Showing 1 words to 3000 words out of 78880 words

Chapter 1 - YAR KANCE free pages na Maman Abdallah.doc

??ࡱ?>?? d
????????????? ?
????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????a
? 

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?Fe
WordDocument????1j0Table????????)Data
???????????????????? P??? KSKS?1jVP?????????""""""???,"@)))))))W%? (>?""))"""")G(?"G()")G("))"" ?V`??VNormal $a$1$$CJKHmH sH nHtHOJPJQJ```Titre 1$$???@&#5B*
CJOJPJQJ\aJph6_?```Titre 2$$???@&#5B*CJOJPJQJ\aJphO??X`XTitre 3$$???@&5B*OJPJQJ\phO??bA`???bPolice de paragraphe par d?faut OJPJQJJ?o???JTitre 1#5B*
CJOJPJQJ\aJph6_?B?o???BTitre 35B*OJPJQJ\phO??J?o???JTitre 2#5B*CJOJPJQJ\aJphO??VP??L
p ? 4`??2`??.b?? j!?"$h%?&?'J)?*?+-|.?/1?2?3>5?6?7$9t:?;=n>??AhB?C?DhF?G4I?J?KMPN?O?PRZS?T?U6W?X?Y [n ?AR KANCE
Labari da rubutawa
By
Khadijah Bashir
(Maman Abdallah)



Littafin ?ar Kance ?irkirarren labari ne idan yayi dade da sunan gari ko Wabi'unki to akasi ne=?L?


Sabon salo kuma sabuwar tafiya mai karatu wannan yayi daban da sauran, tafiyar ta musamman ce kedai kasance dani ?ar'uwa.

_Bismillahir rahamanir rahim

Page 1

Tafiya yake cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, sosai yanayin garin ya ke masa daWi sabida iskar da take kaWawa ta ko ina, ?ara rage gudun sa ya yi dai'dai lokacin da ya kunna wakar Decot? a cikin motar, musamman daya kasance shi ne mawa?in da ya fi so a cikin mawa?an hausa na garin Agadez.


?aran kiran wayar sa da aka yi ne yasa gabaki Waya ya rage volume din wakar, daga gefen titi kaWan yayi parking lokacin da yake Waukan kiran.


''Man fatan kana lafiya?'' ce war Engineer Abdallah Abdul-?adir Ousmane.

''Ina lafiya! Wai kana ina ne? Nazo gida Ummi take faWa mini ka fita zuwa wani aike da Abby yayi maka'' Yusuf ya amsa shi ta Wayan Sangaren.


''Ok da magana a bakin ka kenan?'' Outhman ya tambaye shi.

''Wallahi kuwa! Yanzun kana dai'dai ina ne in tarda kai?'' Yusuf yayi tambayar cikin za?uwa da san jin inda Abokin nasa yake.

Ba Sata lokaci yayi masa kotan cen wajan da zai same sa, cikin mintuna goma sha biyar sai gashi ya iso.

?an acaSan daya kawo sa ya biya kafin ya nufi inda ya hango motar Ousmane din.


Yana ?o?arin tayar da motar yace da Yusuf ''Ina jinka miye labari?'' daidai nan ya koma saman titi ya ci_gaba da tafiya.


Ajiyar zuciya Yusuf ya yi kafin yace ''wallahi Aboki ina cikin damuwa, Wazu ina shago Baba ya kirani gida haka na rufe shagon na tafi, hum kasan mi yake ce mini kuwa?'' yayi maganar kamar zai yi kuka.

Sai da Ousmane ya guntse dariyar data zo masa ganin yanayin abokin nasa kafin ya ce ''a'a bansani ba sai ka faWa yaron Mama''.

Buris ya yi kamar bai ji sha?iyancin da Ousmane din ya ke masa ba ya ce ''wai ina zuwa Baba ce wa ya yi ya gaji da bani damar da yake akan na fitar da matar aure amma naki, yanzun haka ya yanke hukuncin zai auro mini mata a can garin mu, kuma ni wallahi bana so ko kaWan hakan yana nufin auren dole fa kenan, kuma ma da ?ar kauye ?auyen ma na Matamay, kai gaskiya da sake''.


Sauke glass din Motar Ousmane ya yi ya tofar da yawu yace ''wani sunan garin idan kaji kamar kayi amai wallahi'', Wan harararsa Yusuf ya yi ya ce ''Bana san iskanci da wulakanci fa, sunan garin namu ne ya ke shirin saka ka amai?''.


