Showing 3001 words to 6000 words out of 96677 words
Chapter 2 - GOYON KAKA(1 to End) Complete Document Writing by Umma Yahya Musa.txt
ππ
π
*GOYON* *KAKA*
*6*
Cikin ikon Allah kasuwancinsu y kara karfafa lokacin arxikinsu y kara bunkasa.
Fateema ma ta samu ciki kula khadija take bata ta musamman har cikinta y isa haihuwa ta haifi na miji aka saka masa sunan yayan Aliyu wayako Abdul qadeer (ameer)haka sukaci gaba da haihuwa inda aslam nada shekara 2 khadeeja ta khadeeja ta kara haihuwa ta haifi namiji aka saka masa Aliyu suke kiransa (Haidar).
Cikin ikon Allah khadeeja tana da yaya 5 duk maxa aslam,haidar,sadiq,khaleefa,usman.
Fateema kuma tana da yaya 3 itama duk maxa ameer,yusuf,khaleefa ,har yau basu samu mace ba burin yaran gidannan y ta'allaka akan su samu kanwa sannan suna girmama tsakaninsu,cikin ikon Allah fateema ta samu ciki yana da wata 2 khadeeja ma ta samu duk ilahirin yarannan addu'a sukeyi Allah yasa babanninsu su haifa musu yan mata.
Cikin ikon Allah fateema ta tashi da nakuda aka kaita asibiti bata dauki lokaci ba ta haifo xankadediyar yarinyar ta mai kamata babanta sak sai dai kawai hasken mamarta ta dauko,murna kuwa gurin iyalan gdan ba'a cewa komai.
Ranar suna aka sakawa yarinya Aysha aslam yace (Islam) xa'a na cemata tun daga lokacin rainon islam y dawo daga makaranta y dauketa ba wanda y isa y karbrta babban abinda yake sakawa aslam y kai islam gurin mamanta shine kuka in tana kuka batasan lallashi ba shine yake hadasu fada,tun lokacin da aka haifi islam kaka ta roki alfarmar tanaso Aliyu y bata ita inta isa yaye tun daga lokacin y amince yaxo y fadawa fateema itama tace ba komai tunda y yarda godiya yayi mata sosai.
Islam nada wata 2 mommy ta haihu itama mace ta haifa aka saka mata zainab sunan maman mommy amer yace shima ameera xa'a saka mata haka kuwa sukece mata ameera akwai hakuri dan in amer y daukota sai aslam yaje y dauko islam amma shi sai y mayar da ita saboda kuka yayita jin haushi kuwa.
Kwanci tashi babu wuya su islam sunyi 2 years a lokacin aslam nada 14 years dan yana j.s 3 wata rana y dawo daga makaranta yaxo y tarar an dauki islam an kaita gwarxo ranar wuni yayi yana kuka ko abinci bai ciba ranar.
Islam acan ma kuka take tanata gwarancin neman yaya dakyar kaka ta lallabeta tayi bacci,satin islam 2 ta ware shikuwa aslam ganin da iyayenshi sukayi damuwa tayi masa yawa yasa suka tattara shi suka mayar dashi boarding skul y koma s.s 1 tun daga nan rayuwa taci gaba da tafiya.
Wani hutu y dawo da murnarshi ya shirya y tafi gwarxo amma lokacin da yaje y tarar islam tanata birgima tana ihu duk ta watsar da abincin tsawa y daka mata tundaga lokacin ta fara tsoronsa harya dawo bata yadda y dauketa inya dauketa kuwa tadinga ihu kenan har saiya sauketa.
πππ
*daga* *sisin* *mama*
πππ
[11/12, 8:53 PM] βͺ+234 703 443 5155β¬: (4/10/2016 2:00pm)na umma yahya musa
ππππππ
ππππ
ππ
π
*GOYON* *KAKA*
*7*
Tun daga lokacin y daina daukarta in tayi laifi shine yake tsawata mata tsoronsa takeji sosai,har y tafi tana fara fitina in kaka tace ga aslam nan yanxu xata nutsu.
