Showing 1 words to 3000 words out of 87659 words

Chapter 1 - HADARIN GABAS Book Complete By Nazeefa Sabo Nashe.pdf

HADARIN GABAS…….


NAZEEFAH SABO NASHE✍


BRIGHT PENS SECOND BATCH.




*********1️⃣



A hankali ta mik’e daga faffa’dan gadon nasu da yaji shimfi’da mai kyawun gaske ta zallar wani bedsheet
da duvet d’insa Pink color mai kyawun gaske. Idanu ta zubawa Twin sister d’inta sai kuma ta saka hannu
ta Shafa gefen chin d’in ta tana murmushi she loves her sister so much. Bata son abinda zai tab’a ta ko
ka’dan ko don sun zama y’an biyu ne. Iman ta ‘d’an juya ka’dan tana bu’de idonta Akan na Amani sai
kuma ta d’an Ware ido tana Kai kallonta kan agogon da ke bedsides drawer d’insù. Ware ido ta yi da sauri
tana furta “Oh shit, already na San mun yi late zamu sha fa’dan Dada be quick mana Ama ki shiga
wankan.” Amani ta d’an turo baki tana mik’ewa da y’ar b’ingilar rigar barcinta fara tas silk da ita. Hakan
yasa tabi jikinta ta manne ta fitar da kyakykyawar surarta duk da bata da k’iba Amma akwai cikar zati duk
wani waje da ake son ya cika a jikin mace na Amani a cike yake musamman kwana biyu da take sake wani
irin cika da k’iba da kyau na ban mamaki kamar mai k’aramin ciki. Toilet ta shiga tana tafiya kamar bata
son taka k’asa. A toilet d’in ma bata fara wanka ba sai da ta gama jan rai sannan ta shiga bathtub d’in ta yi
wankan kamar bata so. Bata damu da fa’dan Dadan ba dama yanzu a kullum so take ta dinga b’ata masa
rai she hates him kamar ba mahaifin da ya kawota duniya ba, da tana da iko bata Jin zai sake ko kwana
guda a duniya nan. Ta da’de sosai tana Jin Iman na ta buga mata k’ofa Amma ta yi burus sai da ta gaji don
kanta sannan ta fito. Jikinta da mitsitsin towel. Idanunta akan Iman da take ta mata masifa. “Kin San me
kika aikata kuwa Ama? Kina son yau Dada ya yi yagalgalamu ne sai dai ya yi warning d’in mu kada mu yi
late Amma kin shiga toilet kamar mai son canja fata. Ji har kin saka na yi staining jikina….” Ama da sauri

