Showing 42001 words to 45000 words out of 96677 words
Chapter 15 - GOYON KAKA(1 to End) Complete Document Writing by Umma Yahya Musa.txt
a ruwan wankanki na daurayar karshe xakina sakawa in kin futo kuma saiki mulke jikinki da wannan ki barta ta bushe a jikinki,cikin jin dadi islam tace toh domin dama akwai son kanshi,mai gyaran jikin tace banda yawo a rana indai kinaso gyaran jikinki yafi haka kyau,in futarma ta xama dole to ki dinga saka katon hijab da nikaf,islam tace a'ah ba inda xani aidama hutu mukeyi,murmushi mai gyaran jikin tayi tace toh nixan tafi sai gobe islam tace Allah y kaimu aunty ki gaida gda,mai gyaran jiki tace gda xaiji.
A palo suka hadu da mommy tace hajiya mungama saikuma gobe,mommy tayi godiya tace Allah y kaimu,islam ce ta futo tace mommy ta y kika ganni,mommy tace masha Allah yata kinyi kyau kinji yadda kike kanshi,wani farr islam tayida ido tace kuma mommy har humrah masu kanshi ta bani tace nadinga shafawa inna futo a wanka harda sabulun wanka ma,mommy tace toh ki dinga boyewa kar Amira ta karar miki tunda itama in an gama miki xa'ayi mata,islam tace toh sannan tace mommy ta bani wasu Abu masu dadi nasha,mommy tayi murmushi tace toh ai suma dukkansu na gyara jikine,islam tace toh ta fice,mommy kuwa murmushi tayi don tasan duk daran dadewa dole Aslam yayi alfahari da auran islam don yarinya ce mai shiga rai.
Taku har kullum *sisin mama*
πππ
*mrs hamisu taura*
πππ
[11/17, 4:25 PM] βͺ+234 810 749 9249β¬: (17/11/2016 3:00pm) *na umma yahya musa*
ππππππ
ππππ
ππ
π
*GOYON KAKA*
*65*
Islam da gudu ta shiga part din kaka jikin Amira ta fada tana 6* y kika ganni,Amira ce tace hmmm wannan kanshin fa wani farr islam tayi da ido ta kashe daya hannunta Amira ta kama tana kallo tace 6* kinga irin kyawun da kikayi gashi sai wani sihirtaccen kamshi kikeyi wai menene sirrinne wata dariya islam ta kyalkyale da ita tace abin sirrine Amira ce tayi narai2 da idonta tace kai 6* bafama haka dake,islam tace mommy ce ta dauko mai gyaran jiki ta faramin shine gift dins tace na kokari danayi a skul,da sauri Amira ta mike tace bari naje wlh baxan yadda ba nima sai tasa anyimin,islam ce ta riko hannun Amira tace kefa banxa ce basaiki jira nagama fada miki ba mommy tace na 8 day xa'amin daganan sai a farayi miki cikin jin dadi Amira tace toh shikenan yanxu naji magana naxata sankai xa'amin islam ta mike tace bari nayi wanka ta shige bedroom dinsu.
Bayan ta futo a wanka ta mulke jikinta da humrah sannan ta xauna ta tsantsara makeup wani hadadden swiss lace blouse & skirt ta saka light pink an masa kwalliya da dark pink flowers sannan ga wasu stones da aka jera sai daukar idanu sukeyi ta daura dankwalinta das tamkar nadin gwagwgwaro tasaka fashion dan kunne da sarka silver tayi bala'in yin kyau tamkar wata dan daren 15,fitowa tayi daga bedroom dinsu.
Tun kafin ta karasa kamshin ta y isa palon,lokacin yaya haidar na palon kallanta suka tsayayi kaka,yaya haidar,Amira karasawa tayi ta hurawa haidar iska a ido danshi yafi kura mata ido harwani lashe baki takeyi,cikin shagwaba ta fara dire2 tana kai yaya haidar irin wannan kallo haka ai saikasa na kifa,murmushi yayi yace 6* kinga kyawun da kikayi ga wani mugun kanshi da kikeyi tun kafin ki karaso yayi mana sallama,dariya tayi ta koma jikin kaka ta lafe ta kalli kaka tace wai haka kaka,kaka tace eh nikam dabadan nasan ba inda kikaje ba danace wankan inji kikaje akayi miki saboda yadda kika canja lokaci daya,dariya islam ta kyalkyale ta kama kunnan kaka ta rada mata magana,kakama dariya ta kyalkyale da ita saboda tasan kwanan xancen,amma itama cikin kasa2 da murya tace mommy kuwa ta kyauta.
