Showing 78001 words to 81000 words out of 87659 words
Chapter 27 - HADARIN GABAS Book Complete By Nazeefa Sabo Nashe.pdf
dai a idonta ya dinga hango tarin tsanarsa, a cikin idon ya hango zata iya kashe shi
saboda Jin haushinsa da take. Idanun Sun birkice zuwa wata color daban. Jingina ya yi da bango yana Jin
sautin kukanta yana kewaye kwanyarsa. Kuka ne da take yinsa da yake bayyana irin zafi da k’uncin da
zuciyarta take ciki. Idonsa kawai ya lumshe yana cigaba da Jin k’uncin zuciyarsa. Ganin tana shirin
shi’dewa ya yi saurin isa wajenta da niyyar kamata da sauri ta dakatar da shi ta hanyar sake rotsa masa
Abu a d’aya b’arin goshinsa. Bai damu ba ya yi saurin gocewa yana furta “Ki tsaya Ama… just wait, you
need help…” A fusace ta sake d’agowa sai dai idanunta basa gani sannan gangar jikinta ta yi rauni bata
da wani k’arfi sai na zuciya, don tana Jin zuciyarta kamar k’arfe tana Jin kuma zata iya aikata komai sai dai
sassan jikinta Sun k’i bata ha’din Kai. Don haka tana ji tana gani Dadan ya d’agata cak zuwa lallausa kuma
faffa’dan gadon. Zata yi masa gardama ya yi k’ura mata ido yana furta “Shsssh, relax.” Ta runtse ido kawai
tana Jin Amon muryar tasa a tsakiyar kanta. Muryar da da take son ji yanzu ba muryar data tsana saboda
ita. Wayarsa ya danna tana ringing Doctorn ya d’aga “Please ka zo railway akwai patient, come with a
nurse…” ya furta yana sake damk’e hannun Ama da take k’ok’arin fisgewa tana son ta mik’e. Tsuke
fuskarsa ya yi sosai ya ha’de rai yana kallonta ya furta “Ba zaki bari ba, me ye haka?” “Ka bari Dada ka
cuce ni. Wallahi na tsane ka, bana son kallonka kuma ma…” sai ta kuma rushewa da kuka. Fisgar leb’ensa
ya yi yana furta “Don’t forget bani na kawo ki ‘dakina ba, ke zan tuhuma me yasa kika zo? Me kika zo yi
min?” Sai ta rushe da kuka tana furta “Kai ne Dada, kuma ka sani Kai ne silar fa’dawa ta cikin wannan
halin kai kake tsafi da gangar jikina….” Turo k’ofar da aka yi ne yasa ta ha’diye sauran maganar. Ganin
Umma T ce yasa Moddi mik’ewa fuskarsa a ‘daure ya koma gefe yana kallon Umma T ‘D’in da tata fuskar
tafi ta shi d’aurewa, idanunta Sun yi jajir ta kau da Kai tana kallonsa…. Sai kuma ta cije bakinta ta fara
magana k’asa k’asa… “Fita waje Moddi.” Ya yi kamar bai ji ta ba kamar ba zai fita ba, sai kuma ya fitan.
Umma T. Ta nufi toilet ranta duk a jagule. Ruwa mai zafi ta ha’da mata sannan ta fito. Hannu kawai ta
saka ta mik’ar da Amanin tsaye. Da sauri Amanin ta saka k’ara ka’dan. Tausayinta ya kama Fateemah
amma ta cije tana furta “Wannan ne kawai gatan da zan miki, a yanzu kam Ban San me zan ce miki na
rarrashi zuciyarki ba, cuta dai Safna ta riga ta yi mana ita wacce ba Wanda zai iya warkar da mu.” Ta fa’da
suna shiga toilet ‘din. Towel k’arami ta mik’a mata tana furta “Ki cire kayanki ki shiga cikin ruwan can, shi
zai saka ki warware jikinki ya daina ra’dadin da yake.” Amani kamar ta zunduma ihu haka take ji. Don dole
ta runtse idonsa ta shiga cikin ruwan wani bak’in ciki na ratsata ta sha mafarkin hakan Amma ga mijinta
na halak ta sha mafarkin wannan ranar da yarda mijinta zai lallab’a ta idan hakan ta kasance, sai gashi
lamarin yazo mata a abinda zata kira mummunar k’addara. Umma T ta juya tana furta idan ya salamce sai
ki tara wani ki yi wankan tsarki. Amani ta lumshe ido hawaye suna sake zubo mata kamar da bakin
k’warya.