ta kai idonta kan staining d’in da Iman d’in ta ce ta yi zuciyarta tayi wani irin bugu da k’arfin gaske ta kasa
ko motsi tana kallon Iman ta shige toilet. Amani took a deep breath, Bugu k’irjinta yake sosai bakinta ya
bushe bata Jin wani yawu ko ka’dan a cikinsa a hankali ta furta “Innalillahi wa inna ilaihirrajiuna what
happened to me? Yaushe rabo na da period I forgot ma ana wani Abu period…” Zuciyatta ta sake
harbawa da ta tuno mata idan har bata manta ba It is exactly 3 months rabonta da period kuma sam bata
kawo a ranta ba sai yanzu da Iman ta tuna mata ana wani Abu wai shi Al’ada. A wani irin sauri ta saka
kayanta ta fice daga bedroom da sauri hannunta rik’e da Car key d’inta ta fita harabar gidan. Sam bata
cikin nutsuwarta don haka bata San ta gabza karo da Dadan ba ya ja baya da sauri fuskarsa a ha’de ya
zuba mata birkitattun idanunsa itama nata Wild eyes d’in ta zuba masa tana Jin wutar masifa tana cin
zuciyarta…. Kamar ba Dadanta ba kamar ba Wanda take so ba a baya, Uban da ya kawota duniya Amma
a yanzu ya zama wani enemy d’inta. Mak’iyin da bata Jin akwai na biyunsa. Shima a zafafen yake kallonta
yana Jin fiye da abinda take ji a zuciyarta sai kuma ya ja tsaki zai yi magana ta juya da sauri itama tana jan
nata k’aramin tsakin da ya ji sound d’insa har tsakiyar k’irjinsa. Zuciyarsa ta sake hassala ya fincikota da
k’arfin gaske yana furta “Are you crazy? Ni mahaifinki kike ma wannan tsakin?” Ta juya idonta kafin ta
janye jikinta da k’arfin gaske tana pointing d’insa da d’an yatsa ta furta “And so what? Aren’t you
ashamed to call your self my father? Mhmn Mahaifina fa ka ce? Okay bari na dawo daga asibiti idan
abinda nake zargi ya tabbata ka shirya ganin duk wani tozarci a duniya wallahi don ba zan rufa maka asiri
ba, I will show duniya Who you are. Zan nuna musu saboda ku’di ka zubar da mutuncinka ka kusanci
y’arka…” ta sake cije bakinta idanunta Sun ka’da Sun yi jajur ta sake furta lokacin tears ne kawai suke
screaming daga idanunta, ta furta “Saboda ku’di da son mulki ka kawar min da budurci na wallahi sai na
je gidan radio na siyi field guda don kawai na tona maka asiri…. I hate you Dada….” ta fa’da cikin
whispering voice dinta. Duk da a hankali take magana Amma ta cikin muryarta kana Jin rashin nutsuwa
da zafin da zuciyarta take ciki. Leb’enta sai rawa suke jikinta na kakkarwa ta shiga motar ta ta bar Dada a
tsaye hannunsa sanye cikin aljihu fuskar nan kamar bai tab’a fara’a ba. Da k’arfinta ta Fisgi motar tana Jin
kamar ta bi ta kan Dadan nata ta marka’de shi ya Mutu ta huta da ganinsa. Fuskar da a da ba abinda yake
mata kyau sama da ita Amma a yanzu ba Abu mai muni sama da fuskar Dada a idonta….


Zuciyarta na racing ta shiga mota, gaba d’aya a firgice take. A idanunta kana hango shock sosai.

Rough Driving take yi Allah ne ya Kai ta wani private Hospital lafiya. Asibitin k’arami ne sosai sai dai mai
kyan gaske. A jikinta ta dinga Jin ko ba’a gwada ba ta San ciki ne da ita ba kuma cikin kowa ba sai na
mahaifin da ya kawota duniya. Wannan wani irin bala’i ne. Hijab d’inta ta gyara sannan taja tissue ta
goge hawayen da tunda ta fito daga gida yake zuba idanunta Sun ka’da Sun yi jajur gasu dama manya sai
suka sake kumbura. Shade ta saka a idanun ta fito daga motar k’afarta sanye da black slippers ba
companyn givenchy…..

Amani walked blindly, rawa kawai k’afarta take.
Jikinta a sanyaye duk da usually haka take tafiyar ta, sai dai na yau yafi na ko yaushe lazy. Tana takun
zuciyatta na sake tsananta bugu har ta isa inda zata amshi file d’in ta. Ba yau ne farkon zuwanta asibitin
ba dama can suna da File a asibitin. Kallonta nurse ta yi ka’dan sai kuma ta nuna mata scale nufinta ta
hau a gwada weight d’inta. K’aramin tsaki ta ja don sam bata son a b’ata mata lokaci ta lura kuma
wannan matar so take ta yi wasting time d’inta. Bayan auna weight sai kuma ta gwada B.p d’inta ya hau
ka’dan don haka ta d’an kalleta tana furta “Are you okay? Na ga B.p d’inki ya hau.” Zuciyar Amani a zafafe
kamar zata fito daga k’irjinta ta watsa mata wani banzan kallo tana furta “Kin tab’a ganin Wanda yake
Okay yazo wajen likita? I hate silly question…” Shiru nurse d’in ta yi kafin ta furta “Am sorry Ma’am, I
don’t meant to hurt you…” Daga haka ta shiga Office d’in Doctor d’in don kai masa File d’in Amani
Moddibo. Amani ta sake binta da kallo tana turo k’aramin bakinta zuciyarta take jin tana wani irin zafi
kamar ta fito daga jikinta….