Kashe masa ido Waya Ousmane ya yi ya ce ''Allah sunan garin naku ne sai a hankali, wai Matamay'' ya ?arasa da dariya a karshen maganar, dan shi harga Allah sunan garin dariya ma yake basa.


''Eh kayi dariyar ka mana ai kwara sunan namu garin da wani, dan ko ni wuya nake ji idan naji ana faWar cewa munada ma?obtaka da su, sam sunan garin da kuma mutanen cikin sa ba suyi mini ba''.


Abdallah yace ''tofa! kaji ka da wani zance ina ruwan ka da sunan garin mutane, ai kawai ka amince muje mu sha shagalin mu, ina mai tabbatar maka ninan zan je dauko Amarya Malam''.

''Allah kuwa na lura yanzu ka daina damuwa da lamari na, maganar aure fa ake yi auren ma na dole'' cikin damuwa Yusuf yake maganar.


?iiiiii yaja burki dai'dai isowar su wajan, babban fili ne a baya kaWan da cikin gari, filin za'a iya kiransa da ae koki dan babban waje ne da faWin iyakar sa sai an auna da ma'auni, ba'a jima da Gwamnatin jaha ta fitar da sanarwar ana neman mai siya, shine Alhaji Muhammad Ousmane wato (Abby) ya siye shi bisa shawarar ?an'uwansa, Yayansa kuma Aminin sa wato Abdul-?adir Ousmane dan su anfana, lokacin Abdallah baya ?asar yaje ?asar Algeriya ziyara, duka baifi kwanaki uku da dawowar sa ba, shine Abby'n yace yazo ya duba wajan dan asan mi ya kamata ayi dashi a matsayin sa na Engineern ?ere-?ere.


Sosai suke kallon wajan! Iya hangen ka ba zaka iya gane daidai ?arshen wajan sa ba ''ikon Allah dama wannan shine wajan da Abby yake magana'' cewar Ousmane da kyenkyemin wajan ya gama kamashi, ga waje har waje sai dai kuma jama'ar gari sun gama mai da shi bola, ta ko'ina shara ce a wajan lodi-lodi, wannan shine dalilin daya sa Mahukunta suka sayar dashi, anyi ta saka dokar hana zubar da shara amma mutane sun kasa dai nawa.


Sai yanzu ne Yusuf ya gane ma?asudin zuwan su wajan jin Abdallah ya ambaci wajen da kuma sunan Abby, duba agogon hannun sa yayi kafin yace ''Ya kamata muyi abunda ya kawo mu mu bar wajan nan kaga Magarib na sayo kai'' .


Ganin kamar nazarin wajan zai bashi wuya kai tsaye sai ya ciro wayar sa ya fara Waukan video, a dubarar sa idan ya je gida sai ya yi nazarin a tsanake.
Tafiya suke yana videon wajan haka sukayi ta zagayawa.


''Talatuwa! Talatuwa'' sukaji sautin murya kamar daga sama, ba Yusuf ba hatta gogan sai da yaji tsoro ya kama shi ganin rana tana shirin faWawa ga gari ya fara dubu, basu tsure da lamarin ba sai da suka ji an kuma cewa ''Talatu yi sauri kigani wallahi nayi tsuntuwa Allah ya bani'', da sauri su ka juya inda suke jin kamar daganan sautin muryar yake fitowa.


''Suba hanah'' shine abinda Abdallah ya faWa ganin wata ba?ar yarinya a tsakiyar bola tana rurin azo aga ta yi tsuntuwa, gyara tsayuwarsa yayi dan ganin ta ina wacce ake kiran zata Sullo, har yanzu yana Waukan videon sa bai daina ba.


Da hannu Yusuf yake masa nuni ta Wayan Sangaren, ganin wata yarinyar na tunkaro inda waccan din take, ko a ganin ido ma waccen tafi wannan kyan gani, kayan jikin ta kaWai ya isa kayi tunanin ko dai mahaukaciya ce, wannan shi Abdallah ya saka a ransa, kai tsaye kuma ya bawa kansa amsa da a'a ba lallai mahaukaciya bace.


Lulawar da sukayi cikin duniyar tunani ya sa basu ankara ba har yaran suka bar wajan, babu inda basu duba ba amma babu su, sosai hankalin Abdallah ya tashi, da hanzari suka koma cikin motar su suka nufi hanyar komawa gida.


