Showing 66001 words to 69000 words out of 92772 words

Chapter 23 - KWANTAN BAUNA BOOK 1 COMPLETE by Nana haleema.txt

20 Jul 2024

17690

Gidan da ya saba zuwa yaje ya zauna shi kad'ai yana tunanin da ya saba kansa a kulle kamar ko yaushe. idanun sa a kulle yana zaune ko motsin kirki bayayi babu abinda yake ji a zuciyar yake kuma gani sai Rauda ba tare da yasan dalilin hakan ba kawai ji yake zuciyar sa na motsawa a kan hakan. Ya sauke numfashi mai k'arfi ya tashi zaune sosai yana mutstsika idanun sa, jinin jikin sa yake ji tana shiga ko ina ya rasa gane tausayin ta yake ji sabida ta rasa k'afar ta ta dalilin Hydar ko kuma me? Bai sani ba bai san meyasa yake ganin ta always ba ko yaya ya kulle idanu ita yake gani; ya kasa banbance itace ta mafarkin sa ko ba ita bace?.


"RAUDA!" ya furta a bayyane yana jin wani iri a jikin sa gashin jikin sa na rinsing ba tare da ya san dalilin hakan ba, wayar sace ta d'auki k'ara ta katse masa tunani ya kalle ta yaga sunan Hafiz ne yayi banza bai d'auka ba aka kuma kira ya kalla yaga d'aya daga cikin wanda ya saka su kai su Rauda ofishin yin fasko d'in ya d'auka, "Ranka ya dad'e, Allah ya taimaki yarima, Allah ya ja zamanin ka, ya baka tsahon rai ya taimake ka a duk inda kake."
"Uhum" ya furta kawai ba tare da yace komai ba.
"Ranka ya dad'e anyi abinda kace, yanzu haka mun sauke su sun shiga gida."
"Good" yana furta hakan ya katse wayar bai tsaya yaji mai zasu ce ba.


Lumshe idanu yayi ya tuno lokacin da take hawaye tana masa godiya sai yaji kasala ta saukar masa ya koma ya kwanta a akan kujera yana jin wani irin yanayi a jikin sa.
'You love her' yaji zuciyar sa ta furta hakan ya saka shi saurin tashi ya bud'e idanun sa yana ji zuciyar sa na gasgata masa abinda ta fad'a.


"A'a ba haka bane" ya furta yana cize bakin sa.
'Da gaske Asad haka ne ka yarda.' zuciyar sa ta sake fad'a ya dafe kansa da duka hannayen sa jin yana juya masa. Tashi yayi ya d'auki makullin mota ya fita daga gidan da sauri jikin har shaking yake yi.


*☆☆*


"Uncle ka kira ni then kayi shiru ina da abinda zanyi" Aliyu ya fad'a yana kallon waziri da yake zaune yana facing d'insa. Numfashi ya sauke yace, "Wato Aliyu abubuwan ne suke d'aure min kai, ace kamar ka babba kaine namijin farko da mai martaba ya samu amma a dinga mik'a sarauta ga k'anin ka?. Kasan jiya mai martaba ya zauna da Asad kuma ya tabbatar masa da shine zai mulki garin nan?."


Kafin Aliyu yayi magana yace, "ga kyau, ka k'ima, ga k'asaita, ga nagarta, ga izza, ga ilimi, ga wayewa, ga sanin ya kamata. Waye ya cancanci zama sarki in ba kai ba?. Kai ka san ina son sarautar nan amma sabida dacewar ka ya sanya na hak'ura na sallama; ranka ya dad'e wallahi inda zaka zama sarki zan cigaba da zama matsayin wazirin ka amma meyasa mai Martaba yake fifita Asad a kan ka? Meyasa kowa maganar sa a akan Asad take sab'anin ka?."