Imaan…


Tun bayan da ta fito daga wanka bata ga Amanin ba, a gaggauce ta shirya cikin simple dress kamar yarda
ta Saba, don sam bata fiye son dress da zai dameta ba. Ta gyara gashinta a gaggauce kafin ta fice a
zuciyarta tana furta Ina ta tafi ne? Don dai ta San ba cin abinci ba a rayuwa ba abinda Amani bata shiri da
shi sama da abinci…. Ta waiwaiga parlorn bata ganta ba, hakan yasa ta mayar da kallonta kan Dadansu
da yake zaune ya jingina da kujera idanunsa a lumshe hakan ya bawa gashin idonsa damar sake kwanciya
sosai. Sai dai kamar Imani hawaye ta gani ka’dan a gefen idonsa. Hannu ta saka ta d’an bugi gefen kujerar
tana furta “Dada Are you Okay?” Ya bu’de lumsassun idanunsa ya zuba su akan Imani da yana da dama
da ya sanar mata He is not Okay, sai dai ba ta yarda za’a yi ya yiwa duniya bayanin abinda yake ransa,
wani sirri ne da ba wanda ya sani daga shi sai Amani sai matarsa Safna.

Ya lumshe idonsa yana taune gefen lips d’insa murya a dashe ya furta “Am Okay Iman.” Daga haka ya
mik’e cikin sassarfa zai bar wajen. Ya ji Iman ta ce “Dada where is Ama? Ban ganta ba kada mu yi late yau
zasu bamu admission later d’in mu.” Bai juyo ba ya amsa mata da cewa “Na ga ta fita a mota may be she
can’t wait. Sai ki biya school d’in.” Iman ta mik’e tana k’ok’arin kiran Amanin da take ta rejecting call d’in
don a time d’in zata ga Doctor. Da taga ta k’i daina kira sai kawai ta tura mata text. “At hospital..” ta kashe
wayar. Imani ta dinga duban wayar tana mamakin abinda ta ji Amanin ta ce “Hospital? Wajen wa duk da
d’okin Amani na son fara zuwa makarantar nan a ce ta tafi hospital. Sai taji zuciyarta ta kasa yarda ta tafi

school d’in ba ita don haka kawai sai itama ta tafi asibitin don duba mai ya faru. Ta San asibiti guda suke
zuwa asibiti ne da likitocin cikinsa suka kasance kwararru sosai duk da bai da girma amma ya yi suna
sosai.




Amani…..