A wannan karon Yusuf ne yake tu?in, kasantuwar sa aboki ga Abdallah Abdul?adir Ousmane ya iya mota, ba laifi abota da Abdallah tayi masa rana, tun suna primary suke tare duk da ba makarantar su Waya ba, shi Ousmane yana privete school ne shi kuma Yusuf gwamnan school, amma haka suke haWuwa dazaran an tashe su suyi ta wasa, har iyayen su sai da zumuncinsu ya shafesu, to Yusuf babu raban zai ci gaba da karatu sanadiyyar wata jinya da ya yi na tsawon shekara biyu baije makaranta ba, to daya warke sai yace kawai ya ha?ura, sai aka sama masa shagon dinki ya fara zuwa koyo, dayake yana da zuciya cikin shakera Waya da rabi aka yaye shi, sai Abby ya buWa masa ?aton shago aka cika masa shi da kekunan dinki kala da kala, a gefe kuma aka saka masa kayan magamin dinki irin su zare kyelkyeli, da dai sauransu.


Har suka iso gida Abdallah bai dawo daidai ba, shifa duka tunanin sa da aljannu suka haWu, dan kamannin su da kuma kayan dake jikin su duk bana cikakkun mutane bane.


Fuskantar da Yusuf yayi kamar abokin nasa baya cikin nutsuwarsa ne yace ''Karka damu aboki na! Dan baka cika zama a gari bane shi yasa da kayi ta ganin irin wannan mutanen, sai yanzu ma suka fado mini a rai wallahi, suma Mutane ne kamar kowa sai dai ba kamar kowa ba, a binda yasa na ce haka shine suna wata iriyar rayuwa kamar ba mutane ba, sune jama'ar dayan garin da yake ma?obtaka da tushe na, idan kaji ana cewa (?AN KANCE) to sune, sam basa kyautawa rayuwar su bare har wani yayi tunanin kyautata musu.


''?AN KANCE'' Ousmane ya maimaita, kenan ita ma wannan yarinyar daya gani ?AR KANCE ce? Yayi tambaya a bayyane.


''Kwarai kuwa su duka sunan su kenan ?AN KANCE'' cewar Yusuf cike da jaddadawa.


Shigowar su gidan yayi daidai da fara kiran sallar magariba da aka fara yi a masallacin ?ofar gidan su Abdallah din, fita suka yi daga motar suka nufi Sangaren Abdallah dan yin al'wala.


Bayan an gama sallah Yusuf ya wuce shagon sa, yana da al?awari da wata mata za tazo karSar Winkinta bayan sallar magariba, to kar tazo baya nan shi kuma bazai so hakan ba, mutun ne shi mai girmama alkawari dan yasan ladar dake cikin girmama shi, da kuka rashin nasarar dake cikin saSa al?awari.


A sanyaye a shiga babban falon gidan bayan ya dawo daga masallaci, Abby ne a zaune a kujerar zaman mutun biyu da tsarbi a hannunsa, babban mutum dan kimanin shekara arba'in da takwas aduniya, fari dan asalin kabilar jajjayan buzaye, sudin ?an asalin ?asar Algeriya ne amma iyaye da kakannin su duka a nan Agadez aka haifesu, Alhaji Muhammadu Ousmane kenan, da alamu shima shigowar sa kenan daga masallacin, dayake shi Abdallah baya cikin hayyacin sa shi yasa bai lura da Abbyn nasa ba sai bayan daya shigo yanzu.


Kusa da ?afafuwanshi ya isa ya zauna, hannu Abby ya dora akan sumar kan yaron nasa yana shafawa, sosai ya lura yana cikin damuwa tun a masallaci, cikin muryar sa ta cikkakun wayayun da ilimi ya gama ratsa su yace ''Yarona miya faru ne?'', Wora kansa bisa gwiwar Abby'n nasa Abdallah yayi cike da damuwa yace ''Abby dama a wannan garin akwai wasu waisu ?an Kance?'' ya tambayi Abby dan shi sam bashi da rufi ko Soye abinda ke ransa ko kaWan.


''Eh tabbas akwai su kamar su fasa garin nan My Son, sai ma idan kaje wajan sabgar biki ko suna kaga yadda suke fama akan abinci, zaka rantse da Ubangiji cewa basu taba cin wani abu wai shi abinci ba'' kafin Abby ya yi magana Ummi dake isowa falon da Wan ?aramin tiren data haWo kan kayan shayi a hannun ta ta bashi amsa.