Zuuuuu haka Aliyu yake jin k'asaita da zugar da ake masa na shiga cikin jikin sa, kansa yake ji a sama kamar shine yake mulkin duka duniya, wani irin yarrrr yake ji a jikin sa har bai san ya cize bakin sa ya kalli Waziri yace, "Kana so kace min kana bayana? Kana so kace min kaima ni kake so na zama sarki a garin nan kenan?."
Murmushi waziri yayi yace, "Dari bisa dari, ni daman kaine nawa ai tun kana k'arami ba Asad ba, in kana musawa ka tambayi mahaifiyar ka zats baka labari."
Wani irin kallo Aliyu yake masa na ka raina min hankali amma sai ya murmusa yace, "Ta yaya zan yadda bayan kaima kana harin mulkin nan?."
"A bayyane yake ai ranka ya dad'e, indai kai zaka mallaka wallahi nidai na hak'ura."


Murmushi Aliyu yake na kana mayar dani yaro k'arami bai ce komai ba ganin murmushin da yake yi sai Waziri yace, "shine nace me zai hana baza mu samo mafita ba; matuk'ar Asad ya mallaki garin nan shiga gidan sai ya gagare mu, ya kamata mu san abinda zamu yi."
"Ina jinka."
Ya gyara zama yace,"Na shirya wani abu a raina amma ban sani ba ko zaka amince."
Da hannu yayi masa alama da yana jin sa.


Gyara zama ya sake yi yace, "Daman mafita ce na nemo amma ina jin shayin fada maka." Aliyu ya d'ora k'afa kan d'aya yana kad'awa yace, "Go ahead."
"Daman cewa nayi mai zai hana mu b'atar da Asad ya bar k'asar nan ma'ana ayi masa abinda bazai sake waiwayo mu ba, kai kuma sai ka koma acting d'in Asad a fad'awa duniya Aliyu ne ya b'ata ba Asad ba. Ni da kai mun san Aliyu ne yake nan amma duniya za'a ce mata Aliyu ne ya b'ata; kaga mai martaba zai mallaka maka mulkin katagum a matsayin Asad kaga shikenan ciki lafiya baka lafiya."


Wani irin kallo Aliyu yake masa gaban Waziri sai fad'uwa yake yi yana b'oye tsoron sa babban burin sa kar yak'i amincewa da batun sa hakan ya saka tsoro ya bayyana k'arara a tare dashi duk da yana so ya b'oye amma hakan ya gagara sai da tsoron ya kwanta a fuskar sa. Numfashi Aliyu yayi kafin ya saki dariya mai d'auke da izza da k'asaita kafin ya kalli waziri yace.......


*KWANTAN ƁAUNA*


©️ *Nana Haleema.*


*Book 1*
*019.*


Irin kallon da yake yi masa jikin Waziri yayi sanyi qalau kuzarin sa ya ragu amma duk da hakan bai nuna ba ya daure ya cije baya so ya bayyanar da raunin sa kar Aliyu ya gano shi, Aliyu wani irin murmushi yake yi ya sauke k'afar daga kan d'aya ya kalle shi ta k'asan idanu yace, "kana ganin hakan zai yu kuma?."
Jin abinda yace sai ya sauke ajiyar zuciya yace, "Mai zai hana ya yu ranka ya dad'e?, indai zaka bada goyan baya abu ne mai sauk'i faruwar hakan."


Ya juya manyan idanun sa ya sauke su akan Waziri kana ya mik'e tsaye yana kallon sa yace, "Zan yi tunani a kan hakan" yana gama fad'ar hakan ya fita daga falon bai sake kallon waziri ba. Waziri ya dafe k'irji gaban sa yana fad'uwa sosai ya d'auko waya da sauri jikin sa har rawa yake, kiran yake ba'a d'auka ba ya cillar da wayar akan kujera ya mik'e yana zaga d'akin.
"Me yaron nan yake nufi dani? Yaji sirrina a banza ya tashi ya tafi ya barni....? kenan yana nufin na jira shi?, in bai amince bafa?." Naushin iska yayi ya koma ya zauna jikin sa har b'ari yake sabida tashin hankalin da yake ciki.


Kamar kuma anyi masa allura ya mik'e da sauri ya shiga d'aki dan bai ga ta zama ba.




