Showing 6001 words to 9000 words out of 78990 words

Chapter 3 - YAR KISHIYA BOOK COMPLETE BY Zee MD.txt

Zee MD   

19 Feb 2025

3671

wayar tare dayin jifa da ita kan gado tana rik'e kai .......


Minty Goma na cika sai ga Diyana a gidan su Sanam tamkar Aljana , tana zuwa Sanam tafara bata labarin tun daga farkon Abinda Huneed yayi mata har izuwa yau d'in nan daya kafa mata wannan sharud'an , Diyana tace " inason sanin sunansa dakuma Number gidan su , Sanam tace " Sunansa Wai Huneed Abdallah number gidan su kuma wallahi bansan taba , sai dai inaganin in kika rik'e iya sunan ma yayi zaki samo min komai nasa , Diyana tace kibani 50 min. Zanfita induba miki cikin Estate d'in nan naku harda wajen sa , Sanam tace " hakan yayi dan sonake nayi shiri sosai akansa dan bazan k'yalesa ba tunda ya tab'oni , Diyana tuni ta mik'e dan fita nemo labari akan Huneed.......




Diyana na fitowa tafara duba cikin Estate d'in , duk k'ofar gidan dataga da megadi sai taje ta tambayesa ko yasan Wani Huneed Abdallah , sai da taje gidaje wajen guda hud'u kowanne yana baisan shiba , tana shirin buga gida na biyar sukayi karo da Hisham yafito daga k'ofar gate d'in gidansu , yana ganinta suka dubi juna Diyana tasakar masa wani shu'umin murmushi , k'arasowa tayi tana wani yauk'i sannan ta dubesa tace " dan Allah tambaya nakeyi ko Allah zaisa nadace ? Hisham yace " yi tambayarki ko Allah zaisa nasani , Diyana tace " ina neman wani Guy ne me suna Huneed Abdallah , dubanta Hisham yayi sosai sannan yace " Saurayin kine Kenan ? murmushi Diyana tayi sannan tace " ko d'aya wlh saurayin k'awatane shine ta aikoni gunsa kuma ni bansan gidan suba , nadai san a cikin Estate d'in yake shiyasa nake cigitashi ko Allah zaisa nagansa , Hisham yayi murmushi yace " ni ma bak'one a nan Unguwar sai dai kibari anjima zansamu me gadin gate d'in Estate d'in gaba d'aya na tambayesa ko zai san shi , Diyan cike dajin dad'i tace " yauwa nagode sosai kaga ka hutar dani , yanzu bari nabaka Number na inkasamu Labarin inda yake saika kirani , tuni Diyana tabawa Hisham number ta , dan ita kam tana ganinsa taji ya burgeta dan guy d'in yahad'u sosai , nan sukayi salama ta wuce tatafi Abinta , Hisham na tsaye har saida yaga b'acewar ta sannan ya juya yashiga gida.......


Diyana na dawowa tabawa Sanam labari duk yadda sukayi da Hisham , sai dai kwata kwata ta manata bata amshi number sa ba itace tabashi tata , gashi ko Sunan sa bata sani ba , dan haka suka zauna suna jiran kiran wayar Hisham ........


Koda Hisham ya shigo cikin gida tuni yakira Huneed , yana d'agawa ya sheda masa anzo nemansa kuma budurwa ce wai k'awar tace ta turota , Huneed yayi murmushi yace " kai me kake tunani akan haka ? Hisham yace " nidai bankawo komai ba nayi tunanin kodai ita wacce tazo nemanka d'in itace take sonka ? Murmushi Huneed yakumayi sannan yace " aikota akayi amman ba itace ba , kuma Bera ce ta saka ta tayi bincike akaina dan haka kabasu duk Abinda suke buk'ata indai basu wuce gona da iri ba , sai munsake waya kit yakashe wayar yabar Hisham rik'e da waya baki asake , yana bala'in mamakin Huneed da wannan halin nasa , tabbas zai iya cewa Huneed d'in d'an baiwane sosai acikin mutane.......




*Bana ganin Comment*πŸ€•


*Zantafi yajin aiki*
[9/26, 21:04] Muhammad Karim: *'YAR* *KISHIYA*
_Rik'on_ _Me_ _Hak'uri_
πŸ€¦πŸ»β€β™€οΈπŸ€¦πŸ»β€β™€οΈ




*NA*
*Zee* *MD*






*Hamdala* *Writer's* *Association* πŸ’ͺ
https://www.facebook.com/111403834371046


✨✨ *{{* *H.W.A* *}}*✨✨



*Bisimillahir* *Rahamanir* *Rahim*






Chapter 5.