Haka kwanaki sukayi taja islam kuwa ta dage da xuwa part din mommy gyaran jiki wataran kafin mai gyaran jikin taxo islam ta dade a part din,mommy kuwa tayita mata dariya,kanshi kuwa y xauna ajikinta don indai ta xauna a guri to sai tabar kamshinta a gurin.
Aunty amarya ma ta dage tana gyara yarta,yauma dahuwar kaxa cikin yatsina islam tace nifa aunty amarya wai dan Allah menene wannan abubuwan da kullum saikin bani,naci na kifi da magani,naci na kwai da magani,yanxu kuma gana kaxa kina bani kumafa ni kadai ake bawa banda Amira nigaskiya nagaji dacin magungunannan,ta washe baki tace to dan gwara2 wannan xumarma tunda ita xakine da ita,harararta aunty amarya tayi tace banason surutun banxa kiyi maxa ki cinye ki tashi ki bani guri,xumbura baki islam tayi tana kunkuni buge bakin aunty amarya tayi kara islam ta kwallah tana wayyo nashiga 3 ta fasamin baki,mamakine y kama aunty amarya tace toh kiyi shiru kiji meyasa nake baki komai da magani,cak islam ta tsaida ihunta tamkar daukewar ruwan sama aunty amarya tace maganin bakine bakiga kina dadayin kyau ba ko kinaso bakin mutane y kamaki,murmushi islam tayi ta rungume aunty amarya tace shiyasa nake sonki aunty na,aunty amarya ma murmushi tayi a haka islam ta karashe cinye kaxar tanata xuba surutu ta tashi ta fice.
Akwati set 2 akayiwa islam kayan lefe daddy da Abba ne suka bawa su mommy kudi suka hado,kayan sunyi kyau sosai dan english wears ma akwati 4 aka cika 2 wadanda islam xata iya amfani dashi yanxu 2 kuma saita dada girma,boye set 1 akayi wanda y kasance na dai2 islam a yanxu aka mommy ta kirawo Aslam yaxo y gani,lokacin dayaxo ko bude akwatunan baiyi ba yace haba mommy wannan kayan ai sunyi yawa hakan ai asarar kudine,harara mommy ta dakawa Aslam cikin tsawa tace wannan akwatunanne sukayi yawa dududu fa guda 6 ne,ni tashi ka bani guri in baxaka kallah ba,jiki a sanyaye Aslam y mike a ranshi kuwa yana dadajin tsanar matar da xa'a aura masa dan tun tasowarsa mommy bata tabayi mai fada ba amma yau harda tsawa.
Taku har kullum *sisin mama*
πππ
*mrs hamisu taura*
πππ
[11/17, 4:26 PM] βͺ+234 810 749 9249β¬: (17/11/2016 3:30pm) *na umma yahya musa*
ππππππ
ππππ
ππ
π
*GOYON KAKA*
*66*
Islam ce kwance a daki saboda yanxu ta daina futa kwata2 rabonta da gdansu khausar ma yau kwana 5 wanda yayi dai2 da saura kwana 3 daurin auran ta.
Khausar ce suka shigo itada Amira kanta suka fada,Amira tace 6* Ashe bikin yaya Aslam xa"ayi cikin mamaki islam tace aure yaya Aslam din xaiyi,khausar tace eh yanxu mukaje mukaga kayan lefen da aka hadawa amaryar kingansu kuwa masu mugun kyau,dariya islam ta kyalkyale da ita tana ta dariyarta harta fado daga kan gado dakyar ta xaida dariyar tace tab ita kuwa wannan yarinyar data yadda xata auri hero wanne irin rashin rabone da ita a duniya,to in banda xabar mata ma ta biyo tarasa wanda xata aura sai wannan mugun tab ta tabe baki tace wlh dana santa da sainaje nabata shawara karta sake ta auri hero ta karasa maganar da kyalkyalewa da dariya.
Amira kuwa duk ranta y baci saboda rashin mutuncin da islam takewa Aslam yayi yawa,khausar ce tace nikuwa banga laifin yaya Aslam ba yana da kwarjini sannan ga kyau ga cikar xati,kece dai kawai kike ganin aibunsa kuma dan halinku baixo daya bane,Amira tace wlh fa fada mata dai ai nasan baxaki taba auran mijin dayakai yaya Aslam ba,harara islam ta watsa musu tace wlh karya kukeyi duk abinda kuka fada karya kukeyi yaya sagir yafi hero komai da kuka lussafo,dariya khausar ta tuntsire da ita tace wlh karya kikeyi kawai kin fadane don kiji dadin bakinki,cikin kufula islam ta xari hijabi har kasa tace ni kun tunamin mai sanyina ma bari naje nagansa ko xanji sanyi ta xura katon hijabinta ta fice.
