Showing 87001 words to 90000 words out of 92772 words

Chapter 30 - KWANTAN BAUNA BOOK 1 COMPLETE by Nana haleema.txt

20 Jul 2024

17700

masa mata tun ba yanzu ba, gidan sarauta gida ne na rikita-rikita kanki bazai d'auki abinda yake faruwa a cikin sa ba koda an baki labari, duk inda kike tunanin abun ya wuce haka gwara ki zauna a gefe hakan zaifi miki alkhairi. Nasan halin mahaifin sa tunda yace amsar ki ake jira ita ake jira indai kika amsa zance ya k'are in kuma kika yi akasin haka za'a fasa shiyasa nazo na shawarce ki akan karki kai kanki ga halaka matsayin da kike k'okarin takawa yafi k'arfin ki akwai mata sosai a gaban ki." Kallon Umma tayi kana tace, "Ke uwa ce baza kiso ki rasa d'iyar ki ba ki bata shawarar kar ta amsa batun Asad domin kuwa tana niyar shiga wuta ne da k'afar ta."


Umma tace, "banda abin ki kinji ance y'ar mu zata auri d'anki ne?." Mama ta tab'e baki tace, "ko d'aya nasan baza tak'i tayin ba ai shiyasa nake fad'a mata gaskiya."
"Ai kuwa sai muce a kai kasuwa domin kuwa tana da wanda yafi Asad d'in" Yaya Ummi ta fad'a tana kallon ta. Kyakykyawan murmushi Mama tayi tace, "tana da daidai ita dai amma bawai wanda yafi Asad ba ko yarinya..? Ta samawa kanta lafiya da kuma zaman lafiya."


Rauda da take gefe tace, "in kuma na amince masa fa?." Mama ta kalle ta tace, "abinda ma bazai yu ba kenan, keda shi sai dai taimako amma yafi k'arfin ya zama mijin ki har Allah ya tashi duniya, Rauda sunan ki ko?" Ta fad'a tana kallon ta cikin k'ask'anci da rainin hankali Rauda tayi dariya tace, "kodai nafi k'arfin sa ba tunda shine yake jiran amsa ta bani nake jiran tasa ba, shi ya gani ya mato yace yana so har kika kasa dakatar dashi kinga kenan nice nafi k'arfin sa bashi yafi k'arfi na ba. Ki rike d'anki daman bana sha'awar auren kuramen maza ni."


"Ke yarinya ki iya bakin ki! Ki san da wacce kike magana" Mum ta fad'a a fusace tana kallon ta Rauda tace, "in kuma nak'i fa akwai abinda za'ayi min ne?." Mama tace, "Naga alama kanki yana rawa sosai kina ji da y'an matanci, ki saita harshen ki tun kafin ya kai ki ya baro ki" ta fad'a tana nuna ta da yatsa. Umma tace, "Rauda ya isa haka." Mama tace, "ya kamata dai kija mata kunne ta san da wacce take magana."
Rauda tace, "Ke kika tako k'afar ki kika zo har inda muke dan haka baki isa ki fad'a mana maganar da batayi mana ba kuma nayi miki shiru ba."


Mama tayi k'wafa tace, "Ba wannan ne a gabana ba abinda na fad'a miki shi ya kamata kiyi, maganar auren Asad ki d'auka a mafarki kika tab'a ji ba a gaske ba" ta fad'a a kausashe. Rauda ta tab'e baki tace, "Umarni ne ko shawara?."
"Umarni ne!" Ta fad'a a fusace tana kallon ta.
"Dalili?" Rauda ta fad'a tana binta da kallon raini. Mama tace, "ke banzo wajan nan dan na fad'a ki fad'a ba, ina so kisan badan Jan kunnen da zan miki ba uban ki ma bai isa na fad'a ya fada ba balle ke y'ar k'aramar tsakuwa. naga alama baza kiji maganar a nutse ba sai an fad'a miki da yaren da talaka yafi ganewa wato duka. Ki samarwa kanki lafiya ki bar Asad in baso kike wani abun ya same ki ba."