Har aka kira Magriba Sanam da Diyana basu ga kiran Hisham ba , k'arshe dai Diyana tayiwa Sanam sallama akan gobe zata dawo lallai sai ta nemo mata labarinsa......


Sanam sosai takeson sake ganin Huneed , dan ita komai nasa ya tsaya mata aranta , tabbas bata tab'a ganin mutum da bashi da tsoro ko kad'an ba irinsa , dan haka tanaso ko sau d'ayane ta bashi tsoro ta kuma nuna masa wacece ita......


Duk wani motsi na Sanam tuni Huneed yasa asaka masa ido akanta , dan haka ma yasan shirin su akan sanin waye shi ita da Diyana..


Washe gari Hisham ya kira wayar Diyana yace mata inta shirya a inah zasu had'u yabata labarin Huneed d'in , aikuwa tamkar anyi mata albishir da gidan Aljannah haka takira Sanam ta sheda mata , Sanam tace " kawai ki kawosa gidan mu cikin Garden sai muzauna anan yagaya mana , da wannan shawarar Diyana ta kira Hisham ta fad'a masa inda takeso su had'u , nan suka tsaida lokaci sannan sukayi sallama.......


Tuni Diyana ta iso gidan su Sanam dan bataso yazo bai sameta ba , suna zaune suna hira saiga kiran wayar Hisham akan ya k'araso , sawa sukayi aka shigo dashi tare da kai masa kayan motsa baki , yafi minty 10 dazama sannan yagansu sunjero sun taho suna hira abinsu , suna zuwa suka gaisa da Diyana , ita kuwa gogar sai wani shan k'amshi take ita ala dole tanajin kanta , Hisham ya dubeta yace " barka da hutawa Hajjaju dafatan kina lafiya , ata k'aice ta amsa masa da cewa lafiya , daga haka taja kujera ta zauna tare d fara danna wayar ta tamkar batasan damutane a wajen ba , murmushi Hisham yayi cikin zuciyar sa yana fad'in " tabbas wannan yarinyar bamai saita ki sai Yaya Huneed shine zai iya saita ki , a fili kuwa yace " to Malama Diyana nasamo miki labarin Wannan guy d'in da kika sani , Diyana tace " ina godiya sosai dan haka ina sauraren ka ......


Da farko dai Sunan sa Huneed Abdallah Ma'aji , Haifaffen garin Borno state ne acan yayi karatunsa tunda ga matakin primary har yakai ga kammala Digree d'insa , Mahaifinsa ya kasance Babban Soja a Barrack d'in Borno , su biyu iyayensu suka haifa dagashi sai d'an uwansa , Mahaifinsa Canal Abdallah Ma'aji yarasu a wajen wani yak'i da akayi lokacin a garin Barno , tunda nan Huneed yayi shirin maye gurbin Mahaifinsa , tashi farko dayatafi training yadawo da babban resure akan and'aukesa aikin soja , kuma yafito da babban matsayi yanzu haka Shima babban Canal ne , aiki ne yadawo dasu Abuja shiyasa yataho da Mahaifiyar sa dakuma d'an uwan sa , Huneed mutum ne me rik'o da Addini gashi da son zumumci , sai dai Akwai abubuwan da baya shiri dasu sune baya shiri da mutum me girman kai , baya shiri da mutum me wulak'anta Al'uma , sannan bayason mutumin da girmama na gaba dashi , miskili ne sosai inkinga dariyar sa to yana cikin 'yan uwansa ko kuma yana tare da mahaifiyar sa , bayason yawan tambaya ko kuma a dunga yi masa dariya , hakan na harzuk'asa sosai kuma yana son wasa da k'ananan yara , a b'angaren cima kuma mutum ne me son tuwon biski miyar taushe , yana son saka kaya k'ananu sannan duk Juma'a yana saka jallabiya , yanason k'amshi sosai yana shiri da dukkan mutum me tsafta da kuma k'amshi , wannan shine cikakken labarin Huneed Abdallah Ma'aji , sai dai kuma abinda ba'a rasa ba wanda bansani ba .....


Ajiyar Zuciya Diyana tayi tare da cewa " mungode sosai Hisham , Sanam tuni ta mik'e tabar wajen tamkar batasan da wasu mutane ba abinta , binta Hisham yayi da kallo yana fad'in tabbas akwai babban aiki atare da Yaya Huneed , Diyana ta dubesa tace " magana kakeyine ? yayi sauri ya mik'e yace " ni zan zo na wuce dan nasan lokacin da Hajiyar mu zata sha magani yayi , nan sukayi sallama da Diyana ya wuce yatafi abinsa ........




