Showing 15001 words to 18000 words out of 80926 words
Ammin ta da Abeeh duk likitocine shiyasa suke
zaune a Turkey suna aiki , Yaran su biyu suka haifa Asuk' da Rauda suna bala'in k'aunar
'yayansu...
Suna k'arasawa gidan su Rauda aka fara murna da zuwan Sanam , duk wanda yake
Family d'in su Rauda sai yasan Sanam saboda shak'uwar su , Ammi tana murmushi tace "
oyoyo my dauther , Sanam tafad'a jikin Ammi tana fad'in " nayi kewarki Ammi dakuma kewar
daddad'an girkin ki , dariya suka saka baki d'aya Ammi " tana fad'in " kwantar da hankalin ki
indai girki nane gashi can a dinning yana jiranki tund'azu , da sauri Sanam ta nufi dinning tana
fad'in "dama yunwa nakeji banci komai a cikin jirgi , tana zuwa ta janyo kujera ta zauna tana
cewa Rauda " zokiyi serving d'ina yunwa nakeji , Rauda ta nufo wajen tana fad'in " girman kine
ai dole nazo nayi .......
Huneed yana zuwa gida yafara shirin tafiya , Hajiyar su yaje yiwa sallama yana fad'in "
tafiya ce tazomi zuwa k'asar Turkey amman ba jimawa zanyi ba , Hajiya tayi masa addu'ar Allah
yatsare shi yayi mata sallama ya fito , wayar Hisham ya shiga kira yana sheda masa tafiya tazo
masa zai tafi Turkey amman ba jimawa zaiyi ba , zai saka masa kud'i a Account saboda ko zasu
buk'ata shi da Hajiya , Hisham yayi masa fatan Allah yatsareshi sannan sukayi sallama ,
Huneed yashiga motar sa yabata wuta ya nufu airpot , yana zuwa visar sa na fitowa aka ce
masa zuwa yamma jirgin su zai iya tashi ..........
Bayan Sanam taci abinci tanufi d'akin Rauda ta fad'a toilet tayi wanka , tana fitowa Rauda
ta shigo tana fad'in " kinsan mungama shiryawa ke kad'ai muke jira , Ammi cewa tayi wai mutafi
mubarki ki huta tunda yanzu kika zo ya kikagani , Sanam tana shafa mai tadubi Rauda tace " ai
babu gajiya atare dani kawai kujirani insa kaya sai nafito mu wuce dan inaso inzaga gari tunda
nadad'e banga garin ba , Rauda tajuya tanufi fita tana fad'in " muna jiranki cikin motar sai kin fito
, Sanam tana gama shafa mai tasa kwalli daman bawata kwalliya tacika yiba , kayan ta ta bud'e
ta d'auko wasu riga da wando bata tab'a sasu tasaka abinta , ta d'auko filet shoe da hand bag
d'in ta iri d'aya , sai wani k'aramin gyale ta yafa ta fesa turare me tsadar gaske , agogon gold
d'in ta ta d'aura a tsintsiyar hannun ta ta fito ....
Tana zuwa falor sukayi karo da Asuk' yayan Rauda , da kallo yabi Sanam tamkar tsohon
maye har wani kashe ido yake , tana k'arasowa tayi tamkar bata gansa ba dan dama tuntuni
haka suke kowa naji da miskilan cin sa , wanda ma yanzu Asuk' shi ya sauko bakamar da ba ,
har ta gifta yace " manyan mata saukar yaushe ? Sanam batare da ta juyowa ba tace " saukar
d'azu dafatan kana lafiya , daga haka bata jira cewar saba ta fice abinta , da kallo Asuk' yabi
k'ugunta cikin ransa yana kiyasta yadda zai sarrafa ta mutuk'ar tashigo hannun sa , wani
murmushi yayi tare da shigewa cikin d'akin sa....
Sanam tana fitowa k'awayen Rauda suka bita da kallo suna fad'in " wow so beautifull lady ,
wani murmushi Sanam tayi tana wani jin kanta , dan dama burin Sanam arayuwa ayabi kyanta
sannan a girma mata , tana k'arasowa tace " My R nice fa zanyi drivernig dan inaso asan
Sanam tazo garin Turkey yau , Rauda tayi murmushi sannan tace " wato haryanzu wannan
halin naki yana nan nasan gudu sosai a motar ? Sanam tana ansar mukullin motar tana cewa "
mezan fasa haryanzu yana nan kuwa , dukansu suka shiga mota Sanam taja da wani mugun
gudu suka fita .......
