Showing 27001 words to 30000 words out of 87659 words

Chapter 10 - HADARIN GABAS Book Complete By Nazeefa Sabo Nashe.pdf

zabga k’amshi yake.
Safna ta dinga kallonsa tana jin alfaharin kasancewarsa Mijinta. D’an rungumo shi ta yi tana shafa masa
wani turare da ba na komai bane sai na mallaka a kullum idan zai fita sai ta shafa masa sam baya kawo
komai a ransa don ta iya salo da kissa iri iri.


A parlorn su madaidaici ya zauna. Daidai lokacin da Iman da Amani suka shigo jikinsu a d’arare yaran
suna kallon Dahdansu da yake shan tea da k’wai. Yawu suke ha’diyewa don dai su ba shi aka basu ba.
Kunu ne da k’uli-k’uli kullum Mommyn take sakawa a basu kuma ta garga’di masu aikin da kada su
kuskura su fa’da k’arshe ma ta saka duk aka musu dabaibayi sai abinda tace suke aikatawa. Don haka ba
zasu tab’a bu’de bak’i su fa’da ba sai idan ta so. Idon Amani ya kawo ruwa tana kallon Dahda ta nuna
k’wan hannunsa. Da mamaki yake kallonta cikin tausayin yaran da kullum a fuskarsu zaka san su marayu
ne ba su da walwala sam sai dai idan Hajja tazo gidan ta kwana biyu. Ya ja hannunta ta matsa kusa da shi
ya furta “Zaki ci ne?” Ta d’aga kai. Shiru ya yi kafin ya d’ago yana kallon Safna ya furta “Yaran nan basu
karya ba ne?” Ta ware ido tana furta “In ji Uban wa? Ke dube ni nan baku karya ba?” Ido Dahda ya zuba
mata ya ce “In ji Ubana….” Ya gutsiro k’wan ya mik’a musu duka dankali da k’wan da suke cikin plate d’in.
Da wani irin sauri suka dinga ci… har bai san sanda wata k’walla ta fara zubo masa ba.. Daga ganin yarda
suke ci ya tabbata yunwa suke ji. Sai da suka ci sosai sannan ya ha’da musu tea mai kauri suka sha. Ya
d’ago yana kallon Safna “As from today da yara na zan dinga cin abinci…” Safna ta ha’diye wani mugun
yawu tana furta “Haba dai kawai kuma sai mu zauna da su cin abinci su hanamu sakewa…” Ya watsa
mata wani kallo da ya sakata yin shiru bata shirya ba. Goge musu baki ya yi sannan ya bu’de lunchbox
d’insu abinda bai tab’a yi ba. Waro ido ya yi yana furta “What? Me
Ye wannan? da d’umamen tuwo za su makarantar?” Da sauri Safna ta waro ido kamar gaske hankalinta a
tashe ta ce “what a nonsense, wannan ai ba laifina ba ne laifin su Talatu ne bari a kira su a ji dalili….” Har
ta je bakin k’ofa ya jata baya da k’arfin gaske… ya wancakalar da ita saman kujera, idanunsa sun fito sosai
ya furta “Wallahi na samu laifinkine sai kin ga abinda zan miki. Don su nake nema na don haka dole a
dinga ciyar da su da cima mai kyau…” ya fita tsakargida yana k’wala kiran Mama Talatu da Inna Laraba.

Da sauri suka fito daga d’akinsu da yake gefen tsakargidan. Yanayin da suka gan shi a lokacin ya basu
tsoro suka furta “Baban yara lafiya?” Lunch box d’in ya cilla musu “Meye wannan? waye ya ce a zubawa
su Ama wannan abin su tafi da shi school?” Idanu suka waro suna kallon juna. Tsawar da ya sake saki ne
ya saka su saurin amsawa da rawar baki duk da Suna jin shakkar Safnan ba su fasa cewa “Hajiya ce ta yi
umarnin haka…” Ya juyo ya mata wani kallo da ya kusan sakata fitsari a wando. Bai yi magana ba illa cije
leb’ensa na k’asa da ya yi ya fice yana jan hannun yaran. Zuciyarsa na wani irin tafarfasa shi ka’dai ya san
hukuncin da zai yiwa Safna idan ya koma gidan yana jin k’arshen zamansu ne ya zo. Don ba zai laminci a
dinga zaluntar masa yara ba…


