Showing 84001 words to 86085 words out of 86085 words

Chapter 29 - FEERYAL Part 3 Complete Hausa Novels by Rasheeda S Director.txt

FIYA ke nan nan."
murmushi tayi tana kwantar da kanta jikin kafad'ar sa ta ce
"Garin ya burge ni tun ban shiga cikin sa ba, lallai an tara manoma a wannan yankin."
murmushi ya yi yana shafo gefen fuskarta ya ce
"Bakiji an ce noma tushin arziki ba."
ido ta lumshe tana dad'a narkewa jikin ta ce
"Tabbas na sani."
"Kina dai ji ana fad'a me kika sani a kan noma."
ya yi maganar yana leko fuskarta
"Ai kaima baka sani ba Daddy ne yasan wannan."
"Digiri nake da shi a harkar noma, ko Daddy sai dai ya nuna min jimawa a harkar ba dai kwarewa ba,
Daddy baya so na gaje shi kamar yadda shi ya gaji mahaifinsa,
burinsa na zamo likita,
bayan na zamo kwararren likita natafi naje na karanci harkar noma har na yi digiri a fannin ba tare da ya sani ba."
baki ta bud'e ta ce
"Yanzu duk jimawar da kayi Daddy bai sani ba."
kai ya girgiza yana murmushi ya ce
"Ai baki sani ba wai ni b'oye masa nake ashe ya sani sarai,
ba'a jima da gaya min yasan me nake ciki ba, da san da na fara karatun da san da na gama har kasar da nayi karatun duk sai da ya gaya min."
dariya duk suka yi ta rungume shi tana cewa.
"Kai da kana ganin kayiwa Daddy wayo ashe kallonka kawai ya ke, har nayi niyyar muna komawa zan sanar masa."
kumatun ta ya ja ya ce
"Basai kin fad'a masa ba ya sani."
murmushi ta yi tana kuma lafewa jikinsa.
fuskarta ya leko ya ce
"Beauty kin d'au ciki fa mu koma a yaye Saddeeq da Haydar."
ido ta waro sai kuma ta mike a jikin sa da sauri tana kwab'e fuska da leka yaran da suke bacci a sit d'in baya,
ta dawo da kallon ta gare shi kamar zatayi kuka ta ce
"Sahab ciki kuma shekaran su fa 1 da wata 2 ne."
kiss ya manna mata ya ce
"Meye abin tada hankali yara da kuzarin su da kafarsu, Allah yasa biyun kika kuma d'auka, mu koma na duba mu gani."
"Ni dai wlh aa haba dan Allah duk shekara mutum yayi ta haihuwa."
"Ai kiji a ranki 12 zaki haifo min, kina haifo wad'an biyu na cikin zan kuma saka wasu biyun a cikin ki kara haifo su duk shekara."
kafa ta shiga bubbugawa tana ture shi.
ya rika dariya cike da shauki, kamar ba DOCTOR ABDULHARIM AA FIYA ba ne.

Koda suka isa taga karamci da soyyar agurin mutanen garin Yelwan Shendam, takuma ganin girman su, mutane masu karamci da son jama'a.
kwanan su biyu suka juya.
sukayi kwana d'aya a Jos suka bi jirgi suka koma legos.
a gidan sa da lokacin da ya karb'ota a hannun 'yan kidnapping ya kai ta can sukayi kwana uku, nan suka sauka.
washegari bayan sun huta, ya d'auke ta suka je asibitin sa.
yana gwadata yaga ciki wata biyu a jikinta.
daga asibiti suka nufi AA FIYA STREET.
suna tafe a mota yana rarrashi, dan kuka ta saka masa har da cewa a cire kicin.
ya ce abun da zai tab'a yuwuwa ba ke nan.
suna isa gidan ta sauka ta bar mishi yaran a gurin ta shige parlour'n Aunty da gudu.
Aunty na ganin ta tare ta da sauri.
ta saka kuka Aunty duk ta rud'e tana tambayar ta me ke faruwa.
cikin muryar kuka ta ce
"Ammie na ce ya cire cikin wai bazai cire ba."
a take Aunty ta fahimci wani cikin take da shi.
zatayi magana sai ga Abdulrahim ya shigo da yaran a hannunsa.
Aunty ta ce
"Yauwa Abdulrahim kawo su nan, aje a kawo min kayansu, ke kuma kar na sake jin maganar zubar da ciki a bakin ki,
in duk shekara zaki rika haifo 'ya'ya uku duk ki kawo mun su zan rike."
Aunty ta sab'i d'aya a baya ta d'au d'aya a hannu.
Zahra ta taho da gudu ta rungume ta tana
"Ammie nima ki goyani."
Aunty tayi dariya tana shafa kanta ta ce
"Aunty Zahra ai yanzu ke Aunty ce, ki bari anjima zan goyaki."
Abdulrahim ya yi murmushi ganin yadda yaran suka shaku sosai da Aunty.
ta ce a je a kawo mata sauran kayansu dan rabin kayan nasu yana wajenta.