Huneed sai hud'u sannan jirgin su yataso zuwa Turkey , yana cikin jirgi yafara tunanin ko a
inah Sanam ta sauka ? tabbas zaiyi bincike sosai har sai yagano inda tasauka , sai wajen k'arfe
goma suka sauka a airpot d'in k'asar Turkey , suna isowa yasauka a wani Babban Hotel dake
cikin garin , sai da yagama kintsawa sannan yafito ganin gari , dan yasan sai dare ake fitowa
yawo a k'asar Turkey , kuma yana da tabbacin lallai Sanam zata fito ganin gari itama , yana
fitowa ya nufi shopping d'in k'asar wanda akeji dashi sosai , yana zuwa wajen shiga yaji
k'amshin turaren Sanam , tabbas wannan turaren yasan Sanam ce take sakashi kuma yana da
tabbacin tana wajen , bai gama tunani ba yagan su sunfito ita da k'awayen ta suna wata
mahaukaciyar dariya , da sauri ya b'oye a jikin bishiya dan bayason tasan yazo garin yanzu har
sai ta saki jiki zai bayyana mata kansa yazo , yana hangosu suka shige motar kuma itace ta
zauna a b'angaren tuk'i , da sauri ya tsaida motar ya hau yana fad'in " kabi mun wannan motar
dake gaban mu duk inda tayi , da turanci yayi maganar direban yafara bin motar su Sanam ,
wani gudu tashiga yi tamkar zasu tashi sama , shima direban binsu yashiga yi da gudu yana
fad'in " wannan gudun yayi yawa sosai , Sanam tuni tashiga wana motar tamkar wacce ta sha
k'waya take tangad'i , Huneed wani takaici ne ya rufe sa cikin ransa yake fad'in " wato wannan
yarinyar bazata gyaru ba kenan ? a k'asar da bata ta ba ma saita yi musu wannan iskancin nata
, tabbas zata gane shayi ruwa ne dan sai ya koya mata hankali wannan lokacin .........
*Comment* plss
*'Yar Mutan Kanawa* _Ce_
[9/26, 21:04] Muhammad Karim: *'YAR* *KISHIYA*
_Rik'on Me Hak'uri_
♀️♀️
*NA*
*Zee* *MD*
*Hamdala* *Writer's* *Association*
https://www.facebook.com/111403834371046
✨✨ *{{* *H.W.A* *}}*✨✨
*Bisimillahir* *Rahamanir* *Rahim*
Chapter 12.
Allah ne kawai yakai su Rauda gida lafiya , dan dukansu sai da suka jigata da tuk'in da
Sanam takeyi , suna fitowa kowannen su ya fara tari na wuya , ita kuwa dariya ta dunga yi musu
tamkar wata zararriya , bayan sun lafa da tarin da sukeyi wata daga cikin k'awayen Rauda tace
" a gaskiya kina da matsala bazan k'ara shiga motar ba mutuk'ar kece zakiti driver , Rauda tace
" wai dama har yanzu Sanam baki daina wannan gangancin naki ba kenan ? wallahi sanake in
kika k'ara girma zaki dai na ashe ba haka bane abun , Allah ya shirya ki wallahi nan k'asar ba
kamar Nageria bace kidaina kar aka maki , murmushi Sanam tayi tare dayin tsalle ta haye
saman motar ta dube su tace " babu ruwana da nan Nageria ce ko ba Nageria ba dole nayi
yadda nake so a duk inda naje , matsora ta kawai duk kun wani firgice wlh kunbani dariya ,
haushi bai sa sun k'ara mata magana ba suka shige sukayi tafiyar su cikin gida......
Sanam na zaune a samon motar wayar ta ta soma ruri , d'auko wa tayi tana duba screen
d'in wayar dan ganin waye yakira ta , Daddyn tane da sauri ta d'aga wayar tana fad'in " Miss u
my luvly Daddy , shima cike da k'auna yace " My Dauther dafatan kin sauka lafiya ? lafiya lau
Daddyna ina Mumy na take ? Alhaji Abba yace " ina gidan d'aya Mumyn naki gata ku gaisa ,
daman baki mata sallama ba kika taho , dan danan Sanam ta turo baki tamkar tana ganin su
tace " Daddy nifa bance kabata wayar ba kasan ba sona takeyi ba , Hajiya Maimuna da wayar
take a kunnen ta tuntuni ji tayi maganar ta doke ta , cikin ranta tace " duk wanda zai soki a
duniya bayana yake , nice wacce na d'auki cikin ki har na haifeki kika girma kika zama hakan ,
Maganar Sanam d'in ce ta katse ta daga tunanin datake tace " ba Daddyn naki bane nice ,
Sanam cike da jin haushi tace " kinyini lafiya ? Hajiya Maimuna tayi murmushin takaici wai 'Yar
da ta haifa ce keyi mata irin wannan gaisuwar , kashe wayar tayi batare da ta ce uffan ba ta
mik'awa Alhaji Abba wayar sa tamik'e tabar gurin .......