Safna tana ganin ya fita ta juya tana kallon Mama Talatu da Laraba. Ta k’unduma wani zagi kamar ba za
su yi sa’a da uwarta ba. “Ni kuke son ku kashewa aure ko? Wallahil azeem k’arshen zamanku a gidan nan
ya zo…” Haka ta dinga zaginsu tana ci musu mutunci ba su ce mata komai ba. Sai dai zuciyarsu fal take da
murnar tonuwar asirinta yau. Don kam Safna muguwa ce ta bugawa a jarida ba irin azabar da bata bawa
yaran Allah ne ka’dai ya yi da kwanansu a gaba. Sau tari daga su har yaran ba sa sake cin wani abinci
bayan wanda Zata basu da rana sai kuma garin Allah ya waye. Haka suna ji suna gani za su yi ta jin
k’amshin abu amma haramiyarsu. Ko idan Babansu ya kawo abu zai sa ta d’iba ta bi su k’aramin parlorn
da suke zama a tsakar gida da daddare ta shiga da kayan da’din ta ajiye ta ce kuma duk wanda ya ci sai ya
ha’du da fushinta. Wani lokacin Amani ce duk hanata da zasu yi sai ta ci tun bata iya k’unk’uni har ta fara
sakarwa Mommyn k’unk’uni kuma duk abinda zata mata ba zata yi kuka ba, sai dai ta yi ta cizon leb’enta
tana huci kamar yarda ta ga Dahdansu yana yi. Har tsarki da ruwan borkono ta tab’a yiwa Amani ranar ba
su yi barciba kuma duk kukan yarinyar ta hanasu su gayawa Ubanta… kai muguntar Safna garesu ba zata
k’irgu ba.. idan suka yi nufin gayawa Hajja sai su ji kamar an k’ulle musu baki sun kasa…


Suna kallonta ta shiga d’aki ta saka Hijab ta fito rik’e da jaka. Bata ko kallesu ba ta fice daga gidan. Suma
ba su damu ba don sun san ta saba fita idan baya nan don haka ba wani sabon abu bane a wajensu suka
saki ajiyar zuciya a fili suka fara tsine mata da son Allah ya tona mata asiri komai daren da’dewa….




★✍️

Yana fita ya biya super market ya siya musu kayayyakin da’di da yawa sannan ya sauke su a makarantar
da suke zuwa. Irin private school d’innan ce mai sauk’in ku’di.. Suna sauka a machine d’in Amani da bata
shiru da bakinta ta kalleshi “Dahda kullum zaka dinga bamu k’wai da shayi mai madara… ka siyo mana
kayan da’di mu je da su makaranta?y’an ajinmu duka da kayan da’di suke zuwa, ba da tuwo da kwaki ba.”
Imaam sai da ya yi da gaske sannan ya amsa mata saboda yarda wata k’walla ta fara zubo masa “Zan
muku duk abinda kuke so Ama…” ya fa’da yana sumbatar gefen kumatunsu. Ya rungume su sannan suka
shiga aji. Yau zuciyarsu fal nisha’di ba rashin walwalar nan da suke zuwa da shi makaranta. Imaam ya bi
bayansu da kallo yana share k’wallar da take zuba a idonsa, ya furta “Allah ka yafe min…” cikin raunin
murya don sai ya tattara laifin gaba d’aya ya d’ora a kansa yana ganin koma me ya faru laifinsa ne da baya
bincika halin da yaran suke ciki musamman sanin da ya yi basu da mahaifiya. Kai tsaye zuciyarsa ta ba shi
shawarar ya mayar da yaran nasa gidan Hajja hankalinsa zai fi kwanciya.


�� ���ℯ★✍️HADARIN GABAS…..

NAZEEFAH SABO NASHE★✍️
�ℯℯ� ���ℯ★✍️


08033748387.