Ta zauna jikinta a sanyaye tana kallon Doctorn da tun shigowar ta ya zuba mata ido. Bata son kallo sam
yana daga cikin abubuwan da ta yi hating much a rayuwarta. Don haka ta d’an turo baki tana murmuring
ta zauna suna facing juna da Doctor Hisham.. “Amani me ya faru?” Samun kanta ta yi da daburce wa ta ji
kamar ta tashi ta tafi ta yaya zata dube shi ta sanar da shi she come for pregnancy test alhali ya san ba
aure ne da ita ba. Sai ta ji kamar ta yi wauta tazo ta tari Doctorn asibitin da suke zuwa duka familyn su.
Amma ya zata yi? Nan ta sani tun suna yara nan d’in ma bata tab’a kawo kanta ita ka’dai ba, sometimes
sun fi zuwa da Inna Talatu ko Didi kakarsu. Hakan yasa ta daburce ta kasa magana. Dr. Hisham dai ya zuba
mata ido yana noticing duk wani motsi nata. Har ya gaji da shirunta ya furta “Amani Moddibo talk to
me… ki gaya min matsalarki..” Ta d’ago tana kallonsa sai ta girgiza kai da sauri ta mik’e zata fita amma
Dr.Hisham ya hanata sabida maganar da ta ji ya yi ta doki dodon kunnenta. “Kin zo pregnancy test
Right?” Wani irin bugu taji zuciyarta ta yi da sauri ta juya tana kallonsa zuciyarta da mamakin furucinsa ta
furta “How do you know?” Lumshe idonsa ya yi yana murmushi kafin ya furta “I know because I am a
Doctor…” jikin Amani na rawa ta zube a kujerar da take gabansa har ta fara ha’da Gumi idanunta na
kawo ruwa ta furta “Kana nufin ka gano am pregnant? Tun kafin ma a gwada. How? Na shiga uku.” Ta
furta idanunta na zubar da wasu irin hawaye jikinta ko ina rawa yake shikkenan ya tabbata tana d’auke da
cikin mahaifinta. Ina zata kai wannan abin kunyar? Da wani ido zata kalli duniya ta musu bayani… runtse
idonta ta yi tana hango kanta a jikin Dada sanda abin ya faru. Ba zata tab’a forgetting wannan daren ba.
Ganin hankakinta ya yi mugun tashi hakan yasa Doctorn Hisham d’an girgiza kai cike da tausayinta ya ce
“Sit down Amani, am note sure kina d’auke da ciki, har sai mun yi miki test zamu tabbatar sometimes
period na d’aukewa mace for some reason, idan har kin san ba wani abu you should not worry ki nutsu,
idan ma cikin ne akwai hanyar da za’a rabaku da shi ba tare da wani ya sani ba. Ta zauna har a lokacin
tana jin wani irin jiri. Holding kanta da kamar ana mata pounding ta yi. Tana kallon Doctorn da ya mik’e
da kansa ya fita, sai gashi ya dawo da wani d’an silver tray a hannunsa. Da kansa ya d’au blood sample
dinta sannan ya bata wata y’ar roba ya ce yaba needing fitsarinta. A toilet d’insa ta yi ta fito ta mik’a
masa hanninta na rawa idaninta still suna zubar da hawaye. Cikin rarrashi ya zaunar da ita, don haka

kawai sai ya ji yarinyar na ba shi tausayi. Ya dawo bayan mintuna ya zauna yana jiran result d’in. K’ok’ari
yake ya kawarwa da Amani damuwa sai dai ina ta lula duniyar tunani.



Ba’a yi taking time ba Nurse d’in ta shigo da enveloped a hannunta. Ta mik’a ma Doctorn. A hankali ya
fara ware envelope d’in. Kafin Amani taga ya ‘dago ya zuba mata ido hakan yasa ta ji zuciyarta ta wani irin
bugawa da k’arfi ta ce I know am pregnant Innalillahi wa inna ilaihir rajiuna…. “ Doctor Hisham
hankalinsa a tashe ya dinga k’ok’arin kwantar mata da hankali shi kansa bai san yana da sanyin murya ba
sai a ranar ya tsorata da yaga pregnancy test d’in shows positive. A hankali ya furta “Calm down Amani,
tell me what happened, I promised you zan cire miki cikin right now….” Amani ta d’ago tana masa wani
irin kallo kafin cikin wata irin murya ta furta “I won’t abort it, I won’t Abort it. I want to give birth to it, ko
da ni zan rasa rayuwata saboda bak’in cikin haihuwarsa ina son cikina whether for my sake or to spite my
father. I want to see what people said when I introduce my child. This is the product of his sins Zan b’ata
siyasar tasa siyasar da ya yi amfani da ni don ya cimma burinsa. Zan b’ata masa suna daga mutum mai
farin jini zuwa mai bak’in jini. Oh God give me strength to endure this madness….. Ta fa’da cikin wata
iron murya da take shaking… Doctor kallonta kawai Yake ba Tate da ya fuskanci da wa take ba…


Ta saki wani irin k’ara a duk sanda zata tuna sai hakan ta faru da ita fita take cikin hayyacinta. Da sauri
Hisham ya tare ta ganin zata kai k’asa sai dai ina tun kafin ta fa’do jikinsa ya tabbatar ta suma. Da sauri ya
kwantar da ita a kan gadon d’akin. Kafin ya lalubi wayarsa ya kira nurse kafin tazo ya mayar da kiran kan
Imaam Moddibo….