Aliyu lokacin da ya fita mota ya shiga ya zauna yana tuno abinda Waziri ya fad'a masa sai yayi murmushi yaja tsaki yace, "Wai ni zai yiwa wayo, an fad'a masa ni d'in shashasha irin sa?, ko kuma ya d'auka zuciya ta irin ta Asad ce?." Sai kuma ya tsaya da dariyar ya d'auki waya da sauri ya kira Waziri, kamar jira yake yaji an d'auka ya gyara murya yace, "Na amince da tayin ka." Yana jin ajiyar Wazirin a waya baice komai ba ya yanke wayar ya ajjiye wayar wayar yana kallon glass d'in gaban motar.


Asad bai koma gida ba sai da ya gama yawon sa har dare yaci abinci sannan ya koma, ko wajan Mama bai shiga ba ya shiga apartment d'in su ya tarar da Aliyu a zaune ya kunna sigari yana sha, har ya wuce ya dawo yana kallon sa har ga Allah baya son warin ta ko kad'an ya masa magana sau babu adadi amma yak'i.
"Aliyu ko a lafiyar ka abinda kake yi ba daidai bane" ya furta yana kallon sa. D'ago idanun sa yayi ya kalle shi ya murmusa ya sake zukar sugarin ya fesar kana yace, "lafiya ta kace ba taka ba, a gani na ai hakan ba damuwar ka bace ba."


Asad bai kuma cewa komai ba ya d'aga kafa zai wuce yaji yace, "kabi a hankali ka kuma taka tsan-tsan akwai lokaci Asad." Baice komai ba ya wuce ya k'yale shi ya shiga d'akin sa. Can k'arshen d'akin ya wuce ya janye labule sai ga k'ofa ta bayyana a wajan wacce in ba kasan da ita ba baza ka tab'a cewa tana wajan ba ya shiga ciki ya kulle k'ofar. K'aton wajan karstu ne mai d'auke da drawer na littafai manya-manya na addini dana karatun zamani, littafai ne sama da guda dari uku a wajan ko wanne rukuni da cover sa da sunan su a k'asa ga table da kujera mai guda d'aya a wajan da k'aramar lamp a kai.


Kujerar yaja ya zauna ya dafe kansa da duka hannayen sa biyu kansa na juyawa ya rasa dalilin da ya saka yake jin hakan da zarar ya shigo d'akin sa, daurewa yayi ya tashi ya k'arasa jikin cover ya d'auki littafai guda biyu ya k'araso ya zauna a kan kujerar ya fara dubawa. Karantawa yake a nutse yana bin rubutun daki-daki yana Nazariin abinda yake yi.
Rufe na farko yayi ya bud'e na biyun yana sake bi a hankali har ya kammala karanta inda yake da buk'ata ya kulle ya kifa kansa a kan littafin kamar mai bacci.


Juma'a ce gobe kuma shine zai gabatar da hud'uba shiyasa yake ta dube-duben littafai amma zuciyar sa ta kasa bashi topic guda d'aya da zaiyi hud'ubar a kansa, d'ago kai yayi ya saka hannu biyu ya d'an daki kansa a hankali ya furzar da iska waje yana kallon d'akin gabad'ayan sa. Zuciyar sa yaji yana bugawa da sauri har yana jin sautin ta a kunnen sa ya runtse idanun fuskar Rauda ta bayyana a gare shi.
"Hasbunallahu wani'imal wakil" ya furta a hankali yana dafe da kansa har lokacin bai kuma daina jin bugun zuciyar ba.


Cize bakin sa yayi ya runtse idanu kafin ya koma ya jingina da kujerar, sautin muryar ta yake tunowa a hankali tana shiga ilarin jikin sa, tasirin muryar da dad'in ta ya saka shi kulle idon sa yana sauke numfashi gashin jikin sa na tashi. sautin muryar yarinyar mafarkin sa yaji sai ya bud'e idanun sa; ya kasa banbance shin itace yake gani a mafarki ko kuma ba ita bace?, bai tab'a ganin waccan fuskar ta completely ba amma idanun ta da goshin ta irin na Rauda ne, akwai banbanci a maganar su waccan muryar ta tafi zak'i a kan ta Rauda, ita kuma ta Rauda tafi sanyi da taushi kamar mai mura in tana magana.
Tashi yayi ya kashe hasken d'akin ya fita daga cikin da ya dawo d'akin sa ya zauna a gefen gado ya rasa tunanin ma mai zaiyi.