Aunty amarya ta kara haihuwar ihsan da tasleem ita kuwa mommy daga kan ameera haihuwar ta tsaya,su islam duk sunxo suna yanxu haka rabon islam da cikin kano tun haihuwar tasleem yanxu da take shekara 3 wannanne dalilin dayasa islam dawowa hannun kaka,yanxu islam tana makaranta a garin gwarxo tana aji 2 amma asha ruwan tsuntsaye takeyi yau taje gobe taki xuwa,sannan duk ranar da raje sai ta nemo magana bata kyale kowa ba daga malaman har daliban kaka kuwa daure mata gindin rashin mutunci takeyi duk laifin da islam tayi in akaxo aka fada mata sai ta bugi kirji tace bata aikata ba,makaranta ma tana xuwa allo dan an korosu itada kawarta hanne daga islamiyya ance basa fahimtar komai sai neman fada duk randa akayi hadda in basu iya ba aka dakesu indai yaro yayi musu dariya to dukan da xasu masa sai yafi wanda malami xai musu shine shugaban makarantar yace y gaji y mayar dasu gda,kaka da aka fada mata cewa tayi tafi nono fari dama me suke koyawa yara in banda xalunci kullum cikin dukan islam sukeyi tayi xamanta ta kaita makarantar allo wannan kenan.
*cigaban* *labari*
Islam tana futa bata xarce ko indaba sai gidansu hanne da guntun hawayenta hanne najin sallamarta ta futo da gudu tana waya dakeki islam bakinta ta cuna gaba tace ba wancan mugun yaya aslam din bane y rangwasheni hanne tace Allah y saka miki islam tace ai wlh dabadan yau xai tafi ba da saina rama dariya hanne tayi tace da munyi masa irinta uncle idris itama dariya islam tayi tace kuma shi da wlh a ruwan wanka xan xuba masa karara dariya sukayi gaba dayansu babar hanne tace Allah y shiryaku gidansu ilah da yusufa avokabansu suka je suka biya musu suka tafi kogi dayake yau ana kamun kifi kowa da fatsarshi a hannu.
Aslam kuwa tasha yaje y shiga mota ana kiran sallar magriba y isa gda direct part dinsu na samari y shiga dakine gado daya sai wardrop sai bathroom aciki wannan nasune shida ameer wanka yayi y futo y tafi masallaci sai da akayi sallar isha'i sannan y dawo direct cikin gda y shiga yaje y gaida maman sa take cemishi yau kwananka 3 fa harka dawo kai da kace sati xakayi a lokacin Abbansa da daddy (aliyu)suka shigo bayan y gaishesu yace wlh mommy dawowa nayi saboda kwata-kwata islam bataji gashi duk abinda takeso shi takeyi kaka bata tsawata mata anan y basu lbrn duk abinda y faru sannan,ran Abba y baci sosai yace dama inaso nasamu dama muje mu taho dasu gaba daya y kalli aslam yace karka damu insha Allah xasu dawo very soon aslam cikin farin ciki yace Allah y yarda,ya tashi yace xashi gurin aunty amarya su kuma suka xauna suna tattauna yadda xasu shawo hankalin kaka ta yadda ta biyosu.
πππ
*daga* *sisin* *mama*
πππ
[11/12, 8:54 PM] βͺ+234 703 443 5155β¬: (5/10/2016 2:30pm)na umma yahya musa
ππππππ
ππππ
ππ
π
*GOYON* *KAKA*
*8*
Da farin cikin shi y shiga part din aunty amarya a xaune y taradda ita ita dasu taslem y karasa y xauna a gefenta dora kanshi yayi akan cinyar aunty amarya,yace aunty na nayi missing dinki ina wuni,tace lfy my son i miss u too yayi dariya,kallan su taslem yayi y hararesu yace baku iya gaisuwa ba cikin rawar murya sukace ina wuni yaya lfy kawai yace,yace dallah can ku tashi ku bamu guri kun tsareni da ido naxoyin magana da aunty na da gudu ihsan ta tashi taslem kuwa kafadarta ta make dariya yayi yace kai aunty wlh yarinyar nan rashin jinta daya da islam itama dariya tayi tacewa taslem taho autata wlh wannan tafi islam jin magana yace aini xan baki lbrn rashin jinta yanxu fa ita ta koroni daga gwarxo ga kaka ta daure mata gindin rashin mutunci komai tayi daidai ne,shiru aunty amarya tayi tace to y xamuyi sai dai mu dinga binta da addu'a.