★★★★★ 1️⃣2️⃣





HADARIN GABAS…..

NAZEEFAH SABO NASHE.★✍️


�ℯℯ� ���ℯ★✍️


08033748387.

★★★★★





�ℰ���� ℬ��ℋ......✍️



Hannun Muhammad Alwan ya ji a kafa’darsa cikin wata irin murya mai bayyana lallashinsa ya furta “Kada
ka yi abinda zaka yi nadama Imaam, ko ka yarda ko baka yarda ba sai hakan ta faru gwara ma ka yarda
d’in….” Girgiza kansa ya yi yana kallon cikin idon Alwan d’in “Ba zan yarda ba, don ba abinda zai saka ni
nadama na ji na tsani kaina a rayuwa kamar abinda kake son saka nin… kuke son tursasa min sai na
aikata shi…” Wannan karan Murmushi Alwan ya yi ya saki kafa’dun Imaam d’in yana furta “As you
wish… ba zan hanaka yin abinda kake so ba you can do what suits you… amma ka sani kana so ko baka
so sai hakan ta faru gwara ma ka so d’in…” Tsaki ya zabga ya fice daga office d’in da sauri. Alwan ya bi shi

da kallo kafin ya zare handky d’in da ke aljihunsa ya goge fuskarsa yana cigaba da mamakin taurin zuciya
irin na Imaam. Ya san kuma dole abin ya faru da son sa ko ba son ransa. Ya lumshe ido kawai zuciyarsa a
time d’in ba abinda ba ta raya masa. Kada dai ya zama duk abinda suke so ya kasa faruwa dalilin taurin
kan Imaam…







★★★

Har jiri ne ya dinga d’ibansa kafin ya je gida tun a cikin jirgi yake jin zuciyarsa ba daidai ba. Da k’yar ya isa
cikin motarsa inda drivernsa yake jiransa ya yi saurin shiga cikin motar yana amsa gaisuwar Drivern.


Gidan shiru alamar kowa ya kwanta don haka kansa tsaye ya nufi d’akinsa. Wanka ya yi sosai kafin ya
ha’da coffee mai zafi ya sha burinsa ya ji ya daina jin abinda yake ji d’in sai dai hakan bai samu ba.


Da k’yar ya samu ya runtse idonsa yana tunano mafarin ha’duwarsa da Alwan da ya zama sanadiyyar
shigarsa cikin wannan matsalar…


10YRS BACK…

★✍️

Wani irin zafin rana da ake ne ya saka shi parking machine d’insa a gefen wani babban company. Ya zauna
a saman bench yana jin kamar kansa zai tsage. Daga aiki ya taso k’aramin ma’aikaci ne shi a lokacin a
ma’aikatar aikin Jarida da take k’ark’ashin gwamnati. A lokacin ma rahoto ya je d’aukowa sai ya samu
kansa da matsanancin ciwo shine dalilin da yasa ya ajiye machine d’in ya zauna a saman bench. Don sam
ba zai iya cigaba da tuk’ashi ba duk da k’ok’arin da ya yi na aikata hakan.