Da sauri Abdallah ya tareta ya amshe tiran dake hannun ta, ajiyewa ya yi kafin ya kalleta ya ce ''Ummi na bani labari'' cikin shagwaSar daya saba yi musu yayi maganar.
.
Cike da kulawa Ummi ta kama hannun sa ta zaunar dashi a kujerar ta ce ''Abdallah na akwai rigima, yau kuma miya haWaka da Yan Kance har kake so a baka labari akan su?''.
''Haka kawai Ummi na'' ya samu kansa da rufe musu abu a karo na farko.


''Wayyo Allah kaina! zaku Wora mana shayin nan ne ko sai kaina ya tsage tsabar ciwo'' cewar Abby da kansa ke masa mugun ciwon rashin shan shayi da bai yi da wuri ba .

Da gudu Abdallah ya dawo kusa dashi yana faWin sorry Abby yi ha?uri yanzu za'a dora, maybe yau aiki yayi wa Ummi na yawa shi isa bata Wora da wuri ba.


?an rishon da suke dora sha'yin akai Ummi ta shigo dashi, ba Sata lokaci Abdallah ya kama mata suka dai'daita komai, ta dora ?ar ?aramar butar sha'yin akan rishon Win, kafin kace mai tuni falon ya gauraye da ?anshin kayan hadin da Ummi take ?awata sha'yin ta dasu a kullum, tabbas sun gaji shan shayi tun kakanni da Iyaye, amma a kullum Abby faWa yake cewa Ummi tafi ko iya shayi, duk inda yaje ba?unta aka bashi shayi sai yaji kamar ruwan ganye da suga aka bashi.


Kusa dashi suka koma su duka, Ummi ta ran?wofo daga Sangaren dama shi kuma Abdallah ta Sangaren hagu, Ummi tace ''DR Muhammad nawa ayi ha?uri yanzu shayi zai dahu'' ?ar hararar wasa Abby ya yi mata kafin ya kauda kansa daga gare ta ya kalli sashen da Abdallah yake ya ce ''Yarona Ummin ka ta daina kula dani, ka faWa mata har yanzu inada yarintar dazan iya cike guda ukun da suka mini saura eh'' Abby ya faWa kamar gaske.


Basu ankara ba sai ganin Ummy suka yi a tsugunne a gabansa ta Wora kanta saman tsinyar sa, cikin karyayyiyar muryata ce ''Abbyn Abdallah yanzu saboda na makara ban dora shayi ba kake so ka fasa mini zuciya, ka duba kagani'' ta Wago da kanta tana nuna masa saitin kirjinta da take ji kamar zai rabe gida biyu.


Dariyar Abdallah ce ta Wauki hankalin su, sai da ya yi mai isar sa ya ce ''Haba dai Ummy na ai kisha kurumin ki daga kesai kiWan tashi, Abby na shida aure haka suka yi'' ya karasa maganar da buWe hannayan sa biyugefe da gefe.


Filon dake ajiye a gefe Abby ya Wauka ya cilla wa Abdallah tare da ya ce ''Ba bakinka ba dan ?aniyar ka, kwanan nan zakuji nayi sabon aure abina'', da gudu Abdallah ya fice daga falon yana dariya ya nufi dakin sa dan yayi wanka kafin lokacin sallar isha'i...........


Page 2

Yana fita Ummy ta faWa jikin Abby ta saka masa kukan shagwaSa, sosai take bawa Abby mamaki ita har yanzu ta kasa girma, ta yi masa kuka ba wani abu bane, zame liffayar(sari) dake kanta ya yi ya shafi kantaccan gashin kanta baki wulik ya ce ''haba Gaisha na ke baki san wasa bane, Muhammad naki ne kekaWai har ?arshen rayuwa kinji ko, ke ta daban ce matar Dr, Allah yayi miki albarka ya albarkaci zuri'a, sosai suka shagala da zayyanowa junansu kalamai na kyautatawa a haka har aka kira sallahr isha'?, da kyar da dubara Abby ya cire Ummy daga jikinsa gudun karya rasa jam'in sallah, saida yaje ya kuma Wauro wata alwalar dan waccen kam ta tafi garinsu, kafin ya wuce zuwa masallaci inda acan suka haWu da Abdallah.

Itama Ummy nata Wakinta wuce tajkintsa kafin ta gabatar da tata sallahr.


Kafin su dawo daga masallaci tuni Ummi ta jera kayan abinci a falon, da yake Abby baya san cikin abinci a daining table yasa suke cin abinci a ?asa, Alfatat da miyar kayan ciki ne Ummi tayi musu dan tasan Abby yanada san kalar abincin sosai.