A kasalance Dada ya d’aga wayar yana mamakin dalilin da yasa Doctor Hisham zai kira shi. Haka kawai sai
ya samu kansa da fa’duwar gaba sai dai yanayinsa bai nuna ba don da wuya kaga abinda zai firgita zuciyar
Moddin Didi. Amsa sallamar ya yi.Doctor Hisham da sauri ya sanar da shi abinda ya faru… Wata irin
kakkarwa Jikin Dada ya fara yi ya ce “Did you just say Amani is pregnant?” Hisham ya ce “Yes she is
pregnant result ya nuna haka.”

A zafafe Moddi ya ce “Ka zubar da shi Doctor, ka zubar da shi yanzun nan bana son kowa ya san da shi
zan biya ka ko nawa ne……” “Cikin wa za’a zubar?” Mommy Safna ta fa’da tana shigowa cikin d’akin. Ya
dubi Uwargidan nasa hankali tashe….

JIKAR NASHE CE★✍️‎HADARIN GABAS……



NAZEEFAH SABO NASHE★✍️

BRIGHT PENS SECOND BATCH:


KARFE A WUTA(Ayshacool)

MUDALLAB(Nimcyluv)

HADARIN GABAS (NAZEEFAH SABO NASHE)

ZAYTOON (ZEE KUMURYA)



08033748387.

#AmanisStory
#Resillience
#Healing
#SurvivorStory
#Newbook
#LoveStory.

FROM SURVIVOR TO THRIVER: AMANI’S STORY.

Where darkness meets resilience.


Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/5Y2EmZDu7OvHg6iDTCY81D



2️⃣



Idanuwa suka ha’da Safna a bayyane ta nuna tashin hankalinta da sauri ta isa inda yake ta zauna a
gabansa. Hannayensa ta kama tana kallonsa da raunatattun idanunta ta furta “You are not telling me
Amani ce ke da ciki? Innalillahi wa inna ilaihirrajiuna yanzu ya za mu yi Imaam?” Wani irin kallo ya zuba
mata kallo mai bayyana zallar takaici kafin ya cusa hannayensa cikin gashin kansa, leb’ensa ya taune daga
gefe a zafafe cikin B’acin rai Ya ce “Ke kika jawo Safna, ke kika cilla ni cikin wannan bala’in

sabida neman duniya, ga duniyar ta samu Amma yanzu ta yaya kike son idan asiri na ta tonu na yi
bayani? Ta yaya kike son na yiwa Didi bayani da sauran Yayyena da idanunsu yanzu zasu dawo kai na?
Didi zata tsine min, Yayyena za su yi Allah wadarai da na zamo ni ne kawai d’an uwansu namiji. Jama’ar
duniya musamman na jihata za su tsaneni mulkin da na samu ya tashi a banza kowa zai dinga kallon arziki
na a wani mudubi na daban. Kin cuce ni Safna tun a lokacin na ce Miki No! Amma Muhammad Alwan ya
ha’da baki da ke kuka saka na kusanci y’ata ta ciki na dole, na yi ruining life d’inta na saka mata tsana ta a
zuciyarta a zahiri a yanzu ba Wanda Ama ta tsana a duniyar nan fiye da ni, tana jin kamar ta kashe ni.”
Safna ta ja hannunsa zata rik’e da wani irin zafin nama ya janye hannun yana kallonta da birkitattun
idanunsa. Ko a baya tana shakkar Imaam Moddibo da wannan kallon balle yanzu da yake cikin yanayin da
bata tab’a ganinsa ba. “Ka nutsu Imaam mu samu mafita. Laifi ne an riga an aikata kuma ya wuce ba
shikkenan ba. Yanzu zuwa zamu yi asibitin mu saka Doctor ya yi aborting cikin ko bata so. Maganar wai
kada asiri ya tonu ka bar ni da ita I will figure it out” Ta furta tana d’an sakin murmushi da alama sam

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login