Showing 48001 words to 51000 words out of 86085 words
Chapter 17 - FEERYAL Part 3 Complete Hausa Novels by Rasheeda S Director.txt
akayi.
Aunty ko hankalin ta ya kasa kwanciya ta kira Daddy ta sanar masa.
Abdulrami bai d'au minti 20 ba ya iso asibitin.
da karfi ya turo kofar room d'in yana ware idanunsa akan gadon.
Feeryal na kwance tun da ake maganar bata furta ko kalma d'aya ba.
da sauri Ajmaal ya ce
"Ya Abdulrahim nayi ta kiran wayar Mommy bata d'auka."
da karfi ya juya ya fita Ajmaal yabi bayan sa........!
Cikin hanzari ya shige mota, Ajmaal ya bud'e d'aya gefen ya shiga yana cigaba da kiran Mommy da har yanzu bata d'aga ba.
da karfi ya fige motar da mugun gudu, suka haura titi.
da sauri Ajmaal ya kunna computer motar yasoma tracker ya shiga lalub'o ta in da Mommy take.
da sauri ya d'ago yana nuna computer yana cewa
"Ya Abdulrahim kilomita 15 ta hanyar titi ta baya kilomita 10 tazaran mu da su, sun doshi Cea, sun sauka a titi suna bin hanyar kasa a lamu ya nuna ta baya zasu bi,
idan mukabi hanyar titi yafi garanti sai dai za'ayi jinkirin isa, ta baya hanyar ba kyau bazai yuwu ayi gudu ta hanyar ba."
kafin Ajmaal ya rufa baki ya juya sitiyarin motar yabi ta hanyar da yake gaya masa babu kyau, yaja sit belt ya d'aura.
Ajmaal ya kwalalo ido yana kallon yadda ya figi motar kamar zai watsar da su, ba shiri ya ja sit belt shima ya d'aura, yana gyara zaman sa idanunsa akan d'an'uwan nasa ganin yadda jijiyoyin hannun sa suka firfito damatsan sa suna bud'awa, yayin da fuskarsa ta juye ta rikid'e izuwa na tsananin b'acin rai, idanunsa sukayi jajir.
gudu yake baya sanin inda yake saka tayun motar tasa.
Ajmaal idanunsa akan computer yana gaya masa adadin sauran lokacin da ya rage su cim musu, da ta inda zaibi.
kiran Daddy ya shigo wayar Ajmaal, Ajmaal ya bashi adireshin in da su Mommy suke.
yana kashe wayar
da sauri Ajmaal ya d'ago yana cewa
"Ya Abdulrahim sun tsaya a kusa da gab'ar Cea!
muna daf da cimmusu."
kure gudun motar yayi wanda duk tsananin gudun da yake, ganin nawar gudun yake, da karfi ya naushi sitiyarin motar badun ingantacciyar mota ce mai tsadar gaske ba, da tuni ya tarwatse sitiyarin nasa.
sai da Ajmaal ya razana..
Mommy tafito daga ciki motar da sauri rike da yaran a hannunta.
da sauri ta nufi bakin gab'ar ruwan tana fad'in
"Zo ku koma in da kuka fito, bazaku zauna cikin jinsin mutane kuna aljanu ba, ku ko ma can in da kuka fito."
da sauri direban ta ya fito ganin abun da take shirin aikatawa ya biyo ta yana cewa
"Hajiya dan Allah kiyi hakuri kar ki aiwatar da abun da kike shirin aikatawa."
tsawa ta buga masa ta ce
"Ka tsaya a matsayin ka na direba, kada ka sake ka shiga lamarin cikin gida."
ai ko ya ja ya tsaya ya nad'e hannu jiki na rawa cike da d'inbin fargabar abun da take shirin aikatawa.
ta dad'a matsowa bakin gab'ar.