Fateemah tana fita daga toilet ‘din ta fita parlor, itama nata idanun hawayen suke zubarwa, da gaske tana
Jin wani irin ciwo a zuciyarta, sai take ga kamar Sun ci amanar mahaifiyar yarannan Sun ci amanar Y’ar
riga. Me yasa Moddi ya kasa hak’uri da aka hana shi auren Safna, ya turje ya dage sai da ta aurota ba tare
da amincewarsu ko na Didi ba? Y’ar riga suka so, suka kuma yi masa sha’awar zama matarsa ba don
komai ba sai don kyawawan d’abi’unta. Ta tuna ranar da suka je Kai kayan lefen aurensa, bai sani ba bai
San ana nema masa aure ba. Su kansu iyayen y’ar riga basu sani ba sai da suka je, a take a wajen
Mahaifinta ya ce ya basu aurenta, bai b’oye musu ba ya sanar da su y’ar riga bazawara ce ta tab’a aure,
sai dai auren da wata guda Mijin ya mutu ta hanyar hatsarin mota. Basu wani ji komai ba Sun San Didi ba
zata k’i ba suka bayar da kayan aka kuma saka rana sati biyu. Sanda suka sanar Didi ai y’ar riga bazawara
ce cikin murmushi ta ce “Shikkenan sai Moddi ya raya ingantacciyar sunna, Manzon Allah ma da
bazawara ya fara…” a haka aka nema masa auren, bai sani ba har sai ranar d’aurin auren da aka gaya
masa aka kuma sanar da shi da y’ar riga aka d’aura. A take a wajen ya tubure ya kuma rantse baya sonta
me zai yi da ita gashi an sanar da shi bazawara ce… “ ta saki ajiyar zuciya Jin taku a bayanta, hakan ne ya
dawo da ita daga duniyar tunanin data shilla. Idanu ta zubawa Kiddo ganin likita a bayansa. Fuska a
‘d’aure ta masa filatanci don bata son likitan ya fahimci abinda take fa’da… “Baka da hankali ne Moddi,
tona mana asiri kake son yi? To ba zai duba ta ba ka ja shi ku koma, tun kafin ranka ya b’aci. Oo walla
hakki…” ta cigaba da masifa da filatanci. Moddi dai yana jinta bai ce komai ba, ya ja hannun Doctorn
suka fice. Sai da taga fitarsa sannan ta ja ajiyar zuciya tana jin yarda zuciyarta ke zafi. bedroom D’in ta
koma suka sake fitowa da Amani da take taku a hankali. Sashen Didi suka shiga daf da asuba. Didi na
kwance ta dinga bin Amani da kallo kafin ta lumshe ido ta d’aga hannu alamar tana kiran Amanin.
Amanin ta k’arasa wajenta ta shige jikinta. A tare suka saki ajiyar zuciya da Didin suka kuma saki kuka a
tare. Didi ta dinga Shafa mata kai tana furta “Ki yi hak’uri kin ji Magajiya, sannan kuma ki yafewa
Moddibo duk da bai cancanci yafiyar a wajenki ba, na San da ciwo Amma don Allah kada ki fitar da
wannna sirrin don fitarsa kamar tonuwar sirrin ki ne, don Allah ki rufa mana asiri ki rufawa kanki asiri…”
Ama kuka Kawai take tana jin zuciyarta na zafi. Me yasa Didi zata ce kada ta fitar da wannan sirrin? Me
yasa bata son ta tonawa Moddi asiri? Akwai adalci akan hakan? Ita bata k’i ta tona asirin ba abu guda ne
ta San ba zata samu Mijin aure ba to sai me? Dama ita bata jin zata yi aure a duniyar nan. Fateemah ta
zauna a gefenta itama. Hannayenta ta kama ta saka cikin nata tana matsa su a hankali. “Ba wai don
Moddi muka ce ki rufa wannan maganar ba, sai don kan ki Ama.” Ta fa’da cikin murya mai cike da sanyi.