Rauda tace, "babu abinda zai same ni sai abinda Allah ya nufa. Sannan babu wanda ya isa ya saka ni yin abinda banyi niya ba, in naga dama kuma zan iya cewa ina sonsa na aure shi kodan naga yadda zaki koma a lokacin."




A fusace Mama ta mik'e tace, "Kee! Kar ki sake hasashen wannan ranar a rayuwar ki domin baza tazo ba har abada. Ke wacece da zaki zama matar d'an sarki jikan sarki kuma sarkin gobe? Wacece ke? Banza kike, bak'a, mummuna, matsiyaciya, gurguwa mai tallan abinci a titi. Ke ko a mafarki akace zaki zama matar sa sai ki amince?."
Murmushin rainin hankali Rauda tayi tace, "Da alama sirikata kina wasa da ikon Allah kinga ta inda muka samu banbanci kenan ni nasan duk wahalar abu a wajan Allah mai sauk'i ne." ta fad'a tana kallon ta itama tana kallon ta.


Mum tace, "kul kar ki sake kiran ta da wnanan sunan bai dace a bakin mace irin ki ba, ki sani akwai matan da suka amsa sunan su mata sama da d'ari da suke son su furta wannan suna amma yafi k'arfin su." Rauda tace, "ba tsoron ta kar na amsawa Asad zan sa aure ba? To ina so ku sani da zarar lokacin da aka d'iba yayi zan tabbatarwa da mai martaba ina son Asad kuma zan aure shi kodan naga ya zakuyi a lokacin da Bak'a, mummuna, gurguwa, y'ar talaka, mai tallan abinci ta zama matar sarki Asad; kuma sirikar y'ar sarkin Kano babar sarkin jibi. Kunga sai ku d'auki bindiga ku harbe kan ku" ta fad'a tana kallon su one by one.


A fusace Mama tayi kanta zata mare ta Mum ta rik'e tana girgiza mata kai Mama a fusace tace, "matuk'ar kika aikata haka zakiyi dana sanin da baki tab'a yi ba tunda Allah ya kawo ki duniya. Zan iya sakawa a b'atar dake daga duniyar gabad'aya wannan ba komai bane a wajena matuk'ar zan samu abinda nake so. Sai na tabbatar baki tako k'ofar gidan sarauta ba balle ki kasance a matsayin da kika lissafa domin yafi k'arfin kaf dangin ki gabad'aya. Zan miki biyu babu, babu Asad babu sauran wanda suka zo taimakon ki su aure ki tunda abin naki rashin kunya ce" ta fad'a tana nuna ta da yatsa cikin murya mai amo da alama kamar wani abun ma bata san tana fad'a ba sabida b'acin rai.


Rauda ta tab'e baki tace, "Ina jira na gani sirika ta, in kuma nice naci wasan na shigo gidan matsayin sirikar ki nice nayi nasara bake ba." K'wafa tayi fuskar ta har ja tayi sabida b'acin ran da take ji a zuciyar ta wanda bata tab'a jin irin sa ba sukayi hanyar waje kafin Mama ta tsaya ta juyo ta kalli Umma da Anty Ummi tace, "Duk abinda ya samu y'ar ku kuyi kuka da kanku.." Rauda ta d'aga murya tace, "babu abinda zai same ni sai alkhairi. Kii gaida min mijina kinji sirika ta!." Juyowa tayi ta kalle ta Rauda tayi dariya kafin ta girgiza kai ta fita daga falon a fusace.


Kallon Rauda Umma tayi bayan sun fita cikin fad'a tace, "Wannan wanne irin rashin hankali kike aikatawa haka Rauda?. Ke kuma babbar banza mai biye mata ina yi mata magana kina tab'a ni wai na k'yale ta tana yiwa wacce ta haife ta rashin kunya, Ni in aka yi min haka zaku ji dad'i ne?. Matar sarki ce fa bamu yi mata komai ba ta saka anzo gida an ci mana mutunci ina ga kun fad'a mata wad'annan maganganun marasa dad'i...? Ba kaina nake ji ba ke nake ji Rauda zata iya yi miki komai dan ganin bayan ki." Yaya Ummi tace, "Umma ai ke baza ki aikata abinda ita tazo tayi mana har cikin gida ba bayan wanda ta saka akazo har gida aka ji miki ciwo, ai wallahi munyi mata da sauk'i ma irin ta'asar da tayi kamata yayi mu kamata mu rama irin abinda ta saka akayi miki. gani take kud'i shine komai zata iya juya mu tayi mana rashin mutuncin da taga dama bata san bata isa ba wallahi. Dan tana matar sarki baza muji tsoron ta ba tunda ita ta d'auko k'afa tazo har inda muke ko zane ta mukayi itace ta jawo."