ta d'aga d'aya ta na kokarin wurgashi a ruwan, dai-dai san da motar Abdulrahim ya sharo kwana in da suke iya hango tekun.
wani irin wawan burki ya taka dai-dai sanda ta jefa d'aya yaron cikin kogin.
direbanta ya d'aura hannu a kai yana salati.
da karfi ya b'alle murfin motar ya duro kasa batare da ya kashe motar ba.
a hargitse Ajmaal ya zare sit belt d'in jikinsa ya yi azaman ruko sitiyarin ganin motar tana kokarin gangarawa cikin ruwan.
yayi kwana da ita ya kashe motar.
wani irin gudu Abdulrahim yake cike da zafin nama yake taka kasa, cikin wani irin murya mai nuni da tsantsar tafasar zuciya gami da amon sauti, mai fita da karaji,
ya ke fad'in
"No! Mommy kada kiyi haka!."
yana daf da isowa inda take tayi saurin dad'a masowa bakin ruwan, ta d'aga zata kuma jefa d'ayan.
ya mika hannu yana fad'in
"Aa Mommy a'aaaaaa!."
bai rufa baki ba kaji bundun, ta jefa shi yaron ya calla kara.
yana wutsil-wutsil kamar yadda d'anuwan sa yayi kafin ya nitse a daina ganin sa.
da gudu ya wuce ta zai yi tsalle ya dira cikin ruwan.
Ajmaal da direban ta sukayi hanzarin ruko shi ta baya.
Ajmaal da tuni hawaye yashiga wanke fuskarsa ya ce fad'in
"Aa Ya Abdulrahim kada ka shi ga."
"Yellab'oi ruwannan da zurfi sosai tanan gefen kada ka shiga."
da jarfi ya fizge yakuma yunkurin shiga suka juyo muryar Daddy a bayan su
"Ka dakata Abdulrahim!."
Daddy ya yi maganar cikin d'aga murya.
wani irin durkushewa yayi da gwuiwowin sa a bakin gab'ar tare da cusa hannanyen sa cikin gashin kansa da karfi ya yi wani irin ihu mai kara gami da karajin gaske,
yana yamutsa gashin yana wani irin huci tamkar namijin zakin daya kwana baiciba.
Daddy ya nufo su da sauri mai kama da gudu, in da direban sa shima ya rufa masa baya.
Ajmaal ya juyo yana hawaye murya na rawa yake fad'in
"Daddy Mommy ta kashe su ta jefa su a ruwa, ta kashe su Daddy!."
ya fashe da kuka kamar karamin yaro.
Daddy ya karaso ya dafa kafad'ar Abdulrahim dake durkushe yana bubbugawa, yayin da idanunsa ke kan ruwan da babu alamun yaran a ciki.
idanun Daddy suka kawo kwalla sai ga Daddy na hawaye da idanunsa.
kan kace me aka nimi Mommy a gurin aka rasa, ta zame ta shiga mota tasa direba ya juya da ita gida.
tana ji a ranta ta raba su da fitinar aljanu.
Nan da nan Daddy yasa aka kirawo masana ruwa, aka shiga jirgi akayi ta yawo cikin ruwan ana nima,
amma ko gawarsu ba'a samu ba, daga karshe aka samo abun d'aukar d'aya jaririn.
ma'aikatan suka bawa Daddy tabbacin gawarsu baya kusa, ruwa ya tafi da su amma zasu tura sanarwa a tare su acan rariya idan suka isa can za'a neme su.
Jiki ba kwari Daddy ya juya gurun Abdulrahim, ya ruko hannun sa da tun d'azu ya masa ya zauna gefe kan wani dutse ya sunkuyar da kai kasa.
Ajmaal da tun d'azu ya kasa tsayuwa guri guda ya zo gon d'an'uwan nasa ya koma bakin ruwan yana lekawa ko za'a ciro yaran.
ya taho da sauri sanda Daddy yake mikar da shi tsaye.
tausayin d'anu'wan nasa ya kuma baibaye shi.
idanunsa sunyi jajir jijiyoyin jikinsa sun mike rad'a-rad'a,
zufa yana gangarowa daga cikin sumar kansa zuwa fuskarsa.
