Showing 18001 words to 21000 words out of 92772 words

Chapter 7 - KWANTAN BAUNA BOOK 1 COMPLETE by Nana haleema.txt

20 Jul 2024

17681

a cikina shine yake irin wad'annan halayen mara sa kyau da dad'in ji, kuma a haka yake burin kasancewa sarki a garin nan."
"To ya za'ayi sai hak'uri ai." Shiru ya biyo baya dan ita dai bata san maganar shiyasa ta katse ta kafin tace, "ya batun ajjiye sarautar taka?."


"Na jinkirta zuwa nan da wani lokaci, ina so komai ya zama dai-dai kar a bar baya da k'ura. In kuma kafin lokacin na bar duniya shikenan." Nan ma shiru tayi bata ce komai ba zuciyar ta na cigaba da fad'a mata k'arya da gaskiya a kan komai da ya shafi lamarin gidan sarautar da take ciki.


Washe gari.


*☆☆☆*
Rauda ko aikin gida bata samu ta tashi tayi ba duk da daman gyaran gidan Rahma ne ciwon kai ya mata mugun kamu dak'yar take iya juya kanta, har su Khairi suka tafi makaranta bata sani ba tana bacci sai goma na safe ta tashi tayi mamakin baccin dan bata saba jimawa haka ba. Sosai taji dad'in ciwon kan tayi wanka ta karya ta zauna a kusa da mahaifiyar ta suna hira. Har akayi Azahar babu inda taje tana kusa da ita duk da tana so ta fita taje gidan da take karb'o sarin alawar madara amma ta kasa fita.


"Ke Rauda! Ke Rauda!!, maza fito" Baba ya fad'a daga waje. Mik'ewa tayi ta fito ta ganshi da kular da ta saba fita siyar da abinci tace, "Baba gani." Kallon ta yayi yace, "To maza a tafi, na dubu biyu da dari uku ne ki lisaafa dakyau in zaki bawa mutane."
Kallon sa take yi da mamaki a fuskar ta ganin hakan ya saka shi yace, "Wai ke a tunanin ki dan jiya baki fita ba yau ma baza ki fita ba?, yo ko saurayin naki ya kawo min abinda yafi keke ai siyar da abinci yanzu kuka fara Rauda. Maza d'auki ki tafi bana son b'ata lokaci."


Khairi da ta dawo daga makaranta ta fito daga d'aki tace, "Baba kanta ciwo yake." Ya harare ta yace, "ta sha magani kafin ta k'arasa zai warke, d'auko hijjabi ki maza ki wuce ki tafi." Jikin ta a sanyaye ta shiga suka had'a idanu da mahaifiyar ta da take jin su bata ce komai ba ta d'auko hijjjabin ta fito ta saka takalmi.


"Kina wata tafiya kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki in baki hanzarta ba Rahma ta dawo ta barki wallahi ranki ne zai b'aci. In bakya son zuwa ai jiya saurayin ki ya baki kud'i d'auko su yanzu ki siye abincin ki bani kud'in kiga in baki zauna a gida ba." Bata ce kanzil ba ta sukunya ta d'auki kular ta fita daga gidan gabanta yana fad'uwa.
Tsaki yayi ya fice babu wacce ta tanka cikin matan nasa kowa yasan halin sa shiyasa ko wacce taja bakin ta ta tsuke.


Ko a can inda suke zama suna siyar da abincin Rauda ranar gabad'aya bata da walwala kana ganin ta kasan bata da lafiya duk da daman ba magana take da mutane ba, tana nan zaune Khairi tazo wajan ta tace, "Anty kije gida ni zan cigaba da siyarwa." Girgiza kai tayi tana kallon ta tace, "ya akayi baki je islamiyya ba?."
"Yau alhamis ai babu shiyasa ban je ba."
"Ki koma gida Khairi nima yanzu zan tawo."


