kishi nake yi ba, duk da nasan kishi dole na yi
sa tunda ina ƙaunanka, amma ba hakan bane dalilin maganana, ka je ɗakin Maman Kabeer ka duba halin
da Umaima ke ciki, na tabbata kai ma za ka fahimci janye maganan nan shi ne alkairi da zaman lafiya."

Abbaa bai kuma cewa da Ummu komai ba ya fice a ɗakin, ɗakin Umma ya koma lokacin ta idar da sallah,
ba murmushi ba komai kaman an mata dole ta ce, "Sannu da dawowa."

Abbaa ko ta sannunta baya yi ya ce, "Ina Umaima?"

Umma taɓe baki tayi ta ce, "tana ɗakin su."

Abbaa bai ce komai ba ya juya, da sallama ya shiga ɗakin su Umaima, bai ma kula da ita a stakar ɗakin ba,
sai da ya ga bata kan gadonsu sannan idanuwansa ya sauƙa a stakar ɗakin, da mugun sauri Abbaa ya nufe
ta a rikice yana faɗin, "Ummu-khultum lafiya?"

Umaima ta jima da tashuwa daga baccin wahala, amma zuwa lokacin jikinta yayi stananin stami, ba abinda
take sai aikin nishi, ko da taji Abbaa na ƙiran sunanta ba daman amsawa, sai kuka ta sanya wanda idan ba
kana kallonta ba, ba za ka ji sautin kukan ba saboda yanda muryanta ya dishe.

Abba yana taɓa jikinta yaji yayi zafi sosai, ya juyo da ita kuwa ya ga fiskan a kumbure alaman ta sha kuka,
kallonta yayi cikin damuwa ya ce, "Me ke damunki Umaiman Abbaa?"

A hankali take mosta laɓɓanta tana jan zuciya ta ce, "Umma ceeeee" ta ƙarishe maganan kaman za ta
sume.

Abbaa ficewa yayi ya nufi ɗakin Umma, amma ya samu ta kulle ƙofa, bugawa yayi taƙi buɗewa, ɗakin
Ummu ya koma ya ƙirata, tana shigowa ta kalli Umaima sai ta fara hawaye tana mata sannu, Umaima
lumshe ido tayi cikin azaban da jikinta ke mata, Abbaa ya ce, "Khultum shiryata mu tafi asibiti" yana faɗa
ya fice.
Ummu haka ta ƙoƙarta ta ɗaga Umaima ta ja ta banɗakinsu da ke cikin ɗaki, ruwan zafi ta koma ta ɗauko a
ɗakinta ta zo ta haɗa ruwa, kamawa Umaima jikinta tayi, ta mata wanka ta shiryata sannan ta yiwa Abbaa
magana akan ta gama.

Abbaa da kansa ya ɗauki Umaima suka fice a gidan, asibiti ya kai ta a cikin gari, sai dai an kama su a gado,
dole Ummu ta kwana a asibiti, shi kuma Abbaa ya koma gida, bai bi ta kan Umma ba dan tabbas zai yi
abinda ba dai-dai ba, mataki ne kuma ya ɗauka, in Allah ya yarda zai auri Mamin Faɗima ya ga ta ƙarshen
rashin mutuncin ta.

Ɓangaren Mami da Banafsha haka suka kwana, ba wanda ya fito balle ya sa wani abu a cikinsa, Mami sai
da dare tayi sosai sannan ta fito ta zo ɗakin Banafsha, samu tayi tana bacci jikinta da zafi, kayan jikinta ta
rage mata ta share mata jiki da towel mai sanyi, sannan ta tofa mata addu'a ta ja mata ƙofa ta koma nata

ɗakin, alwala Mami ta ɗaura ta dinga sallah, har sai da ta ji ƙiran assalatu, bayan tayi sallahn asuba tayi
ayyukanta ta gyara gidan staff, ɗakin Banafsha ta shiga ta sameta ta fito wanka kenan, Mami murmushi ta
sakar wa Banafsha ta ce, "shalelen Mami har an tashi, fatan jikin da sauƙi?"

Banafsha wani abu ne ya soki zuciyanta, sai take jin sam-sam bata kyauta ba duk da gaskiya ce, amma
Mami bata chanchanci haka daga gare ta ba, hugging na Mami ta yi ta amsa da sauƙi, ta gaisheta ta amsa,
Banafsha ta ce, "ki yi haƙuri Mamina."

Murmushi Mami tayi ta ce, "ya wuce Allah miki albarka, Allah shirya mini ke."

"Ameen Mamina" na amsa ina murmushi, haka na gama shiri muka fice da Mami muka karya, yau ma ba
iya zuwa makaranta zan yi ba Mami ta ce na bari sai wani Monday kawai, muka zauna muna hira Mami na
ƙara mini faɗa.

Haka rayuwa ta dinga tafiya har aka cinye wannan sati Banafsha bata je makaranta ba, kuma sai da ta cika
kwana bakwai ciff sannan ta samu sauƙi ranan Lahadi, Umaima ma duk sauran kwanakin bata je
makaranta ba, kwanan su kusan huɗu a asibiti sannan aka sallamesu, har Ya Mus'ab ya zo shi ma daga
Camaroon duba jikin Umaima, Ya Kabeer su ya Sadeeq su ya Farooq duka, kowa duk ya ji abinda Umma ta
yi amma ba daman magana sai ido, Abbaa ma idon ya zuba dan shi ya gama ɗaukan nasa matakin, Ummu
kuwa bata da bakin magana tunda gori Umma ke mata ko ta yi magana ta ce ai ba ƴar ta ba ce, haka ta
dinga jinyan Umaima har ta warke, ya Danish ne kawai bai zo ba kwata-kwata ga shi har weekend ya ƙare
yau Lahadi.

Ɓangaren Malam Abbo kuwa ganin Umaima ma ta daina zuwa makaranta kwana biyu ba ya jin halin da
masoyiyarsa ke ciki, tuni hankalinsa ya tashi, haka a daddafe ya daure har sati ya cika, ranan Lahadi da
yamma ya sha wankansa ya chakare ya shirya rass ya nufi gidan su Banafsha, farinciki kawai yake ciki da
ɗauki gani yake ba ya isa da wuri saboda yanda yake ɗaukin son ganin abar ƙaunarsa, Sayyadarsa, Malama
Faɗima.



Bunayd hutawa yayi sosai ba wanda ya san yana sashinsa a gidan, sai da General ya ƙirasa a waya sannan
ya faɗa masa ai yana cikin gida ma tun da ya dawo ya taho gidan, General mayar da wuƙan yayi ya kashe
wayan yana sakawa Man nasa albarka.

General layin Suhail ya kuma ƙira yana ɗauka ya rufe shi da faɗa ya ce, "Suhail ina ce dai ba gidan ubanka
ba ne a Turkish ɗin nan ko? To idan ka kuskura gobe ba ka dawo ba sai na ƙwace har jarin da yayan naka ya
baka, sai naga ta inda za ka zauna a ƙasar mutane babu kuɗi."

Suhail murmushi yayi da haɗaɗfiyar muryansa ya ce, "sorry General! Na gama shirin komai jirginmu da
asuba zai tashi."

Ƙwafa General yayi ya ce, "Idan ma baka dawo ba kasan abinda zan iya yi, dama har yanzu ban huce da ƙin
aikin soja da ka yi ba, kuma ka zo kana zuga mini yarona Nabeel."

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login