Aslam yace au ashe fa albishir naxo yi miki ai nasamo solution very soon islam xata dawo,murmushi ne y subucewa aunty amarya tace Allah yasa my son yace ameen y dade suna hira sai wajen 10:00pm yayi mata sallama y tafi part dinsu.
Islam baxaki tashi ba 7:30am fa tayi ko so kikeyi ki makara,kaka ce take tashin islam daga baccin safe saboda ta tafi makaranta,juyi tayi ta cuno karamin bakinta gaba tace wlh ni kaka baccinnan bai isheni ba,kaka tace ashe bakyaso ki xama mai lbrai a gidan radio ko da sauri islam ta mike dan dalilin dayasa take xuwa makaranta saboda tanaso taxama yar jarida shine babban burinta,amma da tuni ta daina xuwa wanka ta cire kayanta ta shiga,baccinta taci gaba dayi a toilet kaka ganin islam ta bata 15 minute bata futo ba shine yasaka ta bita a xaune ta tarar da ita akan kujera tana bacci tsaki kaka tayi tace wlh islam kedai anyi yarinyar banxa ta karasa ta sheka mata ruwa firgigit islam ta farka ihu ta kwala tana kururuwa kaka tace yimin shiru wlh yau in angle idris yayi miki dukan latti ba inda xanje,dariya naga islam ta tuntsire a raina nace mai kuka yana dariya,tace ba angle idris ba uncle idris ake cewa tsaki kaka tayi tace xancen banxa ai nayi kokari ma,amma menene tsakanina da yaran bokoko a wuta a haka kaka ta gamawa islam wankan suna fada.
πππ
*daga* *sisin* *mama*
πππ
[11/12, 8:54 PM] βͺ+234 703 443 5155β¬: (5/10/2016 3:00pm)na umma yahya musa
ππππππ
ππππ
ππ
π
*GOYON* *KAKA*
*9*
Sun fito daga toilet hanne dasu yusufa suka biyowa hanne mai ta shafa ta xauna sukaci abinci,ilah yace wlh wannan taliyar irinta gurin mai shayi dadinta y baci yusufa yace sosaima hanne kuwa lokacin da takai loma tace ai wlh saboda ita bana taba yadda nayi fada da islam,dariya islam tayi tace ba sunanta taliyar gurin mai shayi ba sunanta indomie ta karkatar da baki tace wannan mugun yayan nawa ne y kawomin ita dasu madara harsa biscuit da choculate wai na xuwa makaranta murmushi hanne tayi tace gaskiya y kyauta sai wajen 8:30am suka gama ci dan sunayi suna hira kaka harta gaji da magana islam ta shiga daki ta daukowa kowa chocolate da biscuit kaka kuma ta basu 20 naira sababbi sannan suka tafi.
A hanya hanne tace islam mu biya gonar malam tanimu islam tace a'ah ki bari mu dawo tukun tinda kinga munyi latti kar a dakemu nikuwa nace latti na yaushe basu suka karasa makaranta ba sai 9:00am dudu du tafiyar batafi ta 10 minute ba amma suka dinga canta sai data kaisu 30 minute islam tace yanxu muje mu haura ta katanga dan wlh baba mai gadi ko muna yawo da uwayen mu baxai barmu mu shiga ba yusufa yace haka xa'ayi daraf naga suna kama katanga sai ka rantse da Allah yan biraye ne sai da suka gama durawa Ashe wani fripect y gansu kuma dokar makarantar ce an hana shigowa ta Katanga.
Y kamasu sai office din head master akayiwa kowa bulala 5 masu xafi suka dinga kuka sannan aka sakasu neal down sai da sukayi na 30 minute sannan akace su tafi class aikuwa su islam sunsha takaici saboda basu samu sun siyi komai ba a break gashi an buga bell kowa y koma class.