Zama tayi kusa da ita tace, "Zan jira ki a nan." Suna nan zaune ga abincin bai k'are ba Rauda taji jiri yana d'aukar ta ta mik'e tace, "Khairi d'auki kular nan muje kawai." Ba musu ta tashi ta d'auka suka tafi. A hankali suke tafiya dan sosai Rauda take jin jiri sabida yadda kanta yake sarawa.
Titi suka zo tsallakawa Khairi ta tsallaka ta barta tana fad'in, "kya tsallako da kan ki dan nasan halin ki da tsoron titi bazan jira ki ba."


Rauda bata ce komai ba ta saka k'afa a kan titi da niyar tsallakawa sai da tazo tsakiya ba zato babu tsammani taji anyi sama da ita an dawo da ita k'asa ta fad'i a gaban motar, wata razananniyar azaba taji a dukkan ilarin jikin ta musamman k'afar ta dalilin hakan ya sanya ta sumewa a wajan. Ihuu Khairi tayi a haukace tace, "Anty Rauda!" Ta fad'a a guje tana tsalkawowa daidai lokacin wanda yake zaune a cikin motar ya fito a gigice yana kallon Rauda da take kwance cikin jini hankalin sa a tashe............


*KWANTAN ƁAUNA*
FitattuBiyar 2023.


©️ *Nana Haleema.*


*Book 1*
*006.*


A guje Ummulkhairi ta tsallako a lokacin Hydar yayi inda take kwance hankalin sa a matuk'ar tashe ya d'auke ta cak ya saka a bayan mota bai ma kula da Ummulkhairi da take kuka ba ya shiga motar ya ja a guje a hankalin sa tashe. Kasancewar titin babu jama'a sosai babu wanda ya lura da abinda ya faru Ummulkhairi ta kwasa a guje ko ta kan kwanikan abincin bata bi ba ta tafi gida.


Babban asibitin kud'i na garin ya wuce da ita jikin sa gabad'aya rawa yake fuskar ta ta tasa lokaci d'aya har lokacin bata motsin kirki, k'ara gudun motar yake yi har ya isa asibitin nan take yayi waya akayi sa'a likitan da yake nema yana nan aka fito a guje aka d'auke ta aka wuce ciki. Gabad'aya ya kasa nutsuwa yana zaune a office d'in Dr amma zuciyar sa bugawa take da sauri, bai tab'a buge koda kaza ba tunda ya fara tuka mota sai wannan lokacin, shiyasa hankalin sa ya tashi sosai.


Sun jima matuk'a a kan ta kafin Dr ya shigo yana ganin sa ya kalle shi alamun k'arin bayani nake nema, Dr ya zauna yace, "Prince ta samu karaya a k'afar ta munyi x-ray na k'afar mun gano k'ashin da yake rik'e k'afar ta baya wanda ya kasance bashi da k'wari ya karye shima, k'afar ta d'aya lafiya take sai dai buguwa da tayi amma d'ayar gaskiya tana da matsala munyi iya abinda zamu iya a yanzu in abin baiyu ba gaskiya dole sai anje Egypt."


Hydar ya sauke numfashi ya lumshe idanun sa ya bud'e ya kalli likitan yace, "Yanzun jiran me za'a yi baza a tafi can ba?." Dr yace, "dole za'a jira ciwon ya warke in ka lura karaya ce mai jini ma'ana karaya ce mai had'e da ciwo, in ciwon ya warke in abinda muka yi bai ba shine za'a fitar da ita." Baice komai ba ya mik'e ya fita ya shiga d'akin da take yana kallon fuskar ta da ta kunbura amma kamannin ta basu gushe ba.


Kallon ta yake k'irjin sa na bugawa ga k'afar ta a d'aure haka goshin ta ma an manne shi sabida ciwon da ta samu, numfashi yake fesarwa dana sanin fitowar sa daga gida gabad'aya ta damalmale masa zuciya ya fito daga d'akin suka had'u da Dr d'in a k'ofar d'akin yace, "A nemo family nata but bana so a sanar dasu nine na kad'e ta, a tabbatar musu da za'a tsaya ta samu lafiya ko nawa ne za'a kashe" abinda ya fad'a kenan kawai ya fita daga wajan bai jira ma yaji mai likitan zai ce masa ba.