Daddy ya dubi d'an nasa da d'inbin tausayawa dan yasan yakai makura a b'acin rai ko bai furta ba, basai ya furta ba yasan wannan halin nasa tun yana d'an karami,
idan yana cikin b'acin rai haka zufa zatayi ta karyo masa daga cikin sumar kansa yana gangara fuskarsa, jijiyoyin jikinsa zasu mike rad'a-rad'a.
sai dai na yau yafi na duk sauran lokutan dan kuwa yau karkashin jajayen idanunsa sai da sukayi damshi alamun ruwa nason fita daga cikin su.
Daddy ya damke hannunsa da kyau ya dube shi yana fad'in
"Ka yarda da Allah kayi imani da kaddara mai kyau ko mara kyau, muje gida Abdulrahim."
ya janyo hannunsa motar Daddy suka shiga shi da Daddy gidan baya,
direba ya ja su.
Ajmaal ya shiga motarsa da suka zo da shi yabi bayan su suka nufo gida.
Su Shamsuddin da Faisal da suka d'auko hanyar zuwa, bayan sunyi waya da Ajmaal ya sanar musu abun da ke faruwa, kafin su fito suka sanar a gidan, tuni gidan ya d'auki labarin.
suna hanya suka kuma kiransa ya yi musu kwatance, ya ce su juya gida gasunan suma dawowa.
Wani irin gud'a Umma Karima ta rangad'aga, tayi tsalle ta tafa hannaye, tamkar anyi mata albishir da aljanna.
"Hajiya Halima kinyi abun da ya dace, da baki farka ba da ni zan mike dan ni bana bacci."
Bilkisu data kawo mata labarin ta ce
"Umma wai murna kike wlh ni jikina yayi sanyi, ko da bani son Feeryal amma 'ya'yan nan na Ya Abdulrahim ne shi kuma yayan mu ne,
ai bazai so ace yau ayi masa haihuwa a yau d'in kuma yana ji yana gani akashe masa yara ba,
gaskiya Mommy bata kyauta ba, kashe rai ai musifa ce, ranma na jarirai wanda yau aka haifesu basu d'auki hakkin kowa ba haba dan Allah."
Bilkisu tayi waje tana Kuma fad'in rashin kyautawar Mommy.
Tun da suka hau hanya Daddy ke bubbuga bayan hannunsa da hannun nasa ke rike a hannun Daddy alamun rarrashi, duk da shima yana jin kuna da b'acin ran a tare da shi.
har suka karaso gida.
suka sauko a motar ya zame jiki ya wuce side d'in sa.
Daddy ya nufi sashin Mommy rai b'ace, a tsaye ya tadda ita a parlour Mommy tana ganin sa ta b'ata rai.
tana fad'in
"Haka kawai a dukeka a hanaka kuka, a wani dalili aljanu suje can su karata."
bata yi aune ba yana karasowa ya wanke mata mari cikin kakkausar murya ya ce
"Allah wadai da hali irin naki Halima wlh nayi nadamar kasancewar ki a matsayin uwar 'ya'yana,
kije na sake ki, kuma bazan kyale ki ba sai nayi shari'a da ke akan jikoki na da kika kashe!."
muryar Hajiya suka jiyo a bayan su tana fad'in
"Mai da ita yanzu nan maza ka mai da ita, in dai ina numfashi baka isa ka saki Halima ba, 'yar uwar taka ko me tayi maka banyar da ka sake ta ba,
yara kuma sunzo kan lokaci ne dama ba masu rayuwa bane su, ka mai da ita na ce ko ka biyani nono na!."
Hajiya ta karaso tana kuma fad'in
"Ka mai da ita nace."