“Ki rufa mana asiri yarda daga ni sai ke sai Moddi Safna, Didi da Iman ne muka San maganar nan to don
Allah ki barta a iya mu ‘din, hakan shine alheri a wajenki.. kin ji My daughter?” Amani ta ha’diye wani abu
da ya tsaya mata a mak’ogaro kafin ta sake sakin kuka, bata jin har abada zata iya rufawa Moddi asiri,
dole sai ta sanar da duniya waye shi? Uban da ya yiwa y’arsa fya’de saboda son duniya. Fateemah ta
kwantar da ita a saman gadon Didin bayan ta tilasta mata shan maganin pain reliever. Shiru ta yi kawai sai
dai ba barci take ba, sak’a da warwara zuciyarta kawai take mata. Kiran sallahr da ake ne ya saka su Didi
mik’ewa daga zaman jigum da suke suka fara shirin sallah. Sai itama ta samu kanta da tashi ta yi
sallahr….
Yana idar da Sallah ya nufi sashen Didi. Fuskarsa fayau kamar Wanda ya tashi daga zazzab’i. Fargabar jiya
ce kawai ta saka idanunsa suka fa’da ciki. A hankali yake taku hannunsa rik’e da counter yana matsawa a
hankali. Ya yi sallama cikin k’asa da muryarsa kafin ya tura k’ofar ‘dakin. Da sauri Amani ta runtse idonta
bata son ganinsa sam. Didi ma ‘d’auke masa kai ta yi, ta cigaba da laziminta tana fatan Allah ya rinjayi
zuciyarta daga tarin fushin da yake cikinta kada ta yiwa Moddibo baki. A kasalance ya zauna a k’asan
carpet d’in. Idanunsa a k’asa ya hau furta “Mun tashi lafiya Didi?” Shiru Didi ta yi, tana hak’ilo da
zuciyarta wajen ganin ta togace kanta daga samba’da wa Moddin zagi. Ya sake maimaitawa still bata
amsa masa ba har sai da Fateemah ta ji tausayinsa ta ce “Didi yana gaishe ki?” A fusace Didi ta ce
“Fateema kada kice min kina goyon bayansa? Kada kice min tausayinsa ki ke?” Fateema ta hau girgiza kai
“Ko ka’dan Didi, ai girman laifinsa ba zai bari a ji tausayinsa ba ko ka’dan, ai aikin gama ya riga ya gama sai
dai ai fatan Allah ya kiyaye na gaba…” Kallon Didi ta zuba mata ne yasa ta yi shiru sai kuma taga Didin ta
mik’e idanunta jajir a kansa ta furta “Moddibo!” Da sauri ya ‘d’aga kai yana mamakin Amon muryar da
tayi amfani da shi wajen kiran sunansa…. Bai san sanda ya samu kansa da furta “Ki yi hak’uri Didi….”
Kallon da ta masa ne yasa shi ha’diye sauran maganarsa. Kallo ne mai nuni da garga’di gare shi, a idanun
Didi yake hango yarda take jin haushinsa. Muryarta a fisge ta ce “Ba zan maka baki ba Moddi, ba zan ce
jeka ka gani ba, zan maka addu’a Allah y’a shiryeka, Allah ya dawo da kai kan tafarkin sira’dil Mustak’ima.