Umma ta kalle su tace, "ya dai isa haka bana son tashin hankali da yiwa na gaba rashin kunya. Ku tuna a gidan d'anta muke ko a yanzu mun ci albarkacin ta dan ba bata haife shi ba damu zauna ba, da badan yazo inda muke ba da wataƙila yanzu bamu san a inda muke zaune ba. Kar na sake ganin kin yiwa wani haka koda nan gaba ne, wannan ba tarbiyya ce." Umma ta fad'a tana kallon Rauda kafin ta tashi ta shiga d'aki.




Yaya Ummi ta kalli Rauda tace, "Ke me kika yanke game da auren shi Asad d'in?." Rauda ta kalle ta tace, "Ban yanke komai bani domin bana ra'ayin auren sa gabad'aya. Ya cika rainin hankali da yawa bazan jure ba."
"Kuna tare da Anas har yanzu?."
"Tun dai ranar yazo har yace min bashi ya aiko mana da kayan abinci ba ban sake jinsa ko a waya ba gaskiya."
"Kuma baki neme shi ba?."


"Na kira shi jiya amma layin a kashe." Yaya Ummi tace, "inda nice ke Rauda da Asad d'in nan zan aura badan yafi Anas kud'i da mulki ba sai dan na nunawa uwar sa ba'a ja da ikon Allah, duk k'ask'ancin mu da take gani in Allah yace yes bata isa tace no ba duk abinda take ji dashi sai dai tayi ta gama ta d'auki jikan da zaki haifar mata. Gurguwa, bak'a mai tallan abinci da take rainawa ta zama mata ga d'an nata da take ji dashi sai naga uwar abinda zatayi." Rauda tayi murmushi tace, "Nima zan so hakan Yaya kodan naga yanayin da zata shiga a wannan lokacin, amma sam ni bana ra'ayin auren sa."
"Kiyi ra'ayin yanzu Rauda, kar ki manta tun ba yau ba kina yawan ce min kinyi mafarki da namiji mai rawani a kansa wataƙila Allah ne ya nuna miki auren sa tun a mafarki. sannan istikhara da kika yi Allah ya nuna miki a mafarki ko?."


Rauda tace, "Haka ne Yaya Ummi amma hakan ba yana nufin shi zan aura ba. Nifa bazan iya zama matar sa ba gaskiya in na aure shi nayi ya da k'iyayayar mahaifiyar sa?." Yaya Ummi ta dawo kusa da ita ta dafa ta tace, "Shi zaki aura Rauda, ki saka a ranki shine mijin ki da zarar an tambaye ki kice kin amince." Rauda ta kalli Yaya Ummi tace, "Nifa bana son sa ta yaya zan amince?."
"Sabida mu nunawa babar sa iyakar ta, mu nuna mata duk abinda kake ji dashi baka isa kaja da ikon Allah ba."
"Ni tsoron gidan sarauta nake fa Allah ya sani."
"Ki ajjiye tsoron ki saka a ranki a nan aka haife ki."
Rauda ta kalle ta da mamaki tace, "Yaya Ummi in na amince da Asad Anas fa? Nayi masa adalci kenan duk tarin d'awainiyar da yayi dani dan na samu wanda ya fishi na watsar dashi...?."






#Vote
#Comments
#Share.