*Kuyi maneji*






*'Yar* *Mutan* *Kanawa* _Ce_ 🌹😍
[9/27, 09:37] Muhammad Karim: [9/26, 21:04] Muhammad Karim: *'YAR* *KISHIYA*
_Rik'on_ _Me_ _Hak'uri_
πŸ€¦πŸ»β€β™€οΈπŸ€¦πŸ»β€β™€οΈ




*NA*
*Zee* *MD*






*Hamdala* *Writer's* *Association* πŸ’ͺ
https://www.facebook.com/111403834371046


✨✨ *{{* *H.W.A* *}}* ✨✨




*Bisimillahir* *Rahamanir* *Rahim*






Chapter 6.


Diyana na shiga cikin gida tasamu Sanam a falor tana zagaye , tana ganin Diyana tace " tabbas dole asameshi da wannan halin ashe soja ne , to tabbas saina janyo masa ansallameshi daga wajen aikin dayake tak'ama dashi , tunda harya shigo rayuwata sai yagane bashi da wayo , nagode Diyana nasa miki dubu d'ari biyar a account d'inki kasha ice cream , tana gama fad'ar haka ta haye sama abinta , Diyana cike da murna ta fice abinta tana murnar samun kud'i........


Tundaga nan Sanam tayi sercing d'in Huneed a Social media , duk wani posting d'in dayayi sai data bi ta duba , tab'e baki tayi cikin Zuciyar ta tana yaba kyan halittar Huneed , samun kanta tayi da kafe shi da ido tana kallo saita ke ganin tamkar murmushi yakeyi mata , Wurgi tayi da wayar sannan a hankali ta furta Huneed zakasan nice nashiga rayuwar ka bakaine kashiga tawa ba....


Washe gari tuni motar Sanam data canza ta iso , nan tasha wanka tashiga tafara zagaya gari , ranar gudun datakeyi ya wuce ko wanne irin gudu datake , duk inda tayi saikaga kowa na neman hanyar tsira da ransa , a haka ta k'araso gidan su Diyana dan nuna mata motar ta , tana shigowa lokacin Diyana na fitowa daga cikin gidan su , sakin baki Diyana tayi tana kallon had'uwar motar da Sanam ke ciki , cikin ranta tace " arzik'i yayi arayuwa , Allah yabamu rabon mu mu inba dan muna shiri da Sanam ba banga dalilin da zai hanani auran Daddyn taba , dai dai lokacin Sanam ta fito cikin wasu d'amammun riga da wando tana sanye da glass a idonta , mukullin motar ta na hannunta sai karka d'ashi take tana taunar cingum , da gudu Diyana ta k'araso tana fad'in " wow congrat my k'awa kice motar ta iso , Sanam tayi murmushi tana duban Diyana tace " Zahra meyin gasa dani to wlh wannan motar ko Babanta baitab'a hawan irinta ba , Diyana tace " wace ita taja da me *'Yar kishiya rik'on me hak'uri* ai duk kud'in Baban ta bai isa ya siyamata irin wannan ba , Sanam tace "kinshirya hawan ta ko ba yau ba ? da Sauri Diyana ta zagaya tana fad'in " wanne ba yauba yanzu ma haka dama ice cream zani sha , nan Sanam ta shiga taja motar dawani mugun gudu.......


Alhaji Abba yana zaune a falor sa yana cike wasu takaddu , Hajiya Maimuna ta sakko daga sama tana zabga k'amshi tamkar sabuwar Amarya , tana k'arasowa tace " sannu da aiki My Husbee , murmushi Alhaji Abba yayi yana duban Hajiya Maimuna yace " yauwa tauraruwar mata , samun waje tayi ta zauna tana duban sa sannan tace " inason magana dakai amman ina fatan kayimin kyakkyawar fahimta , Alhaji Abba yace " ina sauraranki ki fad'i duk abinda kikeson fad'a , Hajiya Maimuna tace " inaso dan Allah ka nemawa Sanam makarantar islamiyya kasata a ciki , yadda take tafiyar da rayuwar ta yakamata ace tana da ilimin addini ko Allah zaisa ta rage wasu abubuwan , Alhaji Abba yayi shuru yana nazarin maganganun Hajiya Maimuna , can ya nisa yace " kinsan a yanzu My Baby ta girmi zuwa makarantar islamiya , sai dai zanyi magana da ita muji yadda zatace , inta amince sai asamar mata akaita , dan kinsan tunda tadawo daga k'asar turkey tace hutu take buk'ata , amman zanyi mata magana duk yadda tace haka za'ayi , dubansa Hajiya Maimuna tayi sannan tace " Haba Husbee taya zakace sai yadda tace haka zakayi wai kaine ka haifi Sanam ko kuma itace ta haifeka ? Murmushi Alhaji Abba yayi sannan yace " bazaki gane irin son danakeyi wa Sanam ba , karki manta itace kad'ai 'Yar danake da ita a duk duniya sai kuma abinda yake cikinki , kinga kuwa wanda yake ciki bani da tabbacin samunsa ita kuwa tana doron duniya dole insota fiye da komai , Hajiya Maimuna tace " ban hanaka kaso Sanam ba amman inaso kasani yakamata kasan cewa ita fa mace ce kuma gidan wani zataje , mutuk'ar tana tafiyar da halayyar ta yadda takeso to tabbas bazata iya zaman aure ba , da sauri Alhaji Abba yadubi Hajiya Maimuna yace " dole saitayi auren ? inaso kisani mutuk'ar mijin da Sanam zata aura bazai k'yaleta tayi yadda takeso ba to wallahi sai dai ta zauna haka dan bana son ace antakurawa Rayuwa ta , wallahi Maimuna badan kece kika tsugunna kika haifi Sanam ba to wallahi zance kinq kishi da ita , kuma da yanzu kindad'e da barmin gida , wani tsaki yaja tare da d'ebe takardunsa dukansu ya nufi sama......