(Alfatat) wani kalar abinci ne da ake yinsa da fulawa da kuma garin semovita, kamar yadda zaka yi wainar fulawa haka a ke yinsa, sai daishima yanada da tasa tukunyar ta musamman da ake yinsa da ita, wani zakaga ya fita kamar cercule, wani kuma zai fita yanayi da heart, ya danganta da irin ?irar tukunyar ma'abocin yinsa, sai kuma kayi masa kalar miyar da kake so amma anfi yinsa da miyar nama.


Duk cewar da Abby yake kansa na masa ciwo akan bai sha shayi da wuri ba, sai yanzu bayan ya gama cikin abinci sanan yasha, Abdullah ya tattare komai yakai kicthing, saida ya nusar da masu aiki da a kwai aiki a kicthing ta hanyar danna ?ar karraurawar da take nusar dasu kafin ya wuce.


Tani mai aiki tanajin karan tasan sun gama cin abinci na yau saura na gobe idan Allah ya kaimu, ta kuwa biyo ta ?ofar baya ta shiga kicthing Win dan yin wanke wanke.


Koda ya dawo falon zama ya yi kusa da Abby yana hamma alamar bacci kuma yake ji tunda ya bawa ciki hakkin sa.


Abby ya ce ''yarona wai an baka labarin daka tambaya Wazu ko a'a?'', sai yanzu ya tuno da maganar yace ''Yawwa Abby ba wannan ba! Naje naga wajan da kuka ce naje na duba, masha Allah wajan yanada girma sosai amma saidai bayada kyawun gani wallahi'' kamar yaga wani kashi a gabansa haka ya ke maganar .


''To sarkin tsantsani yanzu zakace wajan bai yi ba ko?'' Ummy ta magantu tun kafin Abby yayi magana.

Sashen da take ya kalla yana karkada ?afarsa daya mike a kasan carpet ya ce '' Allah kuwa Ummyna bakiga wajan bane da sai kin tausaya mini, waje duk shara, a haka kuma naga wasu......sai kuma yayi shuru jin wayar Abby ta Wauki ruri.


Daga jin ringing din wayar suka iya gane ma'anocin yin kiran.

Wani yalwataccen murmushi ne ya bayyana akan fuskar Abby jin Wan'uwa rabin jikinsa yana kiran daya gama zame musu wajibi farillah kullum a daidai wannan lokaci.

Ummy ce ta basa wayar ganin tafi kusa da ita, da sallama a bakinsa ya Waga kiran.

''Wa'alaikum salam warahamatullahi wabarakatuhu ya Akhy'' Alhaji Abdul?adir Outhman ya amsa shi ta Wayan bangaren, sosai suka gaisa tare da tanbayar iyalan su na kowane bangare kafin Abby ya gyara zama yace ''Yaya ya wajan sauke jiragen nan fatan komai ya daidaita?'', ''Eh to gaskiya ba wani sauyi Wan'uwa wallahi hanya ta ri?esu gaba Waya, kasan wannan ?ar hatsaniyar da aka samu tsakanin Libonon da Algeriya Win nan ya sa aka rufe ko wace iyakar ?asar nan ta hanyar jirgin sama jirgin kasa, kai hatta motar safara a safiyar yau an dakatar da sifirin ta har sai anga abinda hali yayi, gashi gwamnati tayi tsokaci akan yawan ba?in haure sunyi yawa a ?asar nan, sunyi kira da babbar murya akan nanda kwanaki shida masu zuwa ko wace kasa ta aika a kwaso mata ya'yanta nacan dan cinkosan bakin hauren yayi musu yawa, zakasha mamaki a kaso biyar na mutanen kashi biyu duk ?an Nijar ne abun yana mini ciwo sosai wallahi'' Dady abdul?adir ya faWa.

Cike da kunar rai Abby ya ce ''wallahi Yaya a kullum idan na tuna irin rayuwar nan ta barin muhalli da mutanen ?asa ta suke yi zuwa wata ?asar sai naji kamar na amshi tayin shiga harakar siyasar nan da mafiya yawon jama'ar dake zagaye dani suke mini, wane arziki ne zaka samu a ?asar wasu wanda ba zaka iya neman sa a taka ?asar ba, ka duba fa kaga wai har mata suke zuwa Libya da Algeriya wai da sunan neman ?idi, musamman Yan Kance din nan saidai Allah ya gyara, sosai ya kamata asamu canji zuwa yanzu''.


Sai yanzu da Abby ya anbaci sunan ?an Kance ya tuna da wayan'nan yaran da suka gani a wannan filin Wazu,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login