Kiran wayar Suhail ya gani ya jawo wayar ya d'auka ya saka a kunnen sa yayi shiru alamun ana yi masa magana kafin yace, "Alright" daga haka ya yanke wayar ya tashi ya shiga band'aki. Sai bayan ya gama komai sannan ya kwanta da burin Allah ya sa yau yayi mafarki da yarinyar da yake gani ko zai gane ta.


Washe gari da ya farka yaso yaje ofishin fasko amma sabida juma'a ce dole ya tsaya yayi hud'uba ya saka babu inda yaje har aka shiga masallacin cikin gari, kamar ko yaushe yayi hud'uba ya kuma yi sallah bayan an idar ya hau mota ya wuce office d'in. Da kansa ya karb'o faskunan nasu guda uku da hotuna yana shiga mota ya zauna yana kiran agent d'in su a waya, ana d'auka yace, "Egyptian visa nake so guda uku" Shiru ya kuma yi kafin yace, "Okay better" yana fad'a ya yanke wayar ya ja motar sa ya bar wajan.
Gida ya wuce ya ajjiye faskunan ya fito zuwa wajan Mama kamar yadda ya saba. A hakimce ya same ta tana danna waya kamar koda yaushe ya zauna a gefen ta kana yace, "Barka da juma'a."


"Barka Asad" ta furta kawai ba tare da ta kalle shi ba. Shiru ya biyo baya babu wanda ya kuma yin magana kafin yace, "Mama anyi inviting d'ina wani event a Cairo"
"Kwana nawa zakayi?."
"I think one week."
"I'm not allow u to go."
Kallon ya yayi itama ta kalle shi yace, "but Mah...." D'aga masa hannu tafi tace, "Na gama magana Asad, tafiya indai ba ta kwana biyu bace ban amince ka jeta a yanzu ba maybe kaje wani lokacin."


Numfashi ya sauke ya tashi ya fita daga falon nata zuwa falon Hajiya kamar yadda ya saba duk juma'a, tana zaune ita da hidiman ta ya shiga da sallama, "Barka da zuwa Yarima, barka da zuwa fari mai farar wutsiya, fari mai farar aniya, indaroro sai kan soro, kaga tufa mad'aukar d'aki, sikari bakayi farin banza ba, walikiya kake duk inda kabi sai ka haska......" zasu kuma magana ya d'aga hannu sama sukayi shiru cikin girmawawa.
Murmushin yake take tana kallon sa ya zauna a k'asa yana kallon yace, "Barka da Juma'a Hajiya"
"Barka dai Asad, ya jama'a ya kuma k'ok'ari?."
"Alhamdulillah, ina suke?" Ya fad'a yana kallon falon alamun yana neman kannen sa.


"Sunje gidan Yayar ku sai zuwa anjima zasu dawo." Tunda tace Yayar ku ya gano wacce take nufi dan babar yar ta wacce ta kasance babba a gida gabad'aya bata fad'ar sunan ta daman. "Na barki lafiya" ya fad'a yana mik'ewa tsaye tace, "Na gode Asad." Bai amsa ba ya fita ya tafi b'angaren Umma, kamar ita tana zaune itama a zagaye da hadimai suka gaisa kamar waccan ya tafi.
Kasancewar rana ce bai samu mai martaba ya bada kud'in da ake rabawa dan bazai samu damar yi da kansa ba ya koma apartment d'in sa.


Sai yamma sannan wanda zai karb'i faskunan yazo ya bashi ya wuce Abuja dasu domin a buga musu visa. Bayan wanda karb'a ya tashi yana zaune Suhail ya kira shi, bai d'auka ba har ta katse bayan ta katse ya d'auki wayar ya kira hidiman k'ofar ya bada umarnin a bar shi ya shigo ya ajjiye wayar.
Da sallama ya shigo ya zauna kusa dashi Asad yace, "Suna bin umarnin Mama ne."
Suhail ya murmusa yace, "Hakan yana da kyau sosai tsoron lafiyar kace, sai naga kamar ka rame." Tab'e baki yayi baice komai ba kafin Suhail ya kuma cewa, "me yake faruwa?."