Daddy ya ce "Amma Hajiya."
da sauri Hajiya ta tari numfashin sa
"Ka mai da ita na ce, duk shari'ar da zakayi da ita kuyi tana d'akin ta."
Daddy ya ciza yatsa tare da fad'in
"Na mai da ke amma kar ki sake kizo in da nake."
ya juya yafita cikin matukar b'acin rai.
Mommy dake dafe da kuncinta da alamun jikinta ya yi sanyi.
Hajiya ta dube ta ta ce
"Yanzu ke Halima bakiji ko d'ar ba, da har zaki iya kashe kikokinki da hannunki?
yau ko bare ai bazata aikata hakan ba,
bare ke da kike jinin Abubakar,
ai 'yar nunel ta nuna basai an fad'a ba, da ka kalli yarannan kallo d'aya kaga Abokin turawa,
ko makaho ya shafa yasan 'ya'yan nan na abokin turawa ne,
yo zance ya kare tun da har yabi dare yaje ya had'a shinfid'a da ita,
ai dole mu karb'i 'ya'yan nan, bare ga babban shaida da sukayi kama da uban su,
wannan ai niman jawa mutane magana ne."
Hajiya tayi waje tana bombomi.
Mommy ta zauna kan kujera jiki a sanyaye.
Daddy na fita asibiti ya tafi.
Aunty na tsaye a kan kafafunta hankalin ta a matukar tashe.
tun da tayi waya da shi ta sanar masa, Mommy ta d'auki yaran daga baya tana ta kiransa baya d'aga wayar.
tayi ta kiran Ajmaal shima haka.
Sumayya da Miemie hankalinsu ya kasa kwanciya suka nufo gida,
kasancewar babu motar gida dole taxi suka bi, suka b'ata lokaci a hanya.
Feeryal na kwance tayi shiru, Aunty na tsaye da kafafunta.
Daddy ya turo kofar da sallama,
kallo d'aya Aunty ta masa gaban kirjinta ya yanke ya fad'i.
tafi kowa sanin halin mijinta,
kallo d'aya take masa ta karanci farinciki ko bakinciki ke tare da shi.
da sauri Aunty ta nufo shi tun kafin ya karaso, ta ruko hannayen sa hankali a bala'in tashe take fad'in
"Daddy ina yaran suke ina ta kaisu?."
Daddy ya rumtse idanunsa yana jin zafi cikin zuciyarsa.
Aunty ta kuma jijjiga shi murya na rawa ta ce
"Daddy kayi magana, dan Allah ina ta kai su, dan Allah a dawo mana da su, ko nono basu shaba, a kawo mana su ta basu nono kar yunwa ya dame su."
Daddy ya kifa kansa a jikin kafad'arta.
duk yadda yaso ya daure ya gagara, sai kawai ya rushe da kuka mai cike da kuna da matukar tausayin su.
sai kawai itama ta fashe da kukan da tun d'azu take ta danne shi.
Daddy yayi saurin d'ago kansa a kafad'ar ta ya rungumeta.
yana bubbuga bayanta tare da fad'in
"Kiyi hakuri Fad'imatu nayi duk iya yina yau na gaza."
Aunty ta d'ago da sauri ta ce
"Daddy me kake so ka ce."
"Nagaza taimakon jikoki na Halima ta jefa su a ruwa ta kashesu."
ya yi saurin sakin Aunty ya jingina da jikin garu ya dafe kirjinsa yana tari, da sauke numfashi da sauri-sauri.
wani irin rumtse ido Feeryal tayi, jin kanta ya yi wani irin sarawa.
wasu siraran hawaye suka gangaro gefen idanunta.
Aunty da gaba d'aya ta firgice ta d'aura hannu a ka tana salati da fad'in
"Me sukayi miki Hajiya Halima idan ku bakwason su, kun wadata da 'ya'ya mu bamu samu ba, yanzu ke nan Allah ya bamu, mu muna son su."
gaba d'aya ta daburce cikin d'akin tana ta kaikawo da sambatu gwanin ban tausayi.