Tsawon mintuna yana zaune idanunsa a lumshe ya dinga jin wani irin k’amshin turare mai da’din gaske
yana ratsa k’ofofin hancinsa. Da k’yar ya bu’de ido jin ana cewa “Sannu bawan Allah..” Muryar bata masa
kama da ta hausawa ba sai dai mutanen k’asashen waje. Ai kuwa kamar yarda hasashensa ya ba shi wani
kyakykyawan saurayi ne tsaye a kansa yana sakar masa murmushi. “Sannu.” Ya sake furtawa yana kallon
gefe da gefen hanya. “Na da’de a tsaye anan baka sani ba, sai naga kamar akwai damuwa ko?” Imaam ya
tsuke fuskarsa don shi a rayuwarsa bai fiye son a shiga sabgarsa ba. Amma Alwan bai k’yaleshi ba sai da
ya zauna kusa da shi yana furta “Nima aiki ya kawo ni Nigeria so kuma ban san ko ina ba… ina so na
maka tambaya?” “Allah ya sa na sani.” Imaam ya furta yana kallon wani waje. “Apartment nake so mai
kyau na rent da zan zauna wanda ba zai ba ni damuwa ba…” Imaam ya yi shiru kamar ba zai amsa shi ba
sai kuma ya ce “Hotel ko gida?” “Any one.” Alwan ya furta yana sakin murmushi abinda Imaam ya lura da
shi Alwan ma’abocin murmushi ne. “Okay.” Daga haka ya mik’e yana d’an ka’de jikinsa saboda Imaam tun
bai zama wani abu ba d’an gayu ne na gaske. Ya hau machine d’insa ya ce ya biyo shi. Alwan bai masa
musu ba ya bi shi suka tafi har wani Apartment mai kyau ya ja ya tsaya yana kallonsa. “Yauwa ka shiga sai
ka musu bayani, ni zan wuce.” Hannu Alwan ya saka ya rik’e shi. Hakan da ya yi yasa Imaam ya ‘dago ya
tsareshi da ido. Alwan murmushi ya sakar masa yana d’aga masa kai. “Me yasa zaka tafi? Bayan ina
murna na samu aboki a inda ban san kowa ba. Ka taimake min mana nima fa musulmi ne.. ko baka son
lada?” Ya fa’da cikin gwamutstsiyar Hausarsa. Haka kawai Imaam sai ya ji ya amince da son kyautata
masa “Yanzu ya kake son a yi? Ni bana jin da’di ne ina son na je gida.” Cikin muryar tausayawa Alwan ya
furta “Oh Sorry, Amma pls mu yi exchanging number so that muna communicating..” Imaam bai masa
musu ba ya amshi wayarsa mai d’an banzan kyau ya saka masa numberrsa ya kuma yi saving da Imaaam
Moddibo..” Alwan ya kalli sunan yana furta “Nice…. Ni kuma sunana Muhammad Alwan. From Turkey
hope na samu d’an uwa.” D’aga kai Imaam ya yi daga nan ya masa sallama ya burga machine d’insa ya
wuce.


Koda ya koma gida bai wani kira Alwan ba ya ma manta da shi. Y’an biyunsa Iman da Amani ya yiwa wasa
ya shige d’aki.Safana ta bi bayansa ganin kamar baya jin da’di. Bai b’oye mata ha’duwarsu da Alwan ba ya
gaya mata komai. Murmushi ta saki tana furta “Allah yasa ha’duwar ta zama alheri…”

Da sassafe ya dinga jin wayarsa tana ringing. Yana dubawa yaga Muhammad Alwan ne sai da ya mik’e ya
zauna sosai sannan ya saka wayar a kunnensa “Morning” Alwan ya furta cikin nutsuwa “So ka tafi ka bar
amanarka da Musulunci ya baka, baka sake kirana ka ji ya nake ba na kira kuma baka d’aga ba.” Imaam ya
d’an saki ajiyar zuciya ya furta “Am sorry..” “No problem yanzu ina so kazo ka raka ni inda za ni pls!”
Kallon agogo Imaam ya yi ya furta “Ina zuwa aiki yanzu…” “please ka zo idan akwai yiwuwar ka samu
wani aikin da yafi naka sai kaga ka dace muna da companies a Nigeria and menene qualification naka? Ko
da yake sai kazo dai..” Ya fa’da yana kashe wayar. Safna da ta ji komai kasancewar wayar a handsfree take
ta mik’e da sauri tana furta “Alhamdulilah Moddibo ka maza ka shirya ka je ba mamaki wahalarmu ce
tazo k’arshe, dama aikin gwamnati bakomai a cikinsa sai wahala..” D’an kallonta kawai Moddibo ya yi ya
tab’e baki ya shige toilet ba wai don yana ji zai amince ya karb’i tayin da Muhammad Alwan ya masa ba.
Wanka ya yi ya shirya cikin k’ananan kayan da ya saba sakawa ya fito fes da shi sai zabga k’amshi yake.
Safna ta dinga kallonsa tana jin alfaharin kasancewarsa Mijinta. D’an rungumo shi ta yi tana shafa masa
wani turare da ba na komai bane sai na mallaka a kullum idan zai fita sai ta shafa masa sam baya kawo
komai a ransa don ta iya salo da kissa iri iri.


