Showing 51001 words to 54000 words out of 87659 words
Chapter 18 - HADARIN GABAS Book Complete By Nazeefa Sabo Nashe.pdf
ta isa d’akin Safnan. Da murmushi sosai ta bita da kallo kafin ta bata cup d’in
tana furta sako min sugar ka’dan a ciki idan kuma kika zabga za ki gamu da ni kin san bana son Sugar.”
Kallon cup D’in Imaan ta yi sai kuma ta karb’a da sauri jikinta har b’ari yake ta nufi dinning area. Cube
biyu ta saka na sugar ta dawo Bedroom D’in Mommyn. Cup D’in ta mik’a mata Har ta juya Mommyn ta ce
“Tsaya na ji, idan baki min abinda bana so ba.” Ka’dan ta d’and’ana a bakinta ta yi saurin furzar wa tana
zabgawa Imaan D’in harara “Cube nawa kika saka?” Imaan jiki na rawa ta ce “Just 2 cubes Mommy,
wallahi Ban saka da yawa ba.” A zafafe kamar gaske ta ce “K’arya na Miki kenan? To maza ki shanye ta tas
ai sai da na yi warning d’inki sakarya kawai….” Hannunta na rawa ta amshi cup D’in ta kai bakinta don
kallon da Safnan take mata ya yi mugun gigita ta. Tsaf ta shanye shi sannan Safnan ta janye idonta tana
sakin wani Malalacin murmushi ranta fari k’al ganin ko ina ba’a je ba aikinta ya tafi successful. “Fita ki
bani waje, nan gaba ma ki sake repeating mistake d’inki.” Da sauri Imaam ta fice daga d’akin. Haka kawai
ta samu kanta cikin tsoro da fargaba me yasa ta sha madarar? Shine tambayar da ta mak’ale a zuciyarta.
Safna ta buga k’afa tana shek’a dariya a hankali ta furta “Za ki kawo kanki da k’afarki yarinya kin shigo
hannu, kin zama y’ar hannu.” Sai kuma ta lumshe ido tana hango Diri da surar Imani tabbas zata more….
Don ma ba waccan ba ce? Zuciyarta ta furta tana hango Amani da cikar kyau da surar duka Allah ya bata
sai dai ta San ko giyar wake ta sha Amanin tafi k’arfinta….
Jikinta na rawa Imaan ta shiga d’akinsu….. Amani ta bita da kallo kafin ta mik’e zaune a hankali tana furta
“Lafiyarki kuwa?” Imaan zama ta yi a gefen gadon tana k’ok’arin b’oye abinda yake ranta, so samu ne ta
gayawa Amanin komai sai dai bata son k’ara mata damuwa a kan wacce take ciki. Don haka kawai ta rik’e
kanta tana furta “Nothing, just headache ke damu na, amma na sha magani ma.” Amani bata sake
tambayarta ba ta mayar da kanta ta kwanta ha’de da lumshe idonta, wasu haway na bin idonta masu
d’imin gaske ji take duniyar ma gaba d’aya bata mata da’di.
Daidai lokacin Dahda na tsaye a d’akinsa cikin shigar Suit mai kyan gaske combing kansa yake yi, duk da
baya cikin walwala hakan bai hana shi zabga Uban kyau ba. Ya fesa turaren sa As usual kafin ya tsaya
gaban mudubin yana nazarin kansa, shi da kansa ya san ya rame a kwanan biyun nan. Ya d’an cije pink
lips d’insa masu kama da na mata sai kuma ya fice daga d’akin da sauri kamar Wanda ake ja. Yau yake son
ya kai Didi ta tare a sabon gidansa kafin su kuma gobe su bita. Yana son ya fara yakice umarnin Safna ta
k’arfi da yaji duk da idan ya aikata hakan yana jin wani irin zafi da k’unci a zuciyarsa, shi da kansa ya san
ba haka Safna ta bar shi ba.
