Showing 69001 words to 72000 words out of 87659 words

Chapter 24 - HADARIN GABAS Book Complete By Nazeefa Sabo Nashe.pdf

daga
idanunta… Mik’ewa Dahdan ya yi don isa wajenta da son ya yi mata bayani, sai dai ko kafin ya kai k’ofa ta
fice da sauri, bata son ganinsa ba kuma ta son jin ko wane kalami daga bakinsa. Ta ji komai ta kuma
amince Dadan matsafi ne, da gaske tsafi yake yi shi yasa duka abubuwan suke faruwa. Ashe hauka take
da take d’orawa Mommy Alhajin komai. Dahdan ne mai laifi shi ya yi silar afkawar Amani cikin wannan
halin. Ta mayar da k’ofar ta rufe Har da murza key sannan ta jingina da k’ofar wani irin kuka da bata tab’a
irinsa ba a rayuwarta ta shiga yi. Da dukkan k’arfinta take buga k’ofar da kanta tana furzar da wani irin
huci mai zafi. Daga k’asan ranta take jin wani irin zafi zuciyarta kuwa kamar ana tafasa ta da ruwan zafi.
Gangar jikinta idan banda tsiyayar da gumi ba abinda take yi. Duk da tarin sanyin A.cn da yake d’akin jin
ta take kamar tana cikin Oven, tsabar zafin da take ji na tashin hankalin da take ciki. Ta zube a gado
idanunta akan hoton mahaifiyarsu, kallon hoton ta yi kafin ta fisgo shi da k’arfinta ta shiga magana da shi
kamar wacce take cikin hoton tana jinta. “Me yasa? Me yasa Mahmeey kika Mutu kika bar mu? Me yasa
baki tafi da mu ba, kika barmu a wannan duniyar mai cike da maciya Amana da burin duniya? Mun
fuskanci k’alubale da dama kafin mu tashi mu kai yanzu, sai gashi a yanzu muna fuskantar k’alubalen da
yafi Wanda muke ciki, mahaifinmu Mahmeey, Dahdah yana shirin kusantar Amani y’ar cikinsa don Son
Duniya…” Sai ta sakè fashewa da kuka da k’arfin gaske, ta rungume hoton y’ar riga a jikinta. Ta da’de
zube a wajen cikin fitar hayyaci kamar wacce ta zare, burinta mutuwa a loakcin burinta ha’duwa da
mahmeey a can inda ba zata sake ganin Dahda ba, ba zata sake ha’duwa da duk wani k’alubale mai shirin
tarwatsa mata zuciya ba. Tana so ta Mutu sosai kamar yarda Amani take burin mutuwar itama. Bugun
k’ofar da ake yi ne yasa ta dawo cikin hayyacinta, sai kuma tabi k’ofar da kallo tana tunanin waye sai ta ji
muryar Amani tana kiran sunanta. A kasalance ta mik’e ta bu’de mata k’ofar. Idanu suka zubawa juna
gaba d’ayansu kowa yana jin wani irin ciwo a ransa, ganin halin da d’an uwansa yake ciki. Iman ta finciko
Amanin ta mayar da k’ofar ta rufe ta rungume ta da k’arfin gaske, a tare suka saki kuka sautin bugun
zuciyarsu yana k’aruwa. Jikin Amanin zafi zau da alama mugun zazzab’i ne ya kamata. Iman ta ja
hannunta zuwa bakin gadon ta zaunar da ita kafin ta mik’e cikin First aid box da yake gefen gadonsu ta
bu’de ta Ciro pain reliever ta d’auko table water ta dawo inda Amanin take. A baki ta zuba mata maganin
Amanin tana b’ata fuska ta sha maganin. Kafin ta zube a saman gado. Iman D’in ma kwanciya ta yi daf da
ita tana sakin ajiyar zuciya ta furta “Matsalar mu daga yau In sha Allah ta kau Ama.” Amanin ta ‘d’ago
tana kallonta da neman k’arin bayani. Iman ta d’aga mata kai “Dole zamu bar gidan nan a daren yau….”
Amanin ta zaro ido kafin ta lumshe su sai kuma ta ciji leb’enta bata ce komai ba. “Zamu wuce wajen
dangin Mahmeey, Har sai komai ya lafa, ina tsoron afkuwar wani abu da naji shi da kunne na yau, da
wani ne ya gaya min ba zan tab’a yarda ba…” Amanin bata bu’de idonta ba. Zuciyarta ce kawai take
bugawa da wata irin k’aunar Dahda mai zafin gaske… tana kallo Iman ta shiga ha’da musu abinda zasu
buk’ata. Har ta gama bata ce komai ba, tana jin abinda Iman ‘D’in ta yanke shine mai kyau…

