Showing 15001 words to 18000 words out of 99112 words

Chapter 6 - Mijin Marigayiyya Part Complete Hausa Novels.docx

17 Sep 2025

69

ba.

Can wajen 2pm suna zaune a parlor gaba dayansu aka buga gate. Da kansa ya tashi yake ya bude, jimawa kadan ya shigo Ummin tana biye da shi.

Ya koma ya zauna a inda ya tashi.

Ummi na shiga gidan Shukra ta tashi da gudu ta rungumeta tana cewa ‘Ummi na tsefewa Baby na kanta yau ita Zaki yiwa kitso.’

Ta dauketa ta mika mata hannu suka tafa tana cewa ‘Yauwa kawas, bari nayi sauri na gama shara mu zauna kitso don babynki anti yalash ce.’

Ta sauketa tana ta murna.

Ta rage tsawo ta gaida Khadeeja, har zata shige kitchen Khadeejan tace ‘Shine baki zo da wuri ba yau Ummi? Gashi annfara azumi.’

'Wallahi Anti cikin gari muka shiga.’

Da mamaki tace ‘Ke Ummi ana lockdown din kike fita.’

'Yo Anti ai mu a kasa muke yawonmu, babu inda bam zuwa.’

'Ai kuwa za a kamaku Ummi ko ku kwaso cutar da ake gudu.’

'Ta masu kudi ce Anti.'

Ta shige kitchen tana dariya.

Bata dade da shiga kitchen din ba Shukra ta dubi Khadeeja tace ‘Anti zan Sha ruwa.’

Daga nana ta kwalawa Ummi kira ta debo ruwa ta mikowa Shukra. Kadan ta kurba har Ummin ta juya zata koma kitchen din Shukra ta kurbi ruwan ta mika kofim tana cewa ‘Na Sha Ummi tafi da shi.’

Ta karbi ruwan a Kofi ta juya ta nufi kitchen din, tana juyawa ta kafa kai ta shanye ragowar ruwan sannan ta wuce kitchen din.

Mustapha ya kalli Khadeeja yace ‘Wannan yarinyar kuwa ta san me take yi? Ana maganar Corona tana abubuwa anyhow. Ta gama yawonta a gari Kuma ta zo tana daddumar abubuwa kuma har tana using utensils din yara? Corona din nan fa is real.’

Khadeeja ta kalleshi ta langabar da Kai tace ‘Kayi hakuri zan yi mata magana.’

'To Allah ya kiyaye.’

PAGE 39

MIJIN MARIGAYIYA

A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

Nan da nan Ummi ta gama aikin gidan ba tare da wata matsala ba. Bayan la'asar Kuma ta dawo. Itace tayi komai don Khadeeja kujera ta saka ta zauna a kitchen din tana gaya mata abinda zata yi, shi kuma Mustapha yana zaune a parlor shi da yaransa suna kallon TV.

Kafin magriba sun gama komai Khadija ta kawo ta jera a kan carpet domin Mai gidan ya ce yau a kasa zasu Sha ruwa ba a table ba. Zobo ne mai sanyi, sai dankali da kwai, daga gefe kuma ga farfesun kaza da kuma couscous da sauce. Kafin a fara kiran Magriba ta zubawa Ummi komai ta sallameta ta tafi.

Sai da aka idar da sallar Magriba sannan suka zauna shan ruwa; kowa da plate dinsa wanda Khadeeja ta zuba masa abinci ga soup bowl a gefe, ita kuma Shukra kwanonsu daya da Khadeejan. Bayan ta gama zuzzuba abincin kuma ta fara kokarin hada musu shayi. Bayan ta gama ta hada nata sannan ta dauki karamin kofi zata zubawa Shukra daga nata login, Mustapha ya dubi kofin yace ‘Wannan ba kofin da yarinyar nan ta sha ruwa da shi dazu bane?’

Ta cigaba da juyewa tana cewa ‘Shine, ai ta wanke shi.’

'Kika sani? Bayan ruwa kawai aka Sha da kofin kuma kina zaune a nan tayi wanke-wanken, idan fa kifewa kawai fayu bayan ta gama dambara baki a jiki?’

Ta gyara zama zata mikawa Shukra shayin yace ‘Ya zaki bata, ki canza mata cup mana. Ba kya jin me nake fada ne.’