Sanam najin Hajiya Maimuna ta kashe wayar ta tab'e baki tare da fad'in " huta roro ,
saukowa tayi daga kan motar ta nufi cikin gidan Itama ......
Duk abinda Sanam keyi Huneed na tsaye yana kallon ta , har ta shige cikin gidan sannan
yasa me taxi ya maida shi hotel d'in daya sauka , koda ya koma hotel d'in band'aki ya shiga
yayi wanka sannan ya fito ya anso abinda zai iya ci yadawo , yana cin abincin yana tunanin
yadda zai gyara Sanam tunda ya fahimci batajin magana sosai , haka ya gama batare da ya
yanke me zaiyi mata ba ya kwanta dan ya huta......
Washe gari..
Yau akeyin Bridel Shower dan haka tunda suka tashi suka fara shirye shirye , Sanam na
zaune sai faman chat take da Diyana suna labarin k'awayen su , sai wajen k'arfe biyu ta tashi
tayi wanka sannan ta fito ta shirya cikin wata riga wacce suka d'inka duk iri d'aya , sosai kayan
sukayi mata kyau dan dama Sanam akwai kyau na tamkar itace ta k'era kanta , gashin ta
dayake a baje a gadon bayan ta ta kamo tasa masa ribon kalar rigar data saka , sannan ta saka
wani hils d'in takalmi me tsinin gaske , kwalliya bata dami Sanam ba sai dai tana saka kwalli
wanda ke k'ara fito da kyawun idanunta masu kama da madara , fitowa tayi palor tuni mutanen
dake zaune cikin falor suka saki bakin kallon ta , Ammin Rauda tana duban ta tace " wow my
Beautifull queen , murmushi Sanan tayi wanda siririyar wushiryar ta ta fito tare da dimple d'inta
ya lotsa , ai take suka rud'e sai cewa suke " wow so beautifull nice , aikuwa Sanam tasamu
abinda takeso wato a fasa mata kai ace tana da kyau , wani yauk'i tashiga yi har ta fito harabar
gidan , lokacin Abokan Ango sunfara zuwa d'aukar su dan kaisu wajen Party , suna ganin
Sanam kowanne ya kafeta da ido suna k'arewa k'ugunta kallo da k'irjin ta , wanina ciki yace "
wannan Babyn ta had'u sosai dama zata yarda tabani dare d'aya dana mallaka mata duk
abinda takeso , dukan su suka shiga yabon halittar Sanam wacce ta tsaya gefe d'aya tana
danna waya da alamar kiran wani zatayi .......
Huneed tunda gari ya waye ya shirya ya shiga gari , sai wajen biyu da rabi yasamu kansa
da son zuwa gidan da Sanam ta sauka , dai dai lokacin dayazo a dai dai lokacin Sanam ta fito
da wannan shiga , bayan wata bishiya ya lab'e ya saka face mark d'in sa da glass yana lek'owa
, ganin yadda maza ke kallon Sanam hakan ya kuma b'ata masa rai over , cikin ransa yace "
wai wannan yarinyar anya mutum ce kuwa ? sai kace shaid'aniya zatayi irin wannan shigar ,
tamkar ma ba musulma ba dubi jikinta ko d'ankwali bata saka ba , Asuk' ne ya fito daga motar
ya nufo wajen Sanam , tana zuwa yayi hugging d'in ta batare da ta kula dashi ba , tuni mutanen
dake gurin suka fara yin tafi suna jinjina masa yadda yayi hakan , Huneed nadaga bayan
bishiya jiyayi juwa na neman kamashi , wani abu yaji ya tokare masa a k'irjin sa tamkar
numfashin sa zai tsaya haka yaji , Sanam jin yadda Asuk' ya rungume ta yasa ranta yayi
mugun b'aci , k'arfin ta ta had'a guri guda ta hankad'ashi gefe , tana yin hakan tayi saurin
komawa cikin gidan dan yagama b'ata mata rai over , Asuk' sosai yaji haushin abinda tayi
masa dan har bige kansa yayi jikin motar , dan haka shima cikin gidan yabita.......