Dahda kuwa tun bayan fitar Imani sai kawai ya lumshe ido Ya jingina da kujera yana jin kansa yana matsa
da wani irin ciwo. A hankali yake taune lips d’insa. Daidai lokacin Amanin ta shigo kamar an jehota a
firgice duk ta yi wani irin. Kallonta yake da mamakin yanayin da take kamar wata Mara lafiya. Zama ta yi a
gefen kujerar da yake kawai sai ta samu kanta da saka kuka. Bai ce mata komai ba har ta gama kukan da
ya tabbatar shine zai saka ta samu sauk’in ra’da’din da take ji a zuciyarta. Ta ‘d’ago a fisge ta sauke ganinta
a kansa kafin ta furta “Dahdah da gaske kai ka haife ni?” Shiru ya yi bai amsa mata ba, sai dai bai janye
idonsa daga kanta ba, ya furta “Kina tantama ne?” Ta cije leb’enta da k’arfin gaske kafin a fusace ta ce
“Ina tantama, idan Uban da ya kawo y’arsa duniya zai aikata abinda ka aikata, idan kuwa kai ka haife ni ka
cuce ni ka cuci kanka Dahda, ka gaya min me yasa ka aikata min haka, kuma waye Uba na don ban yarda
Kai ne ka haife ni ba…” Bai mata magana ba, Ya cigaba da kallonta yana fusgar leb’ensa kafin ya mik’e
tsaye. Wata drawer taga Ya bu’de ya zaro wani enveloped. Ya cilla mata a hankali ya furta “Your
answer…” Ya koma ya zauna yana furta “Komai kika gani jiya ke kika jawowa kan ki, shi yasa idan mutum
ya ce abinsa sirri ne baya son a gani, yana da kyau ka janye hankalinka daga kansa, Saboda baka San me
zaka je ka gani ba, yanzu da kika ga abinda ba a so ki gani ‘d’in ga situation d’in da kika jefa kanki nan, so
are you happy?” Daga haka ya koma ya zauna yana cigaba da kallonta, da kallon yarda hannunta yake
rawa wajen bu’de enveloped D’in. Hoto ne da wasu takardu. Hoton jarirai ne guda biyu rungume a
hannunsa yana nunawa Mahmeeynsu gefe guda kuma Didi ce da Umma T. Fara’ar fuskarsu ta kasa b’uya.
Y’ar riga murmushi kawai take idanunta akan jariran da y’ar k’walla a gefen idon nata. Ta San hoton don
haka ba bak’o bane a wajenta. Takardar ta tsirawa ido tana kallon sunan mahaifiyarsu a jiki da ranar da
aka haifesu. Sai kawai ta lumshe ido hawayenta na cigaba da sauka. Dahdah shiru ya yi yana jin wani
rauni a zuciyarsa, yarda yake jin zafin zubar hawayenta daidai yake da d’igar dalma a jikinsa. “Enough
Ama….” Ya furta cikin wata irin silent voice da take fita da wani irin magana’disu da yasa dole Amani ta
bu’de idanunta ta zube su a kansa… d’aga mata kai ya yi kafin Ya saka handky ‘D’in hannunsa yana share
mata hawaye. Zuciyarta ce ta dinga bugu madadin samun sauk’i a ranta sai ta dinga jin wani irin yanayi. A
firgice ta farka daga mafarkinta ta kuma ture hannun Dadan kafin ta mik’e da sauri, ta yi hanyar fita daga
sashen nasa, sam bata ganin gabanta…