Amma ba zan iya zama a gidanka ba, ba zan iya zama inuwa guda da kai da matarka ba, zan tafi zan tafi
zan koma gida na idan ba ina so zuciyata ta buga ba ne, sai dai zan gaya maka zan aurar da yaran nan zan
aurar da marayun Allah, tun kafin mutane su farga su k’i aurensu, kuma tare da su zan tafi. Allah ya
shiryeka shine kawai addu’ar da zan maka.” Ta fa’di tana k’ok’ari sosai wajen ganin k’wallar ta bata zuba
ba. Moddi kasa cewa komai ya yi, to me zai ce? Yana kallonta ta fara shirya kayanta. Ya runtse idonsa
kawai yana son yi mata magana, irin maganar da zata kwantar mata da hankali, amma harshensa ya gaza,
Ya kasa bashi ha’din kai don haka kawai sai Ya kifa kansa a hannun kujera ya yi shiru kawai. Fateemah ce
ta katse shirun nasu ta hanyar furta “Amaryarsa fa Didi? Amaryar da aka ‘d’aura musu aure? Yaushe zata
tare?” Didi ta gintse fuskarta tana nuna Fateemah da yatsa ta furta “Ki shiga hanaklinki Fateemah, ki
kuma fita hanyata matuk’ar maganr Moddi ce zata ha’da ni da ke, bana so bana so ki sake jefa ni cikin
zancen Moddibo, Ya je ya yi abinda yake so, Ya aikata abinda duk abinda yake so, na daina ba shi umarni
tunda ba bin umarnin nawa yake ba.” Shiru Fatima ta yi bayan ta furta “Ki yi hak’uri Didi.” Moddi kuma ya
mik’e waya a kunnensa. Basu San me yake cewa a wayar ba don muryarsa ta yi k’asa da yawa. Fateema
dai ta bi shi da kallon k’asan ido, gefe guda na zuciyarta na jin wani irin tausayinsa.
A bedroom d’inta Ya sameta. Tana zaune hannayenta zube a k’uncinta. Ta d’ago tana kallonsa da sauri ta
janye idonta don ba zata jure kallon birkitattun idanunsa ba, Sun canja sun zama wata kala daban mai
razana zuciya… taku Ya yi na k’asaita ya shiga cikin ‘d’akin sosai. Idanunsa a kanta ya furta “Burinki Ya
cika ko? Sai ki gaya min kuma next abinda zan yi, bana son maganar nan ta fita, ba kuma wai ina rok’onki
ba ne, Aa umarni nake baki, idan kuma kin k’i…” sai ya ciza leb’ensa ba tare da ya furta komai ba. A
fusace Safna ta ‘d’ago tana kallonsa “Idan na k’i me? Na ce idan na k’i me zaka min Moddibo? Saki na za
ka yi ko? Na San shine abinda kake so….” Sai ta tuntsire da dariya “Saki na shine abu na k’arshe da zaka yi
regretting ‘d’insa a rayuwa wallahi, don kana saki na zan bayyana wannan vedion a duniya na rantse da
Allah ba Wanda zai hana ni, a yanzu ma idan baka amince ka yi min abinda nake so ba, sai na saki vedion
nan…” Kallonta yake sosai, yana taune lips ‘dinsa. Ya sunkuya daf da ita yana furta “Me kike so na Miki?”
Cikin wata irin murya da ta yi k’asa sosai. Safna ta ji muryar na nemar d’auke mata numfashi ga k’amshin
turaren da ya baibaye mata hanci, sai ta ji tana neman ta rasa hankalinta. Sai da ta yi da gaske sannan ta
fisgo muryarta da bata da amo sam ta furta “So nake ka saki matar da ka aura Jiya…..”
JIKAR NASHE★✍️HADARIN GABAS…..
32.
NAZEEFAH SABO NASHE★✍️
08033748387.
BRIGHT PENS SECOND BATCH
★★
Wani irin kallo yake mata,kafin Ya furta “Na saketa fa kika ce?” Ta ‘d’aga kai tana furta “Eh, ka saketa na
ce, idan Har kana son na rufa maka asiri…” Sai ya cije lips d’insa ya furta “Idan ina so ki tona fa?” “Kada
ka saketa, ka sha mamaki, wallahi a yau zan saki vedion nan.” Ya waro ido yana furta “Wai da gaske kike
za ki iya tona min asiri?” “Me zai hana?” Ta fa’da tana jijjiga jikinta… “Shikkenan, zan saketa, ba dai
matar da Didi ta aura min ba, ki je ki samu Didin idan ta amince min a yau ma ba sai gobe ba zan saketa,
don dama ba wani son yarinyar nake ba, sau ‘d’aya na tab’a ganinta kinga idan kika saka na saketa kin
taimaka min zama da abinda bana so…” Farin ciki ne zalla ya cika zuciyarta, ta dinga jin zuciyar na wani
irin kumbura tsabar murnar da take ciki. Ashe har yanzu ita take da Moddi ita Moddi yake so ba wata
banza ba can, ashe zata iya tursasa Moddibo Har yanzu. Sai ta samu kanta da b’acewar b’acin ranta, farin
ciki fal Ya cika zuciyarta. Sai ta mik’e kawai tana yafa d’an mayafinta ta fita zuwa sashen Didin. Moddi ya
bita da ido yana girgiza kansa. Lamarin Safna mamaki yake bashi, ta yarda take nuna son kanta tsagwaron
sa, in dai zata samu farin ciki ba ta k’i kowa ya rasa nasa farin cikin ba. Ji ya yi yana son yaga drammerr da
za’a buga da Didi da Safna don haka yaga bari Ya je, duk da idanunsa basa son ha’duwa da Didin ba don
komai ba sai don b’acin ransa da yake gani a idon nata, da gaske ya san Didi na jin haushinsa. Sai ya cije
leb’ensa hannayensa zube a aljihu ya nufi sashen Didin.