Hajiya Maimuna binsa tayi da kallo tana mamakin irin halin Alhajin , kwata kwata indai akan Sanam ne bashi da mutunci , zai iya rabuwa da kowa akanta ita kanta tasheda , saboda Sanam yarabu da ' Yan uwansa da dama a hankali ta furta Allah kasa sugane shi da 'yar tasa.......




Sanam da Diyana sunshiga gari sai faman wasa suke da motar , duk inda suka wuce sai anyi Allah wadai dasu , gidan su Zahra suka nufo dan nuna mata motar , lokacin Zahra na zance da saurayin ta Najeeb , ji sukayi anayin wani shegen hon. Me gigita mutane , da gudu megadi ya bud'e gate d'in aikuwa Sanam ta figo motar a guje tashigo cikin gidan , Zahra da Najeeb tuni suka mik'e tsaye ganin yadda aka shigo da motar da gudu tamkar za'a yo kansu , bin motar Zahra tayi da kallo dan tasan bata tab'a ganinta ba , kuma sannan Daddyn ta yana gida bare tace shine yayi sabuwar motar , kid'an dataji yana tashi tamkar anje club yasa tagane Sanam ce aciki , tuni taji ranta yayi mugun b'aci , bata gama tunani ba taga anbud'e murfin motar Sanam ce ta fito tana taunar cingum tamkar wata karuwa , d'aya gefe kuma Diyana nace tafito itama , dukansu bawacce tayi shigar mutunci ko wacce surar ta a bayyane take , wani kishine ya ziyarci Zahra dan tasan halin Najeeb sarai da son mata , musamman had'add'un mata irin su Sanam , Diyana ce tace " barka da hutawa Zahra dafatan munsameku lafiya , daman zuwa mukai mu nuna miki sabuwar motar da Sanam tayi , itama idan kinga zakisa Daddyn ki yasai miki to mukuma zamu kuma canza wata , dan kinsan *'Yar kishiya* anriga da antara mata ba Albashi suke d'auka ba , Zahra sosai taji zafin maganganun Diyana amman sai ta dake tace " *'Yar* *Kishiya* ina tayaki murna Allah yasanya Alkairi , ke kuma Diyana ai wanda ni ansan muna dashi kefa dakike binta kike maula , murmushi Diyana tayi sannan tace " dad'in abin nice nake maular ba Ubana ba , kuma inayin maular ne a inda nasan akwai abin bayarwa , Zahra zatayi magana Najeeb yace " sorry Baby ba girmanki bane , kishare kawai karki biyewa 'yar yaga riga , wani mugun kallo Sanam tayi masa sannan tace " waye 'Yar yaga rigar ? Najeeb yace " wacce take take miki baya mana , Sanam tace " ka gyara lafazinka tunkafin mu kunyata ka a gaban budurwar taka , tana gama fad'ar haka tashige cikin motar suka bata wuta sannan suka fice daga cikin gidan.......






*Zantafi yajin aiki tunda ba'ayin CommentπŸ˜’*
[9/26, 21:04] Muhammad Karim: *'YAR* *KISHIYA*
_Rik'on Me Hak'uri_
πŸ€¦πŸ»β€β™€οΈπŸ€¦πŸ»β€β™€οΈ




*NA*
*Zee* *MD*




*Hamdala* *Writer's* *Association* πŸ’ͺ
https://www.facebook.com/111403834371046


✨✨ *{{* *H.W.A* *}}*✨✨




*Bisimillahir* *Rahamanir* *Rahim*






_Nagode sosai Mutanena da tarin addu'oinku , Allah yabar k'auna_




Chapter 7.




Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login