A can gida kuwa a guje Ummulkhairi ta shiga gida tana fad'in, "Umma! Umma!!" Umma da take tsakar gida ta kalle ta tace, "Khairi lafiya wannan wanne irin kira ne?." Jikin ta har rawa yake tace, "Anty Rauda!, Umma Anty Rauda!" abinda take maimaitawa kenan tana haki alamun ta sha gudu.


Hankalin Umma ya tashi ta k'araso kusa da ita tana fad'in, "me ya sami Rauda d'in? Tana ina?, me ya same ta?."
"Wani ne ya kad'e ta a mota tana kwance bata numfashi Umma, jini yana ta zuba daga jikin ta Umma" ta kuma fad'a har lokacin bata dawo dai-dai ba tana hakki.


"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, wani ya kade ta fa kika ce Ummulkhairi?."
"Eh Umma, ya d'auke ta a mota sun tafi."
"Hasbunallahu wani'imal wakil, Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un!" Abinda Umma take fad'a kenan jikin ta na rawa itama Inna Babar su Rahma kenan ta fito itama tana salati tace, "To banda shirme kuma irin naki sai ki bari su tafi baki bisu ba?."


"So nake nazo na fad'a muku, Umma Anty Rauda jikin ta duk jini ko motsi bata yi" ta k'arasa fada tana fashewa da kuka ta zube a wajan. "Kukan me nake ji haka?" Baba ya fad'a yana shigowa yana kallon su. Ba wanda ya iya magana yace, "Ya naga kunyi cirko-cirko kamar wad'an da aka yiwa mutuwa?, ke ina Rauda?."


"Baba wani mai babbar mota ne ya kad'e ta ya d'auke ta suka tafi a mota." Baba yace, "Ya kad'e ta fa kika ce? A ina ya kad'e ta?, waye shi?."
"Baba ban san shi ba, ya dai kad'e kuma ya saka ta a mota sun tafi."
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" abinda Baba ya furta kenan ya fita daga gidan hankalin sa a tashe.


Dukka mutanen gidan Hankalin su a tashe yake sun kasa koda zama musamman Umma Khairi kuma har lokacin kuka take sosai hankalin ta ya kasa kwanciya tunda a gaban ta akayi ba kuma ta tab'a ganin hatsari a zahiri ba sai a kan wannan. Baba ya jima da fita ya dawo Umma tace, "Malam an same ta?." Baba yace, "ban samu komai, inda aka buge ta d'in tabbas ga jini nan har yanzu yana wajan amma babu wanda yazo ya bada sanarwa koda y'an uwan ta zasu neme ta."


Umma ta dafe kanta tace, "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, yanzu a ina zamu same ta gashi har dare yayi?." Baba yace, "ki kwantar da hankalin ki ko waye ya buge ta zai nemi dangin ta ai kodan kula da lafiyar ta, kiyi hak'uri."
"Ka gani ko?, kaga illar tallan da suke fita ko? Yanzu da basu je tallan ba da babu abinda ya same ta."
"Tsautsayi ne ko tana gida sai ya same ta" ya fad'a yana fita daga gidan gabad'aya.
Umma kasa magana tayi sai tagumi da tayi kawai zuciyar ta na k'una da zafi domin bata san halin da y'ar tata mai tausayin ta take ciki ba.


*◇◇◇*
Lokacin da Hydar ya shiga gida b'angaren mahaifiyar sa ya wuce a nan ya same ta a zaune ita da Asad ta saka shi a gaba tana ta jero masa tambayoyi amma guda d'aya ya gaza bata amsa, yadda ya shigo ya saka ta bishi da kallo tace, "Hydar lafiya?." Kusa da Asad ya zauna yayi shiru kafin ya kalle ta yace, "Accident nayi."