Huneed take ya yanke shawarar mutuk'ar Sanam tafito to sai ya d'auke ta , dan ya fuskan
ci wannan guy d'in zai iya yimata komai yadda ya fusata , kuma shima bazai so ace ko d'an
yatsan ta wani banza yasake rik'ewa ba , haka ya zauna zaman jiran fitowar ta , yana zaune
motoci suka fara wucewa dan tafiya gurin Kamu , kwata kwata bai ga Sanam ta fito ba har ya
tashi yafara nufar cikin gidan dan ganin me takeyi , lokacin kowa yatafi wajen party har Ammin
su Rauda da k'awayen ta itama , ita kuwa Rauda dama tuni suna can ana shirya ta daga can
za'a wuce sa ita , yana tsaye yana kai kawo a harabar cikin gidan sai ga Sanam da gudu ta fito
tana kuka rigar ta duk ta yage ana ganin jikinta , bayan ta Asuk' ne daga shi sai gaje ran wando
ya biyota da gudu shima , wajen Huneed ta nufo tana fad'in " dan Allah ka taimaka min wallahi
d'an iska ne , wani mari Huneed ya tsinka mata sannan ya janyo hannun ta ya kawo ta wajen
Asuk' dake tsaye yana kallon su yace " gatanan kayi mata duk abinda kakeso kayi , mamaki ne
yaka ma Sanam tafara Nazarin a inah tasan wannan muryar ? Asuk' ya rik'e hannun ta tare da
cewa " Huneed thank u Yana k'ok'arin janta ya shigar da ita cikin gidan , kwata kwata Sanam
bata ceton kanta take ba so take ta tuna muryar waye wannan dan tabbas tasan muryar kuma
taji ta ba sau d'aya ba , juyawa Huneed yayi yana dafe kansa yayin da Asuk' yake jan hannun
Sanam zai shiga da ita cikin gidan , ita kuma tana wai wayen Huneed tana son sanin waye shi ?
gab da zasu shiga k'ofar falor Huneed yace " Stop dawata murya wacce tasa dukan su suka
firgita , tuni Asuk' yasaki Hannun Sanam yana duban Huneed wanda ya nufo su gadan gadan
tamkar zaki , yana zuwa yashiga duka Asuk' yana fad'in " rungumar da kayi mata baiyi ba sai
ka ai ga keta mata haddi , mara tarbiya kawai wawa jaki , sai dukan sa yake tamkar zautacce
haka yakoma , tuni ya sumar da Asuk' sannan ya waiwayo kan Sanam wacce tagama tsurewa
jikin ta sai rawa yake , yana zuwa yajanyo hannun ta batare dayayi magana ba har suka fita
daga gidan suka nufi titi , tunda ya rik'e mata hannu ta tuno da ko waye , Huneed bai saki
hannun Sanam ba har sai da suka isa Hotel d'in dayake suka shiga har cikin d'akin daya kama
...........
*Comment plss*
*'Yar Mutan Kanawa* _Ce_
[9/27, 09:44] Muhammad Karim: [9/26, 21:04] Muhammad Karim: *'YAR* *KISHIYA*
_Rik'on Me Hak'uri_
♀️♀️
*NA*
*Zee* *MD*
*Hamdala* *Writer's* *Association*
https://www.facebook.com/111403834371046
✨✨ *{{* *H.W.A* *}}*✨✨
*Bisimillahir* *Rahamanir* *Rahim*
Chapter 12.
Allah ne kawai yakai su Rauda gida lafiya , dan dukansu sai da suka jigata da tuk'in da
Sanam takeyi , suna fitowa kowannen su ya fara tari na wuya , ita kuwa dariya ta dunga yi musu
tamkar wata zararriya , bayan sun lafa da tarin da sukeyi wata daga cikin k'awayen Rauda tace
" a gaskiya kina da matsala bazan k'ara shiga motar ba mutuk'ar kece zakiti driver , Rauda tace
" wai dama har yanzu Sanam baki daina wannan gangancin naki ba kenan ? wallahi sanake in
kika k'ara girma zaki dai na ashe ba haka bane abun , Allah ya shirya ki wallahi nan k'asar ba
kamar Nageria bace kidaina kar aka maki , murmushi Sanam tayi tare dayin tsalle ta haye
saman motar ta dube su tace " babu ruwana da nan Nageria ce ko ba Nageria ba dole nayi
yadda nake so a duk inda naje , matsora ta kawai duk kun wani firgice wlh kunbani dariya ,
haushi bai