*KWANTAN ƁAUNA*
Fitattubiyar 2023


©️ *Nana Haleema.*




*Book 1*
*025.*


Yaya Ummi tayi shiru alamun tunani kafin ta sauke numfashi ta kalli Rauda tace, "Tabbas Anas ba abin yarwa bane ba, in muka watsar da Anas bamuyi adalci ba." Rauda rausayar da kai tace, "Abinda na gani nima kenan, zan iya auren Anas na zauna dashi duk da bana jin sonsa a zuciya ta har gobe, amma halayyar sa da yadda yake nuna tsantsar so a gare ni zata saka naso shi nan gaba."


Yaya Ummi tace, "Haka ne Rauda, ki cigaba da addu'a kedai kawai duk abinda ya zama alkhairi Allah ya zab'a maki."
"Ina yi sosai." Yaya Ummi zatayi magana kenan aka bud'e k'ofar aka shigo Baba ne da kuma maza guda biyu a bayan sa ganin su waye ya saka Yaya Ummi tashi tsaye tana fad'in, "Sannun ku da zuwa."


D'aya daga cikin su yace, "Yauwa Ummi, ya mai gidan naki?." Yaya Ummi tace, "Alhamdulillah." Gaisawa sukayi har Rauda kana d'aya daga cikin su yace, "Jiya nazo wucewa ta k'ofar gidan ku na tarar an baje gidan gabad'aya ya koma fili ana sabon gini na bulo, daman kuma ina ta ji a gari ban tabbatar ba sai dana gani da ido na; sai yanzu mahaifin ku yake shaida min abinda yake faruwa."


Kawu Badamasi yace, "Ke daman kin san shi ne tun a baya har ya furta yana sonki?." Rauda ta girgiza kai tace, "A'a Kawu bansan shi ba." Ya girgiza kai yace, "ikon Allah kenan, abinda baka tsammaci faruwar sa ba sai kaga ya faru." Kawu Lawan yace, "To ke meye a ranki kenan?." Rauda tayi shiru bata amsa ba Baba yace, "ita bata yanke hukunci ba har yanzu; akwai wani yaro Anas da yake sonta yana hidima da ita sosai ina tunanin shine a ranta."


Kawu lawan yace, "ba d'an gidan Alhaji Tasi'u mai farin gida ba?." Baba yace, "Shi." Kawu lawan yace, "to ai ni Alhaji Tasi'un ya aika min da mutane guda biyu na d'auka ma ko neman auren ta suka zo wajena sai suke shaida min shine ya turo su yace a sanar damu ya yiwa d'ansa mata kar a jishi shiru kwana biyu zai masa aure ne. Sun shaida min bazasu iya had'a ido da kai ba sabida kunya shiyasa suka je wajena kai tsaye." Baba yace, "ikon Allah! Amma baka sanar dani ba."
"Na d'auka shi yaron ai ya sanar dakai ko ya sanar da ita."


Baba ya girgiza kai ransa fari karr har hakan ya bayyana a kan fuskar sa yace, "basu zo inda nake bama shiyasa kwana biyu shiru babu motsin yaron, Allah sarki ni shaida ne yana son Rauda amma da alama iyayen sa basa son alaqar su tare shiyasa suka yanke wannan hukuncin, Allah ya zab'a mafi alkhairi." Kawu Badamasi yace, "Amin. Baza muyi saurin cewa iyayen ne basa son alaqar ba wataƙila alqawarin aure ne sukayi zasu had'a shi yaron bai san dashi ba shiyasa yake neman Rauds. Rauda karki yiwa kanki dole dan ganin kud'i ko dukiya ko kuma sarauta, yanzu maganar Anas ta k'are kinji duk abinda yake faruwa da kunnen ki, kar kice tunda babu batun Anas yanzu bara na amince da d'an sarkin kar kiyi haka kiyi addu'a ki kuma bi zab'in zuciyar ki."


Kai ta girgiza alamun gamsuwa Baba yace, "Ai ana ta addu'a duk inda na bayar ayi mana istikhara sai kaji ance auren sa da ita alkhairi ne ba kad'an ba. Daman Anas d'in nan nake ji tunda abin yazo da haka wallahi nafi kowa farin ciki ya auri zab'in iyayen sa itama ta auri Asad d'in shikenan an huta." Kawu Badamasi yace, "A'a, ka barta ta zab'i abinda take so dan Allah kar abin duniya ya rufe mana idanu mu kaita inda zamu zo muna dama mun sani bamu kaita ba, dan ni Allah ya sani wani lokacin bana yi mata sha'awar shi yaron mai martaba sabida abinda zata tarar ba abu kad'a bane. Na farko da ga babar sa, na biyu ga sauran jama'ar gidan, na uku har abada gidan sarauta bazasu tab'a girmama ta ba k'ask'ance zata rayu dan su gidan sarauta indai ba y'ar gidan sarauta ka d'auko ba talaka sunan ka balle kuma Rauda."