Suna fita ya janyo ta jikinsa ya ce
"Kin ji da kunnen ki ko, bani kad'ai ke son yara da yawa ba, har da iyayen nawa."
fuska ta kwab'e tana turo lips.

A ranar ya d'auki matar sa suka koma gidan sa, a can suke yin rainon wannan cikin.....



Bayan wata tara.

Feeryal ce zaune a parlour ta ta saka cikin ta gaba, tana cin kayan fruit, ita kad'ai ke zaune a parlour, Abdulrahim ya tafi asibiti.
tun da cikin nata yakai watan haihuwa baya fita yana tare da ita, suna zaune ya sami kira daga Dr Omar High doctor of general hospital, kiran gaggawa yazo ya taimaka musu da wani C'S d'in da ya shige musu duhu.
karar dirowar abu taji a bayan ta, da sauri ta waiga.
ta wani irin zabura ganin wasu halittu biyu sun bayyana a bayan ta.
kafin tayi aune sun d'auketa sun b'ace da ita.

A can cikin fadar sarki bakaken aljanu, daya tura dakarunsu su d'auko masa Feeryal.
wan da Sarki Aljani Matip yake ganin komai,
a take ya bada izini wa dakarunsa da suka yi shekara da shekaru suna zaman jiran umurnin sa, kan kamo azzaluman nan,
kafin isowar su da ita sarki aljani Matip, ya umurci dakarun nasa sukaje suka kamo mishi sarkin babaken aljanu ad'aure.
in da sauran dakarun suka zarce kogon sarkin bokaye boka Lazzi da boka Mali, da sauran mabiyan su sauran bokaye masu b'arna a ban kasa.
aka durkusar da su gaban sarki Matip.
Feeryal da ke tare da dakarun sarkin babaken aljanu dakarun sarkin Aljani Matip suka kamasu tare da ita suka kaisu fadar sarki Matip.
a take a gurin Sarki Aljani Matip ya yanke musu hukunci dai-dai da laifukansu.
Sarkin bakaken aljanu aka d'aure shi cikin kejin karfen da akayi shekara da shekaru ana kerashi wanda babu makaren da zai iya bud'e shi har ya kare rayuwar sa ya mutu.
sannan aka d'auke shi aka jefa shi cikin tsakiyar tekun Matip.
sauran mabiyansa aka jefasu a kurkukun da shima babu fita, manya manyan aljanu ne majiya karfe ke kula da gurin,
su boka Mali suma aka kai su kurkukun da aka d'aure Umma Karima ciki, aka had'ata da su akacigaba da hukuntasu...