Ya da’de zaune a wajen bayan ya janye idonsa daga kallon Amanin da ta fice a firgice. Ya sauke ajiyar
zuciya yana murzar goshinsa. Yarda yake murza goshin ji yake kamar yana tafiya ne da tarin damuwarsa.
Wani irin sanyi ya dinga bin sassan jikinsa. Nauyin da zuciyarsa ya yi ya dinga sauk’ak’e. A hankali yake
sauke ajiyar zuciya. Da gaske ya samu hanyar warwarar matsalarsa… Amma ta yaya? Ta Yaya zai amsa
tarin tambayoyin da ya hango a idon Imaan da Amani….. a hankali ya mik’e yana zagaye d’akin ya san
Imaan ta ji shi a wayar da yake magana, a idonta ya hango jin firgicin maganarsa, sai dai bata tsaya ba,
bata tsaya ya yi mata bayani ba, duk da shi kansa bai San kalar bayanin da zai mata Har kwanyarta ta
‘dauka ba. Don haka shirun shine yafi gwara ya ja bakinsa ya yi shiru kawai. Ya san shi mai laifi ne a wajen
yaransa, laifin da yake tunanin ba abinda zai goge shi, a idonsu yake hango tsanarsa lokaci guda kuma a

idon nasu dai yake hango tarin k’aunarsa, da tausayinsa. Da gaske shi abin tausayi ne, Safna ta mayar da
rayuwarsa akan irin tafarkin da take so, Ya amince ta yi winning a kansa…..



Cikin sanyin jiki ya koma sashen Didi. Rarraba ido yake a cikin tarin y’an uwansa ko zai hango y’ay’ansa.
Sai dai Babu su ba alamarsu. Ba wanda ya lura da halin da yake ciki. Don murna da zakwa’din aurensa da
suke yi. Ya d’an tab’e baki kafin ya zauna a daf Didin. Da jarumta sosai a muryarsa don son ya kawar da
yanayin damuwar da yake ciki ya yi magana. “Kun cika gidan nan da hayaniya, and kun sani bana son
hayaniya why all the noises don Allah ku tattara ku tafi, I need privacy ina son magana da Didi….”
Dukkansu da suke wajen sai da zuciyarsu ta buga. Basa son komai zai gayawa Didin ya ce Ya fasa auren,
zuciyar Didi ba zata d’auka ba zai raunata mata zuciya. Ba tun yau ake nema
Masa aure yake fasawa ba. Didi ma kallonsa take tata zuciyar tafi ta yaran nata bugawa bata manta wani
lokaci data nema masa auren ba, a ranar auren bayan an d’aura ya gudu bayan ya yiwa matar saki guda.
Don haka ta dinga kallonsa, kallon da Har sai da Ya saka ya yi k’asa da kansa, a hankali ya furta “Ba zan
fasa ba Didi, ba abinda kike tunani bane.” Sai ta sauke ajiyar zuciya kafin wani murmushi ya bayyana a
fuskarta. Da gaske ta San wannan karan Moddi ba zai watsa mata k’asa a ido ba.. hankalinta ya kwanta, ta
dinga kallon su Fateema da suke tattara kayansu da na yaransu suna mata sallama. Idonsa a lumshe yake,
sam hankalinsa baya kansu yana can wata duniya da Ya yi zurfi a cikin tunaninta… sai da Fateemah ta
dafa shi ta ‘d’an yi magana da k’arfi a kunnensa. “Kiddo mun tafi, saura kuma ka je ka gayawa Safna
k’anwar Didi zaka yi aure..” Bai bu’de idon ba, balle ya bata amsa, alamun y’an miskilancin na kusa, idan
yaso haka yake sai ya cije ya k’i magana musamman idan zuciyarsa bata cikin sukunin yin
Maganar. Shafa gefen kumatunsa ta yi, sai kuma ta
Ja hancinsa tana furta “To Uban miskilanci, saduwar alheri.” Ya d’an murmusa kawai ba tare da ya bu’de
idonsa ba. Ya furta “Akwai sak’o a account d’inki, share it with Your sister’s” Ta k’asan ido yake kallonsu
duk suna ficewa…