Suhaima tace, "Accident a ina?." Kafin yayi magana Mama tace, "Babu abinda ya same ka?."
"Babu Mama, but na buge wata yarinya yanzu haka ta asibiti unconsciously."
"Da ranta dai ko?" Suhaima ta tambaya tana kallon sa. Kai ya d'aga alamun eh Mama tace, "A ina take yarinyar?."
"I don't know, but zata tsallaka titi ne kawai sun fito daga kasuwa, I think tana sai da abinci ne."


"Mtswww, to meye na damuwa? Ba ka kaita asibiti ba?" Ta fad'a tana kallon sa ganin yadda ya wani damu akan y'ar talakawa. Hydar yace, "Ranki ya dad'e Dr ya tabbatar min in abinda akayi bai yi ba sai an kaita Cairo an yi gyaran a can, taji ciwo sosai a k'afar ta kuma nine sila dole na damu." Mama ta tab'e baki tace, "Is okay tunda dai kai lafiya kake, kaje ka huta." Jikin sa a sanyaye ya mik'e sai a sannan Asad yace, "Sorry Bro." Kai ya girgiza kawai ya fita daga apartment d'in.


"See him akan wata yarinya yar talakawa yake wannan damuwar, I hate dis" ta fad'a tana bin sa da kallo tana yatsine fuska kafin ta dawo da kallon ta ga Asad da yake kallon ta tace, "Dis time bazan d'aga maka k'afa ba Asad dole kaje ka nemo auren Jidda itace zab'ina a wajan ka sai kuma ka aure ta." Kai ya girgiza baice komai ba dan bai san me zaice mata ba.


Baiyi magana ba Suhaima taji wayar ta na k'ara ta mik'e ta fita daga falon gabad'aya ta nufi can k'arshen gidan ta hango wanda ya kira ta a tsaye yana jiran ta, "Hello Suhail, I hope lafiya kake nema na haka?" Ta fad'a tana kallon sa. Kallon ta yayi yace, "lafiya lau Auta, akwai wani abu da nake so na baki ne ban sani ba ko zaki karb'a."
"Meye shi?."
"Magani ne nake so ki bawa Asad ya sha ba tare da ya sani ba." Wara idanu tayi tana k'are masa kallo mai cike da harara da mamaki ganin hakan ya saka shi yin murmushi yace, "bazan cutar da Asad ba kin sani, tunda kika ga na kawo masa kin san naji wata magana ne da take shirin faruwa."


Hannu ta d'aga masa tace, "Bana daga cikin wad'annan shirmen naku kai ka sani, baza kuma ka hani wani abu kace na bawa Asad ba tare da ya sani ba, baza ka had'a kai dani a cutar dashi ba." Ya matso kusa da ita yace, "ba cutar dashi zanyi ba Suhaima, ke kin san baza'a tab'a had'a kai dani a cutar da Asad ba because he's my favorite cousin and he's my friend, wannan maganin da zan baki in ya sha zai karya dukkan abinda za'a aiko masa dashi, u know rayuwar Asad tana cikin hatsari a yanzu, kowa neman ganin bayan sa yake ki taimaka ki karb'a ki taimaki Yayan ki."


Suhaima tayi masa kallon up and down tace, "Kai meyasa baza ka bashi ba?, kamar kai ma ya amince da kai ko?."
"Eh ya amince dashi, amma kin fini kusa dashi kece zakiyi ba tare da kowa yasan hakan ba, sharaɗin maganin ba'a so wanda zai sha yasan an zuba. help us please in wani abu ya same shi dukkan mu ya sama." Numfashi ta fesar tana kallon sa a kaikaice zuciyar ta cike da tunani kala-kala.


"Please Suhaima" ya fad'a yana sake marairaicewa yana kallon ta.
"Sorry I can't" tana fad'ar hakan ta juya ta bar wajan ya bita da kallo yana cize bakin sa ji yake kamar ya jawo ta ya shak'e mata wuya yayi k'wafa ya juya ya bar wajan zuciyar sa cike da k'unar rashin samun nasara.