Daddy na dafe da kirjinsa ya mika d'aya hannunsa ya kamo nata sannan ya furta
"Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un."
ai ko da sauri ta cab'e kalmar da furtashi ya samar mata da nutsuwar da har ta juya ga Feeryal dan son ganin halin da take ciki.
ta karaso bakin gadon da sauri ganin hawaye na gangara a fuskarta, ta shafa kanta tana cewa
"Kiyi hakuri, ita wannan kalmar bayan an cutar da kai ake gaya maka ita, idan kayi hakurin kuma zakaga ribar yin ta Allah yana bayan gaskiya."
Feeryal ta bud'e idanunta a hankali, idanunta ya sauka kan inda Daddy yake,
ta d'aga hannu ta nuna inda yake tana cewa
"Ammie Daddy."
da sauri Aunty ta juya numfashin sa na dad'a sama-sama idanunsa yana yin sama-sama.
da sauri Aunty tayi gurin sa ta rike shi tana kwad'awa likita da nurse's kira.
a guje suka shigo jin irin kiran bana kwanciyar hankali bane.
Aunty ta ce "Ku taimake ni ciwonsa ya tashi."
a ka kwashesa akayi da shi wani room d'in.
ranar Aunty taga tashin hankali mara misaltuwa.
ana shiga da shi Ajmaal na isowa, shi ya zauna a gunshi ita kuma ta komo gun Feeryal.
tana kaiwa da kawowa sakanin room d'in da Feeryal take da na Daddy......!
Cikin dare Daddy ya dawo hayyacin sa.
washegari da safe ya bukaci a sallame sa ya
koma gida.
Bappa Salihu da asuban fari ya baro Yelwan Shendam ya shigo garin Jos.
yabi jirjin da ya taso daga Jos ya sauka a airport na Lagos da karfe 9 dai-dai, na safiya.
bai fad'awa kowa zai taso ba shiyasa mota bata je domin tarar sa ba,
taxi ya shiga ya taho AA FIYA STREET.
yana isa ya buga get security suka leko ganin shine sukayi hanzarin bud'e masa karamar kofa ya shiga, suna yi masa sannu da zuwa.
sama-sama ya amsa musu ya shige ciki.
da su Nabila da Sahala da Ameerah suka fara cinkaro sun fito daga sashin Daddy.
shiko kai tsaye sashin Mommy ya wuce.
Ameerah tayi gudu taje ta gayawa Hajiya ga Bappa Salihu ya zo.
tun daga bakin kofar side d'in Mommy Bappa Salihu yake kwad'a mata kira har ya shigo parlour'n ta yana fad'in
"Ina kike mutumiyar banza shashasha wacce ta girma har yau batasan ciwon kanta ba."
Mommy ta fito daga cikin bedroom nata jiki na rawa
Bappa Salihu ya nufo ta ya na cigaba da fad'in
"Halima ke d'in nan da a asibiti aka haife ki da wlh cewa zanyi an canza min 'ya aka bani wacce zata kashe ni,
ban haifi 'yar da zata zo ta zame min fitina cikin ahali ba, gara tun marmaza na cire ki cikin 'ya'ya na tun kafin ki hallaka min ahali,
mutumiyar banza ni ban haifi makashiya ba!."
Bappa Salihu ya rufe ta da duka da hannu bibbiyu yana cigaba da fad'in
"Bani ba ke Halima kada ki sake ki d'aga ido ki kalleni a matsayin mahaifinki,
ke baki isa ki zame mana fitina cikin ahali ba, meye amfanin rayuwar ki ke baki cancanci zama uwa a gurin 'ya'yan ki ba, ke azzalumar uwace mai son kanta."