Har ta kai k’ofa ta tuna bata yi sallama da su Amani ba. Sai kawai ta dawo zuwa ‘dakinsu na b’angaren
Didin. Jin kamar suna magana k’asa k’asa yasa ta tsaya ta lab’e tana jin su. Iman ta ce “Sha biyu na dare za
mu gudu, idan yaso ko garin su Mahmeey sai mu je.” Fateemah ta waro ido, kafin ta tura k’ofar ta shiga
da sauri suka ‘d’ago suna kallonta sai kuma suka sunkuyar da kai. Akwatin gaban Imaan ta kalla sai kuma
ta kallesu d’aya bayan d’aya gabanta na fa’duwa ta furta “Guduwa za ku yi?” K’asa suka yi da kansu. Jikin
Fateemahn a sanyaye ta zauna daf da su. Nasiha ta dinga musu da alk’awarin ba abinda zai faru In sha
Allah. “Moddi ba mahaukaci bane, na San ko giyar wake ya sha ba zai aikata muku komai ba.” Imaan tana

hawaye ta labarta mata komai. Wani irin waro ido ta yi a gigice ta mik’e ta koma parlorn Didin, da wani
irin duba take kallon Moddi Kfin ta furta “Imaam kana cikin hankalinka kuwa? Didi kin san abinda yake
shirin aikatawa?” Da sauri Ya kalleta a idanunta Ya hango da gaske abinda duk ta sani zata gayawa Didi, Ya
runtse idonsa kawai…..

Free pages Saura few pages fa! Ku hanzarta samba’do ku’dinku. 2118666253 UBA


JIKAR NASHE★✍️HADARIN GABAS…..

29.


NAZEEFAH SABO NASHE

08033748387.


BRIGHT PENS SECOND BATCH

Idanu ya sake warewa ganin Fateemah har ta fice daga parlorn ba tare da ya san me suke tattaunawa ba.
Ya sake lumshe idonsa ganin Didin kawai ta zuba masa ido, sai yaga kuma ta mik’e ta nufi d’akin da su
Amanin suke. Tura k’ofar ta yi jikinta a sanyaye ta zuba musu ido. Su ‘‘d’in ma kallonta suke. Ta zauna a
gefen gadon tana kallon akwatinansu sai ta saki murmushi kawai, murmushin da su Amani suka ‘dauka
na mamakin abinda zasu aikata ne. “Za ku gudu saboda Didi ta Gaza a wajen baku kulawa ko? Za ku gudu
saboda k’una tunanin zan iya bari a cutar da ku ko ni na cutar da ku ko?” Sai ta girgiza kai ta furta “In dai
ina raye ku saka a ranku ba abinda zan bari ya cutar da ku, ina son ku ina tausayin maraicinku.. ku k’ara
min lokaci komai yazo k’arshe, na san kuna da matsala Fatima ta gaya min komai, ina kuma kan bincike
akan abin duk Wanda yake da saka hannu a ciki Allah zai yi maganinsa. Komai yazo k’arshe Moddibo zai yi
aure jibi, da matar da nake tunanin ita zata zame masa alheri a rayuwarsa, matar da zata so ku taso mu ta
kuma sake dunk’ule zumuncinku waje ‘daya.” Farin ciki ya cika zuciyarsu gaba d’aya suna jin a ransu

kamar da gaske duk wata matsalarsu ta zo k’arshe. “Kada ku k’ullaci Babanku, bashi da laifi ko ka’dan son
zuciya ne ya shigo cikin lamarin… ku yi hak’uri kun ji.” A wannan gab’ar dai Imaan ta jita kawai ba don ta
yarda da abinda ta ce ba, saboda da kunnuwanta ta ji abinda Dadan yake fa’da a waya. Sai kawai ta ja
ajiyar numfashi ta sauke tana kallon idon Didin da itama ta zuba mata ido, tana son ta gayawa Didin
komai sai dai bata San ta inda zata fara ba, maganar ta girmi kwanyarta. Didi ta shafe kansu ta sake fita.
Iman kallon Amani take da idonta suke lunshe sai kawai ta samu kanta da Shafa gefen fuskarta Amanin ta
Ware ido tana kallonta a hankali ta furta “Menene?” Amanin ta girgiza kai kafin ta furta “Bakomai.” Duk
da akwai komai ‘din wani irin zafi take ji a zuciyarta Wanda ta tabbatar na Kishin Dada ne, sai dai tana
fatan aurensa ya zama silar yayewar matsalarta.