A zaune ya gansu, Fateema har a lokacin tana zaune hannayenta zube da k’uncinta. Sai ya ji tausayinta ya
mayar da kallonsa kan Amani da Imani da suka yi wani irin zuru zuru. Idanunsu Sun fa’da sun kuma nuna
alamun Sun ci kuka sosai. Ya zauna yana sakin ajiyar zuciya ba tare da ya yarda ya yiwa Didi second look
ba. Ba zai jure ba, ba zai jurewa yanayin kallon da take masa ba. Kowa Safna take kallo da take zaune
k’afa ’d’aya kan d’aya. Tana wurga musu wani irin kallo tana taunar chewingum. “Didi wajen ki na zo.” Didi
ta zuba mata ido ba tare da ta ce komai ba, don a Yanzu bata ganin lefin Safna komai ta yi Moddi ne ya
jawo mata. “Yauwa Didi, dama a kan maganar nan ne, idan Har ba so kuke maganar ta fita waje ba, ina
son Moddi ya saki matar da kika aura masa jiya….” Kowa ya ‘dago yana wurga mata wani irin kallo. Ta
girgiza k’afa tana furta “Haka nake so a yi, idan ba haka ba zan saki vedion nan wallahi a gari, don duk
abinda suka aikata jiya da y’ar cikinsa ina da recording d’insa, kamar na San akwai abinda Imam yake
aikatawa na saka k’aramar camera a d’akinsa ba tare da Ya sani ba, sai gashi kuwa ashe yana aikata
abinda nake zarginsa d’in. Didi idan baki sani ba ki sani akwai wani sirri bayan wannan da Moddi yake
aikatawa, akwai d’akin sirrinsa da baya bari kowa Ya shiga, idan kuma ya ce ba haka bane ya bu’de ku
shiga ku gani….” Wani irin kallo Didi ta zubawa Moddibo tana jin hankalinta yana sake tashi, da gaske
Moddi yana shirin bugar mata da zuciya. Moddin cikin takaici yake hararar Safna. Fateemah kuwa runtse
idonta ta yi ta dafe k’irjinta tana fitar da wani colorr numfashi. Amani kuwa ta dinga jin zuciyarta na
tsananta bugu. Idanunta akan Dadan tana son taga ko zai musa. Sai dai ko ‘d’aga kansa bai yi ba. Kan nasa
yana sunkuye a haka yake kallon kowa. “Tashi mu je ka bu’de min d’akin Moddibo, idan baka naso yau na
maka abinda baka tab’a zata ba…” Runtse idonsa Ya yi yana girgiza kai. “Ki yi hak’uri Didi, shigar ki d’akin
bashi da wata fa’ida, don Allah ki yi hak’uri.” Zubewa kawai ta yi akan kujera wannan karan sam ta kasa
togace hawayen da suke zubo mata… ta saki kuka sosai tana furta Ya Allah! Safna ta mik’e tana sakin
murmushi tana kallon Fateemah da ta zama kamar statue. Sai ta kai wayarta daidai fuskarta ta furta “Ke
kin san komai, kin san Moddi ya cusawa y’arsa k’aunarsa da sha’awarsa ta hanyar tsafi, kin ga abinda kika
gani a wayarta, sannan ga vedio, idan baku saka ya saketa ba