Umma da take zaune tace, "tun a yanzu ya fara bayyana kansa dan mahaifiyar yaron bata jima da fita daga gidan nan ba tayi b'adda kama ta shigo tana yi mata gargad'! akan auren d'anta, har da ikirarin in ta aure shi sai ta b'atar da ita daga duniya, ina dalili d'an sarki ai ba d'an wani annabin bane da za'a so a aure shi. Kuma shi yaron ita dashi bai ma ce yana son ta balle yace zai aure ta, haka zasuyi zaman auren?." Kawu Lawan yace, "sai a bar maganar in mai martaban ya nemi jin ra'ayin ta ace bata amince ba ai ba dukan mu za'ayi ba."


Baba yace, "A'a bafa za'ayi haka ba zata amince ma in sha Allah, meyasa kuke haka ne ku? Alkhairi ya biyo mu kuna k'okarin saka mu guje masa?. Ni ina goyan bayan auren d'ari bisa d'ari kuma in sha Allah sai ta aure shi." Umma tayi murmushi tace, "Daman Malam ai baza ka k'i ba kai." Kawu Badamasi yace, "Muma bamu k'i ba muna fatan abinda yafi alkhairi Allah ya zab'a, in shine alkhairin Allah ya tabbatar da arzuk'i a gidan wasu ai gwara a gidan ku, kuma kowa yana so yaga nasa cikin jin dad'i da kwanciyar hankali, abin alfaharin mu ne gabad'aya ace Rauda ta auri d'an sarki dan kaf dangin mu ba'a tab'a ba sai a kanta. In kuma babu alkhairi Allah ya watsa lamarin waje duk kud'i ko mulki bazai saka mu kaita inda zamu zo muna dana sani ba."


Baba yace, "Da alkhairi ma in Allah ya amince." Shiru sukayi dukkan su kafin suyi sallama su wuce. Baya fitar su Yaya Ummi ta kalli Rauda tace, "to kinji yanzu babu batun maganar Anas sai ki dawo da hankalin ki kan Asad." Rauda ta murmusa tace, "Wallahi Yaya sai nake jin zuciyata tayi min nauyi da akace ya fasa aurena, ashe shiyasa ya kasa nema na a waya."


Umma tace, "Ni kaina zuciyata babu dad'i Rauda balle ke, Anas ya cancanci aso shi kodan soyayyar da ya nuna miki ashe Allah bai rubuta zai mallake ki matsayin matar sa ba, Allah sarki! Allah ya zab'a masa abinda yafi alkhairi ya basu zaman lafiya shida wacce aka zab'a masa." Rauda tayi shiru tana jin babu dad'i a zuciyar ta.




*☆☆*


Gudu yake sosai a motar yadda Mama ta kira shi a wayar tana kuka ta d'aga masa hankali sosai hakan ya saka yake gudu kamar zai tashi sama burin sa yaje yaji kiran da take masa. Ko gama faka motar baiyi ba ya fita da sauri zuwa wajan ta yana shiga falon farko bata nan ya shiga ciki ya tarar da ita ita da Mum a zaune sunyi jugum-jugum kamar an musu rasuwa. Hankalin sa tashe yace, "Mama lafiya?." Kallon sa tayi da jajayen idanun sa ta yafito shi da hannu ya k'arasa kusa da ita ya zauna ta rik'e hannun sa tace, "Asad dan Allah ka janye batun maganar auren yarinyar nan, bata da tarbiyya ko kad'an bata da kirki."


Juya idanun sa yayi ya rik'e hannun ta da yake cikin nasa yace, "meya faru?." Mum da take

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login