A parlor ya tsaya yana dube dube, ganin yarda parlorn ya yi tsit shi mai son yara da hayaniya Amma
rayuwarsa ta koma wani irin silent. Ya saki tsaki kafin ya nufi d’akin su Amani zuciyarsa na bugawa da
k’arfin gaske. A hankali ya tura k’ofar ganin yarda suke a kwance ido a lumshe duk da alamu sun nuna ba
barci suke ba, sai kawai ya tsaya yana kallonsu. Sun san ya shigo don Mayen turarensa ya bayyana musu
hakan don haka a hankali Imani ta bu’de idonta Amani kuwa sake runtse idon ta yi tana shak’ar turaren
da yake sake dagargaza zuciyarta Ya narkar da ita da k’aunar Dahdan. Ido ya zuba mata kafin ya d’auke kai
yana kallon Imaan ya furta “Ku shirya, gobe za mu tare a sabon gida yau zan fara kai Didi.” Wani irin
zabura Imani ta yi cikin tsananin farin ciki ta furta “Alhamdulillah, Dahda da Didi za mu tare?” Ya d’aga
mata gira idonsa a cikin na Amani da ta ‘d’an bu’de su ka’dan tana kallonsu. D’auke kai ta yi shi kuma daga
haka ya fice daga d’akin yana furta “Ban ce a gayawa kowa ba.” Imaan wata ajiyar zuciya ta sauke tana
rungume y’ar uwarta ta furta “At last dai Didi ta sauko, Alhamdulillah.” Amani ta lumshe idonta kawai
tana sakin ajiyar zuciyar kwalliyar Dadan yau gaba d’aya ta tafi da imaninta. Zallar kyansa ya bayyana
kamar shi ya k’era kansa bata tab’a ganin namiji mai kyau da kwarjinin Dahdah ba. Duk surutun da Imaan
take mata bata fahimtar komai zuciyarta ta jirkita can wani gefe na musamman wani abu take ji mai
girma a cikin ruhi da kwanyarta.
A harabar k’ofar gidan nasu ya yi parking. Ya fito bayan ya saka glass d’insa da Ya sake fito da kwalliyar sa.
Cikin takun ginshira ya nufi shiga cikin gidan ganin k’ofar gidan ba kowa yasa ya ji da’din hakan a ransa.
Tsakargidan Shiru daga Didi sai mai taya ta hidima da take tanka’de garin kunu. Didi ta amsa sallamarsa
fuskarta cike da walwala da farin ciki take kallonsa tana nazarin tasa fuskar da sam babu walwala da
annurin da ta Saba gani a cikinta, sai ta ji duk nata farin cikin ya yi k’aura ta mik’e da k’yar tana dafa
bango saboda ciwon gwiwa da ya sakata a gaba ta shige parlor. Moddibo ya bi bayanta yana jin yarda
ransa yake masa rashin da’di ganin irin wahalar da take sha kafin ta mik’e ya zama dole ya kaita k’asar
waje ta ga likita.
A daf da ita ya zube bayan ya taimaka mata ta zauna a saman kujera shi kuma Ya dafa k’afarta yana d’an
sakin ajiyar zuciya ya furta “Ina kewar Didi na.” Murmushi mai girma ta saki kafin ta dafa kansa ta furta
“Ni ma ina kewar Moddin Didi.” Ya saki murmushi ka’dan sai kuma ya kama hannayenta yana furta “Yau
duk wannan ta kau Didi, don Allah kizo ki koma sabon gidan dana gina, ko don ki taya ni kula da y’ay’an
da y’ar riga ta bar min….” Ya fa’da yana kallon idonta suna sakin murmushi a tare sai kuma ya marairaice
fuska yana furta “Please Didi, na yarda duk bayan sati guda ki zo nan ki kwana biyu, ko a kawo ki juma’a ki
koma lahadi don abincin sadaka…” Shiru ta yi tana kallon idon Moddi da ya bayyana son a tausaya mata.
Sai ta ji duk hankalinta ya tashi, ta ji tana son ta koma inuwa guda da Moddi ko don kula da tarbiyyarsa
da ta yaransa ma gaba d’aya. Zuciyarsa ta dinga bugu, Ya dinga jin tsoron amsar “a’a” daga bakinta.