Iska ya furzar a hankali yana sauke numfashi amma bai ce masa komai ba, jin hakan sai shima yayi shiru ya saka hannu a aljihun gaban rigar sa kamar mai neman wani abu, "me kake saka min?" Yaji muryar Asad a kansa yayi saurin janye hannun sa daga kusa dashi.


Had'a idanu sukayi Asad ya d'aga gira alamun ya bashi amsa, nutsuwa ya aro ya saka a fuskar sakana yace, "me kuwa zan shafa maka Asad? Kalli hannu na mana" ya fad'a yana nuna masa tafikan hannun sa. Murmushin gefen baki Asad yayi kafin ya d'auke kansa daga kallon sa yace, "lafiya ka ke nema na?."
"Normal ina so mu had'u ne kawai."
"Really?" Asad ya fad'a yana wara idanun sa waje.
"Sure, naga duk ka canja Asad kamar baka yadda dani ba, ko da Aliyu nake tare ne ban sani ba?."


Baice masa komai ba ya shafa kai kawai kafin yace, "u can go." Suhail ya kalle shi yace, "Okay bye" ya fad'a yana mik'ewa ya fita yana mamakin canjawar Asad. Waya aka kuma yi masa ya kalla yaga masu tsaron k'ofar sane ya share kiran ya katse aka kuma kira ya ja k'aramin tsaki ya d'auka baice komai ba, daga can b'angaren suka ce, "Ranka ya dad'e Allah ya wuci zuciyar ka na dame ka, wata yarinya ce take so tayi magana da kai, tana ta magiya mu barta ta ganka."


Jimm Asad yayi yana tunani kafin ya bada umarnin tazo, ba jimawa ta shigo da sallama jikin ta har rawa yake ta zube a kan carpet tace, "Barka da yamma ranka ya dad'e."
"Wacece ke?" Ya furta a hankali yana kallon ta.
"Sunana Habiba ni jikar Gwaggo Gambo ce da take gidan nan. K'awa tace ta samu matsala da Yallab'ai Aliyu to tsoro take ji kar ya mata wani hukunci shiyasa muka kawo k'ara gaban ka a taimaka a bashi hak'uri. "


Shiru yayi bai amsa ba hakan ya saka tace, "Sunan ta Rauda tana da matsalar k'afa shiyasa bamu zo tare ba, mun tab'a zuwa gidan nan da ita ta buge shi bata sani ba ya mare ta, had'uwar su ta biyu kusan hakan ce ta faru, had'uwar su ta uku shine ta mayar masa da abinda ya fad'a mata. Yayi alwashin sai ya d'auki mataki a kanta duk taji tsoro sai kuka take hankalin ta ya tashi matuk'a. A bashi hak'uri ranka ya dad'e wallahi y'ar talakawa ce kar ya cutar da ita."


Yana sauraron ta dan a hankali take maganar hakan ya saka shi nutsuwa yana jin ta, tunda ta ambaci Rauda gaban sa ya fad'i ya sake bata hankalin sa har taje k'arshe kafin, "kar ki damu."
"Na gode ranka ya dad'e, Allah ya k'ara lafiya da nisan kwana, ya ja da ran Mama da mai martaba." A lab'b'an sa ya amsa da amin ya sanya hannu a aljihun sa ya d'auko kud'i ya mik'a mata ta karb'a hannu na rawa zatayi godiya ya d'aga mata hannu ta tashi ta fita.


Numfashi ya fesar kalmar ya mare ta tana yi masa amsa kuwa a kunnen sa nan take ransa yaji ya b'aci ba kad'an ba yaja tsaki baiyi niyar fita ba amma ya tashi ya fita daga gidan gabad'aya.


Habiba na barin gidan wajan Rauda taje ta bata labarin duk abinda ya faru har kud'in da ya bata ta nuna mata, Rauda tace, "Bari kawai Habiba baki san me ya faru washe garin da kika zo nan ba."
"Meya faru to?."
Kwashe duk abinda ya faru tayi ta fad'a mata sannan ta d'ora da cewa, "Jiya ya saka aka kai mu ofishin fasko za'ayi mana zai kaini waje ayi gyaran k'afa madadin k'anin sa."
Habiba tace,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login