Direct apartment d'in su Asad Suhaima ta wuce tana zuwa ta tarar dashi a zaune shida Hafiz ta shiga da sallama ta kalle shi tace, "Yaya ka amince da Suhail or not?." Hafiz yace, "what happened?."
"He called me yanzu yana fad'a min akwai maganin da zai bani na bawa Bro deaf yasha wai zai protecting d'in sa daga abinda za'a aiko masa dashi, ban amince dashi ba gaskiya."


"U see na fad'awa Asad Suhail ba abin yadda bane amma always sai yace min shi ya amince dashi, yanzu kin karb'i maganin?."
"No, I'm not."
"Ki kira shi yanzu ki karb'a sai ki zubar dashi in ba haka ba tabbas zai bayar a zuba masa ne, daga yau ko me zai baki akan Asad ki karb'a."
Asad yace, "kar ki karb'a." Da mamaki ta kalle shi tace, "Why?." Idanun sa ya zuba mata akan fuskar ta yace, "abinda nace kenan" yana fad'a ya tashi ya shiga d'aki ta bishi da kallo.


Hafiz ya kalle ta yace, "ban san me yake damun Asad ba akan Suhail, ya kasa gane inda ya dosa har yanzu but muje mu sanar da Mama ita kad'ai ce zatayi maganin abin." Kai ta d'aga alamun haka ne suka fita a tare zuwa wajan Mama.


Asad lokacin da ya shiga d'aki zagaye kawai yake yi a cikin d'akin gabad'aya ya rasa tunanin me zaiyi cikin kwanakin mugayen mafarkai yake da mutane kala-kala suna k'ok'arin cutar dashi, dalilin da ya sanya gabad'aya baya sha'awar yin sarautar ko kad'an amma Mama ta dage shi bai ga abin so a cikin ta ba.


Kan gadon sa ya kallah a gyare yake tsaf dan Suhaima ce kad'ai take shiga d'akin sa ta gyara sai Mama bayan su wani dogari ko baiwa basa zuwa cikin d'akin dan umarnin Mama ne. Tunda ya kwanta jiya a kansa yake jin kansa yayi masa mugun nauyi ga wasu abu kamar allura da yake ji yana sukar sa gabad'aya kansa ya kulle ya ma rasa tunanin me zaiyi.
Ji yayi gidan gabad'aya yayi masa zafi ya d'auki makullin mota ya fita daga d'akin.


Washe gari.


Bayan gari yayi haske sosai Hydar ya d'auki mota ya tafi asibitin da Rauda take ya nufi office d'in Dr da sallama, yana ganin sa ya mik'e tsaye yana fad'in, "Barka da zuwa prince."
"Ya jikin ta?."
"Da sauk'i, mun samo dangin ta ma suna wajan ta a yanzu."
"Good a cigaba da kula da ita ayi mata komai, but bana so suna na ya fito a maganar ka samu wani sunan but banda nawa."


"Okay Prince in sha Allah."
"Let's go" tare suka fito suka shiga d'akin da take nan suka samu Mama da Baba da kuma Inna suna zaune a kusa da ita. Da sallama suka shiga suka amsa Hydar ya kalle su dukkan su kana ganin su kasan talakawa ne duk da duk wanda yake k'ark'arin masarauta talaka ne amma nasu talaucin ya fito yace, "Ya mai jikin?, nine wanda na buge."


Ganin babban mutum mai kalama da kwarjini kamar Hydar sai Baba aka gyara tsayuwa aka ce, "Jiki gashi nan dai har yanzu bata farka ba, sai dai fatan Allah ya bata lafiya." Kusa da gadon nata Hydar ya k'arasa yana kallon ta ya kalle su yace, "zata ji sauk'i, Dr zai mata komai babu damuwa."
"Mun gode Allah ya saka da alkhairi" Umma ta fad'a tana kallon sa. Kai kawai ya d'aga baice komai ba ya fita daga d'akin daman burin sa a samo dangin ta.


Gida ya koma ya shirya zai tafi aiki kasnacewar Friday

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login