Tun da ya shigo bai ganta a parlour ba, da sauri ya shige cikin bedroom yana fad'in
"Beauty kina ina?."
ganin bai ganta cikin d'akin ba ya wuce bathroom nan ma taba ciki.
da sauri ya fito yana leka sauran d'akunan da kinan sunan ta.
amma wayam bata nan.
cikin hanzari ya fita ya nufi gurin mai gadi yana kiran wayarta yana shiga amma ba'a d'agawa.
ya tambayi mai gadin ko ta fita ne.
mai gadin yace tun fitar sa bata fita ba tana ciki.
shiru yayi da tunanin iri-iri cikin kwakwalwa da zuciyar sa.
sai kuma da sauri ya nufi gurin mota ya shiga da mugun gudu yafita a gidan.
ya kunna computer motar yasoma tracker yana tracker in da take ta hanyar bibiyar wayarta.
har ya kawo shi kungurmin dajin da take.

Da sauri ya sauka a mota yana waige gami da kwad'a mata kira
"Beauty Beauty Beauty!! ki na ina!!!."
yayi maganar cikin karaji sosai.
da sauri ta zabura daga in da take zaune a keb'abb'en guri, ita da su Chuchu da Chulu,
wanda a gurin aka ajiyeta duk abun da ake sunata janta da hira bata san duk abun da ya faru ba.
da sauri ta nufi in da take juyo sautin muryarsa,
da karfi ta amma kiran nasa
"Sahaaab kana ina."
Chuchu ta ce
"Dakata Feeryal bari mu kai ki in da yake."
suka ruko hannunta kamar kiftawar ido ta ganta a bayan sa.
"Sahab!."
ta fad'a da karfi tana nufowa in da yake da gudu.
shima da gudu ya nufo ta ya rungume ta yana huci.
cikin kakkausar murya mai cike da karaji sosai yake fad'in
"Na rantse idan kuka cutar min da mata da 'yata dake cikin ta,
duk bazan kyale ku ba,
me yasa zaku d'auke ta kuyi gaggawar cireta cikin lamarin ku,
kada ku sake sakota cikin lamarin ku idan kuma ba haka ba, wlh duk bazan kyaleku ba,
d'aya bayan d'aya sai na kashe ku."
daga saman su sukajiyo magana
"Garkuwa a gafarce mu, ka d'auki matar ka kuje, daga yau babu mai kuma shiga lamuran ta."
a fusace ya ce
"Kunyi wa kanku."
ya kama hannunta suka nufi gurin mota ya bud'e mota ya sakata shima ya shiga.
ya ja motar a fusace.

Tun a hanya nakuda ya kamata, sabo da firgicin data shiga, dan haka direct asibiti ya shige da ita.
suna isa bada b'ata lokaci ba ta suntulo 'yarta mace.


Bayan wani lokaci...


Motar Abdulrahim ne ya shigo gidan in da suka kawo wa su Aunty ziyara.
suka fito a motar da ka gansu kasan nutsuwa da kwanciyar hankali yasami masauki a tare da su.
Feeryal takara kyau da girma,
shi kansa gogon ya kara murjewa.
Sheerah na rike a hannun Abdulrahim suka shiga sashin Aunty.
Zahra Saddeeq Haydar suna ganin su suka taho da gudu suka rungume su, suna musu oyoyo.
Zahra da ke da shekaru biyar ta karb'i
Sheerah dake hannunsa tana mata oyoyo.
Aunty na zaune tana ta binsu da murmushi.
suka karaso ta karb'i Sheehra tana mata tsalle tana kyakyatawa.
Daddy ya shigo duk yaran suka mike suka tafi da gudu suka rungume shi.
shima ya rungume su da farinciki, yana d'aga su yana cillasu sama.
yaruko hannayen su ya karaso yana amsa gaisuwar da su Feeryal suke masa.
ya dube su cikin kula da ganin yadda rayuwar su yake tafiya cikin saiti ya ce
"Allah ya muku albarka da ku da 'ya'yan ku baki d'aya."
Aunty ta amsa da amin amin.
bayan sun gaisa, suka d'unguma da yaran sukayi sashin Mommy.
suna shiga yaran suka rungume ta suna yi mata oyoyo.
Zahra ta mika mata chocolate d'aya dake hannunta tana ciki ta ce
"Mommy ga tsaraba."
Mommy ta girgiza kai tana fad'in
"Aa na gode kici ni ina azumi."
Zahra ta rike hab'a tana cewa
"Watan azumi ya kama ne?, yau fa Saturday ne kuma Ammie ta ce ba'a azumi sai ranar litinin da alamis, to ke azumin ranar Saturday kike?."
ta karasa maganar tana dafe kumatu, irin abu ya baka mamakin nan.
murmushi Mommy tayi ta janyo su dukansu jikinta Zahra Saddeeq Haydar Sheehra.
sannan ta ce
"Ina azumi Zahra azumi sittin zanyi, na kashe muku 'yan'uwan ku da nayi."
da sauri Feeryal ta ce
"Mommy ki dai na fad'a musu dan Allah."
Abdulrahim daya karaso ya zauna ya ce
"Mommy babu amfanin fad'an kada ki saka musu hakan a ransu."
Mommy ta girgiza kai tana share kwalla ta ce
"Ku yafe min Feeryal Abdulrahim, bazan dai na rokon yafiyar ku ba,
yaushe nima zaka bani 'ya'yan ka na rike, kana gudun kada na kuma kashe maka 'ya'ya ko,
wlh nayi nadama ina bakinciki da abunda na aikata a baya."
ya ce
"Mommy bai kamata ki rika dawo da abin da ya wuce ba, mu tuntuni muka mance,
idan ta haifi wannan cikin za'a baki, dan Sheehra Aunty nayi alkawarin bawa itama,
dan 'ya'ya biyar nayi niyyar bata."
Mommy ta jinjina kai tana cewa
"Hajiya Fatima ta cancanci fiye da haka."