Kallonsa kawai take murmushi na son sub’uce mata ganin yarda ya bayyana tsoro da fargaba k’arara a
idonsa a hankali ta furta “Na amince Moddibo ko yanzu kake so zan bika mu koma Allah ya yi maka
albarka….” Wani irin farin ciki ya shiga ransa Ya bu’de ido yana mamakin saurin amincewarta ba tare da
ta sake tambayarsa wace Sana’a yake yi Ya tara Uban ku’di haka ba… “Yanzu fa Didi.” “Yanzu kuwa
Moddi, ba dai ka saka duk abinda nake buk’ata ba, amma dai ka jira ni ka’dan na yiwa mak’ota da abokan
arziki sallama idan yaso gobe sa biyo ni su ga gida.” Farin cikin da yake ciki ne yasa ya rungumeta ba tare
da ya sani ba. Nata farin cikin ya ninka nasa don haka itama ta rungume shi sosai a jikinta tana jin kamar
wancan Moddin d’an jariri da ta haifa ta Raine shi cikin so da kulawa. Mamaki bai sake kama shi ba, sai
da yaga ta shiga cikjn d’akin ta fito da babban mayafinta ta rufa a kanta sai kuma ta yi hanyar waje tana
furta “Ka kira y’an uwanka ka shaida musu yanzun nan.” Hannunsa Har rawa yake Ya ciro wayar ya fara
kiran wayar Fateemah. Ita Ya kamata ta fara jin wannan kyakykyawan albishir D’in. Sanda ya sanar da ita
a ru’de ta ce “Moddi bana son wasa, Didin ce ta amince ba wani ja in ja.” Ya yi dariya mai sauti yana furta
“Ki zo Railway yanzu, don ki tabbatar.”
Yana zaunen bayan ya gama ha’dawa Didin kayan da zata buk’ata kamar su radio da sauran y’an
tarkacenta. Sai ga Didi ta dawo mak’ota fal a bayanta tana furta “Ai ina fa’da musu suka biyo baya na, Har
da masu kuka na dai sanar musu duk juma’a zan dinga zuwa nan don haka kada ka sake ka sab’a
alk’awari.” Moddi Ya jinjina kai yana furta “In sha Allah, gobe ma zan saka a zo duk a kwashe su, su je su
ga gida.” “Hakan ya yi.” Didi ta furta tana d’aukar radionta y’ar gado suka fita da Moddi, mak’ota na bin su
a baya Har da masu kuka. Sai da Didi ta shiga mota sannan suka watse suka bar wajen jikinsu a sanyaye
suna jin kamar wani sashe na unguwar gaba d’aya suka rasa. Ba abinda yafi zama da mak’oci lafiya…..
Haka suka isa sabon gidan Didi da hadimarta a bayan motar. Suka shiga babbar harabar gidan mai
tsananin kyan tsiya. Moddi yana jiran Ya ga tashin hankali a fuskar Didi sai bai ga komai ba illa zallar farin
ciki tana bin harabar gidan da kallo tana furta “Ma sha Allah, Jalla abin godiya idan ba Allah ba waye zai
yiwa Moddi haka? Dubi gida kamar ba na Moddi ba, Moddi da Ya sha gwagwarmayar rayuwa, idan baka
manta ba fa Har nik’a ka min a k’ofar gida.” Ya d’an turo bakinsa yana shiga gidan, duk wani tsoro da
taraddadi da yake zuciyarsa ya kau ganin Sam Didi bata damu ba, bai sani ba ko itama Safna ce ta rufe
mata baki ruf.