Nan ma suna xuwa sabon mass teacher dinsu y shigo gashi ranar friday y bayar da assighment cikinsu ba wanda yayi nan y kuma futar dasu y sasu kamun kunne ranar dai su islam sunce da kafar hagu sukaxo makaranta nikuwa nace rashin jinsuπ.
Gonar malam tanimu suka wuce sai da suka tsinko mangwaro 1 yahau kai islam tace ainice boss dan haka nixan dauka nan fa dambe y sarkesu har malam tanimu yaxo y kamesu yace gurin mai gari xai kaisu suka dinga bashi hakuri yace wlh sai y kaisu mai gari y musu tsakani.
πππ
*daga* *sisin* *mama*
πππ
[11/12, 8:54 PM] βͺ+234 703 443 5155β¬: (6/10/2016 2:00pm)na umma yahya musa
ππππππ
ππππ
ππ
π
*GOYON* *KAKA*
*10*
Mummy da aunty amarya suka futo suna Allah y kiyaye y tsare hanya Allah y doraku akan hajiya ta yadda ta biyoku sukace ameen suka shiga mota Aslam ne yake driving inda daddy da Abba suke a seat din baya,Aslam driving yakeyi cikin nitsuwa har suka karasa gwarxo parking yayi a kofar gidan kaka suka futa y rufe motar suka shiga ciki.
Shiga sukayi bayan sun gaggaisa da kaka ta kawo musu ruwa da lemo kallon aslam tayi tace baka tafi koyon aikin sojan ba ai naxata wannan satin ka tafi yace a'ah sai wani watan xan tafi,Aslam yace kaka ina aljanar jijarki ne hararararsa tayi tace ban sani ba murmushi daddy yayi yace aslam islam dince aljana yace ai wlh daddy tafi aljana yanxu muna xaune ma kila a kawo kararta,kaka tace to makaranta ta tafi aslam yace Allah yasa.
Sallama sukaji anayi aslam ne y tashi yaje y gano dan aikene daga fadar mai gari ana neman kaka aslam yace toh gatanan xuwa y koma y fadawa kaka aiken da a kayo gurinta mayafi ta saba Abba yace haba hajiya ki tsaya mu muje mana kaka tace a'ah dole na amsa kiran mai gari ai kudaixo muje dayake ba nisa a kafa sukaje.
Su islam suka gani sunata kuka suna sun daina baxasu kara ba iyayen su hanne ma sunxo cikin tashin hankali kaka take tambayar meyake faruwa,su Abba kuwa guri suka samu suka xaxzauna suka gaishe da mai gari,suka tambayi dalilin kiran mahaifiyarsu anan mai gari y fadawa su Abba irin ta'asar da islam da abokananta sukeyi masa a gari sannan da karar da malam tanimu y kawo anan yaja hankalin iyayen sauran yaran daya xama dole su tsawatar da yayansu in ba haka ba kuwa xai dauki kwakwkwaran mataki,sannan yace kowa y tafi da yaranshi sukayi godiya kowa y kama danshi y tafi gda.
Tun a hanya kaka take sababin masifa akan an tsanar mata jika,anan su daddy suka dinga bata hakuri Abba yace yanxu kawai hajiya ki yadda ki biyomu mu tafi kinga acan ba ruwan wani da wani,islam tace eh kaka mu tafi birni dama wlh nagaji da yadda ake sakamin ido,kaka tace toh shikenan muje mu tattara kayanmu farin ciki sosai ne y kama aslam saboda yanaji y kusa gyara islam.
Nikuwa nace anya kuwa mudaije xuwa yanxu lbrn y fara ku biyoni danci gaban lbrnπ.
πππ
*daga* *sisin* *mama*
πππ
[11/12, 8:54 PM] βͺ+234 703 443 5155β¬: (7/10/2016 2:30pm)na umma yahya musa
ππππππ
ππππ
ππ
π
*GOYON* *KAKA*