A kofar gda tayi kicibis dasu yaya Aslam,yaya safwan,yaya amir cikin sanyin murya tace yaya amir ina wuninku shida safwanne suka amsa,Aslam kuwa tsawa y daka mata yace gdan ubanwa xakije kallon up & down ta jefeshi dashi duk da taga rama a tattare dashi ta murguda masa baki tace inda mutum y aikeni,cikin xafin nama yayi kanta ganin haka da tayi ta daga hijabin ta tace kafa mai naci ban bakiba ta falfala da gudu,dariya safwan y tuntsire da ita yace inason kallon drama dinku da islam,inaga rokon kaka xanyi tabawa amarya ita tayi mata xaman daki,amir kuwa murmushi yayi,Aslam kuwa harara y dakawa safwan yayi tsaki y shige cikin gda.
Islam kuwa saida ta shiga gdansu safwan ta tsaya garam ta tura kofar gate ta shiga gdan da sauri baba mai gadi y mike yana rarraba idanu saboda y fara gyangyadi,ganin irin xaburar da yayi shine yasaka islam kyalkyalewa da dariya tace haba baba irin wannan xaburar haka to ba wasu bane nice,shima dariya yayi yace au Ashe yatace tace eh ta gaidashi ta wuce part din sagir.
A palo ta tarar dashi y xurfafa cikin tuna I,sadaf2 ta karasa tayi clapping din hannunta firgigit y dawo daga tunanin daya tafi,y saki ajiyar xuciya dariya Islam tayi tace yaya tunanin me kakeyi,murmushi yayi yace tunaninki nakeyi my baby kwana 2 kin haramtawa idanuwana ganinki,kurr y tsura mata ido saboda wani mugun kyau data dadayi ga wani daddadan kamshi da takeyi tunda tashigo dakin y dume da kamshinta,hannu tasa ta rufe idanuwanta tace yaya wannan kallanfa janyota yayi y dorata a cinyarsa yana shinshina wuyanta cikin wata irin murya yace baby na wani mugun kyau naga kinyi ga wani daddadan kamshi da kikeyi nifa ina tsoron wani yamin snatching,murmushi tayi tace yaya ni takace har abada insha Allah,cikin jin dadi yace Allah yasa kallan cikin idanunta yayi yace nifa baby na da xa"a auramin ke yanxu so nakeyi,saina raineki harkiyi candy sannan mufara rayuwar aure,cikin jin kunya ta mike a kan cinyar tasa tace bari naje nagaida mammy daganan nawuce gda dama missing dinka nayi shiyasa naxo ganinka,cikin jin dadi y mike y riko hannunta yace muje naraka ki ki gaida mammy din daganan naraka ki gda,futa sukayi fuskar kowa dauke da farin ciki.
Sun shiga part din mammy hannunsu cikin na juna,islam ta gaida mammy sannan suka futa,tausayin sune y kama mammy saboda tasan ba karamin shakuwa sagir da islam sukayi ba saboda aunty amarya ta kirata tamata xancen aurar da islam da xa'ayi itadai tana musu addu'ar Allah y bawa yaran dangana,har kofar gda sagir y rakata ji sukeyi tamkar kada su rabuda juna a hakadai islam ta shige gda tana yiwa sagir bye2.
Su Aslam kuwa suna shiga gda tun kafin su karasa part dinsu aunty amarya ta kirashi tace yaxo tanason ganinshi,kallan su safwan yayi yace guys aunty na tana nemana y wuce part din aunty amarya.
Taku har kullum *sisin mama*
πππ
*mrs hamisu taura*
πππ
[11/18, 5:54 PM] π¬ππSalmaπ¬ππ: (18/11/2016 3:00pm) *na umma yahya musa*
ππππππ
ππππ
ππ
π
*GOYON KAKA*
*67*
Da sallama Aslam y shiga part din aunty amarya,kurr ta xuba masa ido saboda yadda taga yayi bala'in ramewa lokaci daya taji wani mugun tausayinsa y kamata,Aslam kuwa ganin irin kallon da aunty amarya takeyi masa shine y sakashi murmushin yake yace aunty na afuwa nake nema wlh abubuwa ne suka shamin kai shiyasa bakya ganina kwana 2,katse shi aunty amarya tayi cikin sanyin murya tace anya my son kanacin abinci kuwa kaga yadda ka rame kuwa gashi dukkayi baki,shafa kanshi yayi tabbas shi kanshi yasan rabon dayaci wani abincin kirki tunda akayi masa xancen aurannan tunaninsa kullum wacce irin yarinya xa'a aura masa.