Part d’inta ya kai ta. Babban parlorn da Ya sha duk wani kayan jin da’di sai kuma k’arami guda da aka yiwa
adon tuntun kamar gidan sarakai. Akwai d’akuna biyu a gefe da gefen na Didin Wanda Ya ce na Imaan da
Amani ne tunda kin ce ba za’a musu aure ba…” tana dariya ta furta “K’warai kuwa, auren su ba yanzu ba
sai Sun sake wayo, amma menene dalilin hakan? Su ka rabu da su kenan? Saboda matarka?” Ya girgiza
kai. “A can ma akwai d’akunansu, ranar da ba kya nan sai su je can su kwana.” Ta jinjina kai tana furta
“Allah ya kyauta, su basu dawo ba ne?” Ya d’aga mata kai “Ke na fara kawowa sai gobe su kuma sai na
kawo su, Uwa ce gaba da kowa ai.” Farin ciki Ya tsarga a zuciyar Didi, ta dinga jin dama su dawwama haka
Moddinta Ya dawo kamar wancan Moddin mai so da k’aunar ta. A zuciyar ta tace In sha Allah, Allah zai
kawo wacce zata dawo min da Moddi na. Ta gyara zamanta tana sake nazarin gidan kyau kam iya kyau
gidan ya yi ba makusa. A hankali ta mik’e ta murd’a d’akin da aka ce na su Amani ne. Idanunta suka sauka
akan hotunan y’ar riga. Ta dinga bin su da kallo d’aya bayan d‘aya idanunta na son zubar da ruwa. Hoto
guda ta d’auka a hannunta ta k’ura masa ido ba zata manta ranar da aka d’auke shi ba, hoton ya tuna
mata da lokutan baya da yarda komai ya canja a yanzu don haka kawai ta zauna a gefen gado idonta a
lumshe yana zubar da hawaye tana tuno Uban Moddi da y’ar riga. Tarihin rayuwarsu ta baya ya dinga
dawo mata daki daki a kwanyarta……………
★★
Shekaru arba’in da suka wuce baya………
Jikar Nashe★✍️HADARIN GABAS……
NAZEEFAH SABO NASHE★✍️
22.
08033748387.
Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/Kztc35CmtLK45zM8fQmmSY
(Book 1 ne free Book 2 and 3 paid ne. Contact this number for subscribing…. 08033748387.)
BRIGHT PENS SECOND BATCH
★★★★Abubuwa da dama sun Faru a rayuwarsu, wasu tana Jin da’din tuna su yayinda wasu take Jin
bak’in ciki da k’una a cikin zuciyarta idan ta tuna su. Da gaske duniya juyi-juyi ce yau fari gobe tsumma
musamman ga y’an uwa irinmu talaka. Rayuwa ta yiwa iyalen Uban Moddibo zafi a wancan k’arnin kafin
komai yazo Ya zama sai labari….
Yaransu Shidda rigis mata, kafin samuwar Moddibo duk da suna son haihuwar namiji sai dai hakan bai yi
tasirin rusa soyayyar da suke yiwa yaransu mata ba. A basu da shi ‘din suka d’auki d’awainiyar karatunsu
tun daga primary har zuwa secondary. Malam Lami’do Uban Moddibo Sam kasancewarsa mutumin da,
da yazo daga Rugar fulani bai saka zuciyarsa ta jahilce shi wajen bawa yaransa ilimi daidai gwargwado ba
na addini da na boko. Dijatu ce babba sai Fateemah, Sa’adatu, Maryam, Kareemah da Jameela. Kafin su
samu cikin Moddibo a lokacin Dijatu da Fateemah sun zama matasan y’an mata masu kyau don duk
yaran Didi sai Allah ya taimaketa ya bata su kyawawan gaske. Sai dai bayan Haihuwar Moddibo da ya yi
Kama kwabo da kwabo da Fateemah sai aka ga Ashe ba wani kyau suke da shi ba, kyau kam mai suna
kyau sai Moddin Didi. Samuwar cikinsa Malam Lami’do Ya kwanta jinyar da ko tafiya baya iya yi, a haka
Didi ta dinga jinyarsa tana kuma kula da laulayin cikin da yazo mata da masifaffen laulayin da bata tab’a
ciki irinsa ba. A Daren da ta haifi Moddibo wani irin zallar farin ciki ta dinga gani a fuskar Lami’do Wanda
bai tab’a yi ba a duk sauran haihuwarta. Yasa a ka d’ora masa shi a saman cinyarsa yana binsa da kallo
murmushi d’auke a fuskarsa Ya furta Allah ya raya min Kai rayuwa mai albarka, Ubangiji yasa ka zama
sanyin idaniya a wajen mahaifiyarka da y’an uwanka, ni dai kam na San bana raye zaka tashi, da na nuna
maka kulawa da gata sosai Amma a hakan ma Alhamdulillah na San zaka Maye gurbina wajen kula da
k’annenka da mahaifiyarka, ina fata ubangiji ya baka managarciyar mace da zaka yi alfahari da aurenta….