Haka aka dinga shirin biki gadan gadan ba tare da Sun bari Safna ta sani ba. Sai dai a ranar ta fahimci
abinda ake shirin aikatawa don da tashin hankalin da take ciki yasa bata Saka ido a kan mutanen gidan
ba, mafita kawai take nema. Mafitar da zata wargaza kwanciyar hankalin zuri’ar Lami’do ta saka musu
firgici da b’acin ran da ba zasu tab’a mantawa da shi ba. A zaune take gefen gado hannunta rik’e da robar
rubutu ta tsurawa rubutun ido tana d’an murmushi k’asa k’asa. A hankali ta furta “Da gaske komai yazo
k’arshe kamar yarda Malam ya ce..” Sai kawai ta saki wata irin mahaukaciyar dariya… daidai lokacin
wayarta ta dinga ringing ido ta zubawa wayar tana jin wani irin matsananciyar fa’duwar gaba. Hannu na
rawa ta saka ta ‘d’au wayar ganin sunan Alwan da ya bayyana b’aro-b’aro a screen ‘D’in wayar. Tsinkewar
gabar da ta samu kanta a ciki ne yasa bata San wayar ma Upside down ta rik’e ta ba. Sai da ta ji muryar
Alwan yana furta “Kin kasa cika mana aikinmu, ga Mijin da kike so kamar ki Mutu yau ya miki Kishiya, yau
an ‘d’aura auren Mijinki d……” wani irin waro ido ta yi tana jin wani irin zafi tun daga k’asan zuciyarta
Har gangar jikinta. A razane ta ce “What?” Alwan Ya saki murmushi yana furta “Da gaske ya yi aure,
mahaifiyarsa ta masa auren Sirri, idan kina son kuma ya rabu da matar sai kin aikata abinda muke so, ki
saka ya kusanci yarinyar can ko ba ya so, ki yi musu vedio kice idan har bai rabu da matar ba zaki tona
masa asiri zaki saki vedion kowa ya san waye shi?” Murmushi ta saki wata irin nutsuwa tana shigarta.
Tabbas wannan ce shawara dama ko ba’a yi haka ba tayi niyyar ta saka ta tilas ya kusanci Amani don ta
b’ata musu rai kamar yarda suka saka tata zuciyar ciwo. Alwan ya katse wayar ya barta da tata wayar a
hannu. Da k’yar ta zame wayar daga kunnenta. Ta tuna a yau tana da damar da Imaam zai kusanceta sai
ta saki jin da’di a ranta,don a yau ne zata yi amfani da maganin mak’ale mata da Malam ya bata. Ya kuma
tabbatar mata in dai Imam d’in ya kusanceta ba zai sake marmarin wata mace ba da sunan aure… “Zan
yi amfani da maganin amma sai na gama da wannna matsalar.” Ta furta kanta tsaye. Wanka ta shiga tana
jin ba wani b’acin rai tare da ita duk wani shiri ta gama shirya shi a zuciyarta.

Ta gama wankan sannan ta shirya ta shiga kitchen. Favorite dishes d’in Didi ta dafa a gidanta su Mama
Talatu suna tayata cike da mamakin sauyawarta, ko dai bata son abinda ake ba ne a gidan.” Mama Talatu
ta fa’da k’asa k’asa tana kallon Inna Laraba bayan Safnan ta shiga store da yake cikin kitchen ‘din. Suka yi
shiru ganin ta fito still fuskarta cike da walwala tana kallonsu ta umarcesu su kwashi abincin su biyota
parlorn Didi da su. Haka kuwa aka yi Didi sai gani ta yi suna jera abincin a babban Dinning area d’inta da
Yasha adon carpet mai taushin gaske da pillows manya. Don Moddi bai saka mata Dinnig table ba ya san
bata so sai ya saka mata wani table irin na k’asan nan sosai Mara tsaho. Cikin mamaki Didi take bin Safna
data zauna a gabanta da kallo. Murmushi Safnan ta yi sai kuma ta sunkuyar da kanta idonta yana tara
k’wallar da ta k’irk’iro ta k’arya. Murya a k’asa sosai ta shiga bawa Didin hak’uri “Don Allah Didi ki yafe
min, In sha Allah ba zan sake aikata abinda duk na aikata a baya ba, na yi nadama kuma ina neman
afuwarki data yaranki Har ma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login