Idanuwansa y dago da suka rune sukayi jajawur lokaci guda cikin sanyin murya yace aunty wlh kwata2 bana iyacin abinci saboda tashin hankalin da nake ciki,kullum tunanina bai wuce wacce irin yarinya xa'a auramin ba,xatayi dai2 da tsarina irin macen danakeso ce wlh aunty ni a tsarina yanxu haka nafison mace yar 25 lokacin nikuma ina 30 year kinga da hankalinta ba wata wauta da datamin muryarshi ce ta sarke sakamakon kukan dayaxo masa,kuka yakeyi sosai,lokaci daya jikin aunty amarya yayi sanyi tunawa da wacce irin yarinya xa'a aurawa Aslam a ranta tace dankari lallai wannan shi ake kira kwado in kuwa hakane sam2 islam bata dace da Aslam ba,dan duk tsarikan daya lissafo na macen dayakeso islam batada ko daya,karasawa tayi gurinsa ta daura kansa a cinyarta shafar gashinsa ta farayi tana fada masa maganganu masu dadi da taushi,tace ni yanxu shawarar da xan baka shine ka yadda da kaddara,domin aurannan yana cikin kaddararka kasani biyayya ga iyaye wajibi ne,domin Allah acikin alqur'aninsa yace (ku bautawa Allah shi kadai,sannan kuyi biyayya ga iyaye)to kaga ko anan y kamata ka gane iyaye sunada daraja tunda Allah y hada biyayyarsu da bautarshi,sannan ka kasance mai hakuri da kawaici duk yarinyar da iyayanka suka xaba maka basuna son cutar dakai bane a'ah gata sukeson yi maka,lokaci daya Aslam yaji duk wata damuwa da kunci dake ransa y tafi,aunty amarya tace alkawari 1 nakeso kayimin ko wacce irin mata aka aura maka baxaka taba xaluntar taba,wani doguwar ajiyar xuciya Aslam yaja saboda yadda nasihar aunty amarya ta ratsashi,yace insha Allah aunty na baxan taba cutarta ba xan xama mai hakuri da yafiya akan duk laifin da tamin,sannan xamuyi rayuwar aure irinta kowanne ma'aurata da sukayi auran soyayya,cikin jin dadi aunty amarya ta rungumoshi tace Allah yayi maka albarka,murmushi yayi yace ameen.
Aunty amarya da kanta ta tashi ta shiga kitchen ta xubo abinci a plate,da kanta ta xauna tayi feeding dinshi tana bashi lbrai masu dadi,cikin farin ciki yakecin abincin harya cinye baisan y cinye ba,bude baki yayi aunty amarya ta xura masa cokali,cikin mamaki yace ina abincin lakace masa hanci tayi tace ka cinye a tare suka tuntsire da dariya,aunty amarya tace ko a dado makane Aslam yace a'ah nakoshi,y lumshe ido yace aunty na ngd Allah y kara lfy da nisan kwana,murmushi aunty amarya tayi ta tsiyaya masa lemo exotic a glass cup ta mika masa tana ameen,Aslam yace gaskiya ne da akace wanda y rasa uwa yayi kuka domin shine babban maraya saboda nidai gashi nagani rabona danaci abinci spoon 3 harna manta dan ina faraci xanji yanamin daci,amma yau da uwata ta sakani a gaba gashi harna cinye cikin plate bansani ba,dariya aunty amarya tayi tace my son bakada dama wlh,dariya yayi shima y mike yace bari naje naji preparation din dasu safwan suka tsara saboda yau aunty na ta bani kwarin gwiwa y fice,murmushi aunty amarya tayi ta dauke try din data sako abinci takai kitchen.
Da farin cikinshi y shiga part dinsu xaune y tarar da safwan da amir shima xama yayi yana guys wanne shirye2 kuka tsara abikinnawa ne,cikin mamaki suke kallanshi tamkar ba Aslam ba mutumin da yakeyi musu masifa in suna hirar program din da xasu gudanar a bikin amma yau shida kansa yake tambayar su,Amir ne yace kawai mun shirya receiption bayan daurin aure shikenan tunda kace bakasan ayi duk wani Abu dan baxaka halarta ba,yace OK naji yanxu najanye duk wani kudiri na,after wedding fateeha akwai reception yes haka yayi,da misalin 4:00pm sai ayi kilisa a fadamin nawane kudin hayan dawakai,ranar asabar 2:00pm akwai parety da daddare kuma akwai dinner sai a nemo hall mai kyau,cikin jin dadi sukace gaskiya hakan yayi.
Taku har kullum *sisin mama*
πππ
*mrs hamisu taura*