Bayan gama masa addu’a ya sunkuya ka’dan ya masa hu’duba da Muhammad Moddibo.
A ranar Sunan Muhammad Moddibo a ranar Malam Lami’do Ya bar duniya. Tashin hankalin zuriyarsa kam
ba’a magana musamman Didi. Sun yi kukan rashinsa kamar ba gobe don duk da bai kasance mutum mai
wadata ba Amma yana daga cikin maza masu kula da ci da Shan iyali da suttura daidai gwargwado. Sanda
ya Mutu bai bar musu komai ba sai gidan da suke ciki. Tashin hankalin da Didi take ciki ya ninka na
yaranta ba don komai ba sai don tana tunanin ta inda zata fara. Duk da tana y’ar sana’arta ta siye da
siyarwa sai dai sana'ar ba inda zata Kai ta don sana’ar ma bata farata ba sai bayan da Uban Moddi Ya
kwanta ciwon ajali. Wannan tashin hankali da take ciki sai ya shafi har kula da Moddibo dole kulawarsa ta
koma wajen Fateemah ita ke masa komai idan har yaje wajen Didi to kuwa shayar da shi zata yi. Hakan ya
sanya wata irin shak’uwa a tsakaninsu kullum yana manne da jikin Fateemah da sunanta ya fara bu’de
baki zaka ga yana d’aga hannu yana kiran T T T. Hakan har yasa kowa ya koma cewa Fateemahn T. Dijatu
ma bai iya ba sai dai D D sai kawai duk sunan y’an uwansa Ya koma farkon sunan sa. Kulawar Didi gaba
d’aya ta koma kan Moddibo wannan Ya d’arsa jin haushinsa a zuciyar Dijatu idan har yaje kusa da ita sai
ta yakice shi musamman ganin yarda ya tashi a sangar ce, ga rashin tsoro da taurin kai. Idan za su yi masa
fa’da Didi ta hana. Abu guda da yasa yake sake shiga ran y’an uwansa tun bayan tasowarsa sai ya tashi da
tsananin y’an Uwarsa da Didi. Burinsa duk abinda ya je ya samo ya k’arar da su akan y’an uwansa. Idan
Didi ta ga haka sai ta yi murmushi ta ce “Allah yasa ka d’ore Har girman ka Moddi, Allah yasa ba zaka auri
matar da zata kawar da hankalinka daga wajenmu, Ubangiji yasa ka auri matar da zata taya ka so na da
y’an uwanka baki d’aya.” Tun bai San dalilin Didi na fa’dar haka ba sai ya turo baki ya ce “Ai Didi ba’a yi
macen da zata raba ni da ku ba, balle ma ni ba zan yi aure ba ina tare da ke, idan ma na yi ta ce zata raba
mu wallahi sakinta zan yi, bayan ina kallon irin wahalar da muke sha tare.” Didi Shafa kansa take a lokacin
ta ce “Allah yasa Moddi, na San Addu’ar Uban Moddi ba zata tafi a banza ba….”
Haka Ya taso namijin gaske da burinsa ya mayar da taro sisi. Burinsa ya fita ya samu ko ka’dan ne ya
kawowa Didi don yana jin haushin wahalar da jikinta da take wajen yin abincin siyarwa Kunu da k’osai da
safe. Da rana kuma shinkafa da wake. Da daddare ma ba zata huta ba zasu ‘d’ora kaskon wainar filawa
duk da wannan su Fatima ne suke yi a tsakargida Amma Allah ya sakawa neman su albarka duk sana’ar da
suka saka hannu a kai sai ka ga ta yi albarka. Shi kuwa Moddi duk ba ya son yaga suna wannan abin,
burinsa ya yi ku’di ya tallafi rayuwarsu don haka ya dage da Sana’a da karatun boko da na addini gaba
d’aya.
Sanda Fateemah da Dijatu suka samu Miji duka dangin Ubansu sai suka guje su suka juyawa Didi baya
Wanda a bayyana take ba don komai suka aikata haka ba, sai don basa son ta jingina musu wahalar
yaranta.