A parlorn su madaidaici ya zauna. Daidai lokacin da Iman da Amani suka shigo jikinsu a d’arare yaran
suna kallon Dahdansu da yake shan tea da k’wai. Yawu suke ha’diyewa don dai su ba shi aka basu ba.
Kunu ne da k’uli-k’uli kullum Mommyn take sakawa a basu kuma ta garga’di masu aikin da kada su
kuskura su fa’da k’arshe ma ta saka duk aka musu dabaibayi sai abinda tace suke aikatawa. Don haka ba
zasu tab’a bu’de bak’i su fa’da ba sai idan ta so. Idon Amani ya kawo ruwa tana kallon Dahda ta nuna
k’wan hannunsa. Da mamaki yake kallonta cikin tausayin yaran da kullum a fuskarsu zaka san su marayu
ne ba su da walwala sam sai dai idan Hajja tazo gidan ta kwana biyu. Ya ja hannunta ta matsa kusa da shi
ya furta “Zaki ci ne?” Ta d’aga kai. Shiru ya yi kafin ya d’ago yana kallon Safna ya furta “Yaran nan basu
karya ba ne?” Ta ware ido tana furta “In ji Uban wa? Ke dube ni nan baku karya ba?” Ido Dahda ya zuba
mata ya ce “In ji Ubana….” Ya gutsiro k’wan ya mik’a musu duka dankali da k’wan da suke cikin plate d’in.
Da wani irin sauri suka dinga ci… har bai san sanda wata k’walla ta fara zubo masa ba.. Daga ganin yarda
suke ci ya tabbata yunwa suke ji. Sai da suka ci sosai sannan ya ha’da musu tea mai kauri suka sha. Ya
d’ago yana kallon Safna “As from today da yara na zan dinga cin abinci…” Safna ta ha’diye wani mugun
yawu tana furta “Haba dai kawai kuma sai mu zauna da su cin abinci su hanamu sakewa…” Ya watsa
mata wani kallo da ya sakata yin shiru bata shirya ba. Goge musu baki ya yi sannan ya bu’de lunchbox
d’insu abinda bai tab’a yi ba. Waro ido ya yi yana furta “What? Me
Ye wannan? da d’umamen tuwo za su makarantar?” Da sauri Safna ta waro ido kamar gaske hankalinta a
tashe ta ce “what a nonsense, wannan ai ba laifina ba ne laifin su Talatu ne bari a kira su a ji dalili….” Har
ta je bakin k’ofa ya jata baya da k’arfin gaske… ya wancakalar da ita saman kujera, idanunsa sun fito sosai
ya furta “Wallahi na samu laifinkine sai kin ga abinda zan miki. Don su nake nema na don haka dole a

dinga ciyar da su da cima mai kyau…” ya fita tsakargida yana k’wala kiran Mama Talatu da Inna Laraba.
Da sauri suka fito daga d’akinsu da yake gefen tsakargidan. Yanayin da suka gan shi a lokacin ya basu
tsoro suka furta “Baban yara lafiya?” Lunch box d’in ya cilla musu “Meye wannan? waye ya ce a zubawa
su Ama wannan abin su tafi da shi school?” Idanu suka waro suna kallon juna. Tsawar da ya sake saki ne
ya saka su saurin amsawa da rawar baki duk da Suna jin shakkar Safnan ba su fasa cewa “Hajiya ce ta yi
umarnin haka…” Ya juyo ya mata wani kallo da ya kusan sakata fitsari a wando. Bai yi magana ba illa cije
leb’ensa na k’asa da ya yi ya fice yana jan hannun yaran. Zuciyarsa na wani irin tafarfasa shi ka’dai ya san
hukuncin da zai yiwa Safna idan ya koma gidan yana jin k’arshen zamansu ne ya zo. Don ba zai laminci a
dinga zaluntar masa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login