Sumayya Ameerah da Hajiya suka taho da gudu,
Ajmaal da ya shigo yanzu shima ya taho da sauri.
Hajiya ta shiga sakanin Bappa Salihu da Mommy tana cewa.
"Haba Malam Salihu mene ne haka, mata da girman ta ai ko 'ya'yan ta yanzu sun wuce duka."
Bappa Salihu ya ce
"Ai kin banza abun da ta aikata ai ko 'ya'yan nata bazasu aikata ba, wacce irin kwakwalwa ce da ita irin na dabbobi,
na cire ki a 'ya'yana Halima ke ba 'yata bace, ni ban haifi makashiya ba,
dad'in me zakiji ki kashe jikokin ki da hannun ki wace irin azzaluma ce ke,
na yafe ki Halima na yafe ki,
me ma kika zauna yi anan hukuma basuzo sun tafi da ke ba, hukuma zasu zo su d'auke ki yanzu,
bayan na nuna miki na isa da Abubakar na sashi ya sake ki,
sannan hukuma suyi gaba da ke!."
Bappa Salihu ya fita rai b'ace.
Hajiya tabi bayansa tana fad'in
"Kar ka kira mana hukuma anan, tun da abu ya faru ai shike nan, me ye na kiran hukuma."
sai da suka fito waje Bappa Salihu ya juyo rai b'ace ga Hajiya ya ce
"Ai ya kata hukumar su had'a har da ke su tatta, dan banga amfanin zaman ki a gidan nan ba,
ke Hajiya Hanne kina cikin gidannan b'arna daban-daban yana afkuwa ace har da kisan rai, meye amfanin zaman ki a tare da su, gara ma ki tattara ki koma can gida Yelwan Shendam, ki zauna babu amfanin zaman ki a nan, tare da su."
Hajiya ta mara baki tana fad'in
"Ahap ba yau aka saba min gorin na tafi ba,
idan abu Allah ya kadda zai faru ko ku mazan baku isa ku hana ba."
Bappa Salihu ya yi gaba yana cewa
"Duk hankalin ku d'aya ne da Haliman, Allah ya sawake irin wannan rayuwar."
ya wuce sashin Daddy.
Mommy ta zube kasa zuciyarta ya kariya,
tun da take da mahaifin nata bata tab'a ganin b'acin ransa irin na yau ba.
jikinta ya yi sanyi matuka.
Ajmaal da ya share kwalla yake fad'in
"Mommy meye hakan wlh baki kyauta wa Ya Abdulrahim ba, kin cutar da zuciyarsa dan kin san a zuciya yake barin ko wacce irin damuwar sa,
ba Ya Abdulrahim ba har da mu kika cutar Mommy, domin damuwar sa namu ne bazamu so ganin d'an'uwan mu cikin damuwa zuciyar mu ta sami nutsuwa ba,
muna murna da samin 'ya'ya kika hallaka mana su, Mommy kin san zafin da naji kuwa,
to ina ga shi Ya Abdulrahim mai 'ya'yan, da kuma uwar 'ya'yan,
da wacce ta raini uwar 'ya'yan,
da Daddy da ya zame mana garkuwa,
Mommy kin cutar da zuciyoyi da yawa,
kiji furucin da Bappa yake fad'a a kanki,
ina mu zamu saka rayuwar mu, ace muna tsaye mu 'ya'yan ki, mahaifinki yana kai hannu jikinki da munanan kalamai,
taya kike son mu goben mu tayi kyau, baki daidai ta sakanin ki da mahaifin mu da mahaifin ki da babban yayan mu ba,
Mommy bakiyi mana adalci ba!."
Ajmaal ya fashe da kuka yana kuma fad'in
"Mommy bakiyi mana adalci ba."
Sumayya da tuni ta fashe da kuka ta na cewa
"Ni gara ma na bar gidan nan natafi Yelwa, wlh tun da naga yarannan naji sonsu a raina, Mommy me yasa zaki