Suna fita daga parlour'n Mommy ta matse shi a jikin bango.
ta ce
"Me kace idan na haifi wannan cikin wani cikin so kake kace akwai wani ciki a jikina?."
gira ya d'aga mata yana kashe mata ido d'aya.
da sauri ta shiga bugun kirjin shi tana fad'in
"Ni dai Allah na gaji ka tsai da min haihuwar nan haka."
da sauri ya rungumo ta yana cewa
"Kina haifo wannan zaki huta,
kafin ki haifo mana namu,
wan da zamu rika ganin sa a kusa da mu,
yanzu zamu barwa Aunty wannan, taji a ranta itama batayi rashen 'ya'ya ba."
baki ta turo tana lafewa a jikin sa.
bakinsa ya kawo saitin kunnen ta ya ce
"Fad'a min abin da ke cikin zuciyar nan naki."
kwayar idanunta ta d'ago ta kalle shi, sannan cikin siririyar muryarta mai sanyi ta ce
"Meye a cikin?."
hancinta ya ja ya ce
"So na mana amma baki tab'a ce min kina so na ba."
ido ta lumshe tana manna kanta a kirjin sa.
ya kawo bakinsa dai-dai santin kunnen ta ya furta mata
"I love you so much in my life, ke rayuwa ta ce Beauty."
ido ta kuma lumshewa tana shigewa jikinsa.
tana jin wani irin sanyi mai sa nutsuwa yana ratsa jini da jijiya gami da kwakwalwa da rai da zuciyarta......


Ai kuwa kamar yadda ya fad'a. wa Aunty suka barwa Sheehra, suka koma gida suka soma rainon cikin da za'a baiwa Mommy idan an haifi abin da ke cikin.....!




*Tammat bi hamdullah*


Anan na kawo karsher wannan littafi mai suna FEERYAL.
ina fata za'a amfana da dasusan da ke cikin sa.
ya rabbi kasa mufi karfin zuciyar mu ka iya mana da iyawar ka kar ka barmu da dabaran mu.
mu had'u a littafi na na gaba.

Kai ga yadda suka kure ido dan son jin sunan littafin😂
bafa zan fad'i yanzu ba dan zan iya samin masu tashi na a bacci🤗
ka-ki tuntub'eni ta wannan number 👉🏻 08034690723 daga zaran na fara sakin sabon book zaka-kiji.

Masu niman HAMDAH da KARSASHI da sauran book's d'ina kuma ku neme ni ta nan don samin litattafai na 08034690723
Ina maraba da ku masoya na🤗

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login