Ta kalleshi kamar zata yi magana sai kuma ta fasa; ba zata iya fara musu da shi yanzu ba domin bata ma da kwarin da zata iya doguwar magana don kishiruwa ta galabaitar da ita a wunin yau. Ta tashi ba tare da tace komai ba ta wuce kitchen, ta zubar da shayin ta dauko wani kofin ta dawo ta sake hadawa Shukra wani shayin. Haka suka gama shan ruwan ba tare da ta kula kowa ba sai Shukra da suke cin abinci daga kwano daya.

…….

A kwance ya sameta a daki, ba wai bacci take yi ba kawai rufe ido tayi tana hutawa saboda yanda jikinta yake ciwo. Duk da babita tayi aikin gidan ba yau amma ta gaji, musamman da yake an yi kishiruwa. Gashi bata son ta ajiye azumin saboda ko bata yi ba ma bata iya cin abincin kirki; garama da tayi azumin ta samu bayan shan ruwa ta ci couscou ta koshi.

PAGE 40

MIJIN MARIGAYIYA

A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

Da sallama ya shigo dakin, ta dan juyo ta amsa sallamarsa, bayan ya zauna yace ‘Sai yaushe zaki shirya yaran su kwanta ne?’

Tace ‘Barinsu nayi da yake daren na azumi ne kuma gobe ba fita za ayi da safe ba, zuwa 10pm sai a kwanta.’

'Ok, haka ne kam.’

Suka yi shiru na dan lokaci, jimawa kadan yace ‘Ina ga kiyi hakuri da aikin nan wannan yarinyar ta daina shigowa gidan nan. Ki bari a sami saukin cutar nan tunda kina ji tace cutar ma ta masu kudi ce don haka ba zata daina yawonta ba.’

Ta tashi zaune takalleshi sosai tace ‘Don Allah ka bari, wallahi nayiata magana kuma gobe ma zan sake mata magana. Ka ga ga azumi wallahi abincin shan ruwa kawai ya isheni balle ga su wanke-wanke da shara, zan mata magana na san in sha…’

Kafin ta karasa ya katseta yace ‘Ki fahimceni ba wai don bana son ta tayaki aiki bane, nima na fi so a tayaki. But she's putting all of us at risk, tunda zata ke ta gama yawonta a gari sannan ta dawo ta shigo mana gida tana mu'amala da yara da kuma ke anyhow. Bana son a sami matsala please ki sallameta kawai, idan pandemic din nan ya wuce zata iya dawowa ai.’

‘To ya zan yi da aikin? Gashi ba dadi nake ji ba, kamar kana mantawa da cikin jikina.’

'Ni ban ce miki na manta na, Amma aikin gidan nawa yake? Duka ba wani abu ne da zai gagareki ba fa, kina ma fa da damar ki ajiye azumin idan yana wahalar dake ba wani abu bane. Amma aikin gida ai ba abinda zai gagareki bane, itama Ma'un haka take hadawa da ciki da goyo kuma da aikin gaba daya. Amma gaskiya a hakura da shigo da kowa gidan nan for now, gaskiya. Da safe ma idan ta zo daga gate zan ce ta koma. Kiyi hakuri ki fahimceni, ke kanki you are at risk idan ta kwaso cutar nan ta shigo mana da ita gidan nan.’

Cike da takaici ta sunkuyar da kai tace ‘Shikenan, duk yanda kayi.’ Ta zame ta kwanta.

Ya bude baki zai yi magana sai kuma ya ga gara ya kyaleta ta huce zuwa an jima ya sake yi mata bayani, amma ba zai iya bari ba ga halin da ake ciki kuma a dinga shige da fice a gida. Idan cutar nan ta shigo gidan ya zai yi da ita? Ya mike ya fice ya turo mata kofar.

PAGE 41

MIJIN MARIGAYIYA

A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

Ta juyo ta kalli kofar ta harareta kamar shine a wajen sannan ta ja tsaki ta juya. Ta San akwai cutar to amma ai ta yiwa Ummin magana, yanzu ya yake so tayi da aikin gidan nan ga azumi? Da ma ace zai tayata aikin me ko kuma ya bari yaranshi su dinga tayata to da sauki. Amma haka zai zuba yaranshi a gaba suna zaune suna kallon TV ita kuma tana kitchen ita kadai. Ta share kwallar da ta gangaro a idonta ta gyara kwanciya; bata san yanda zata kasance ba sai dai kawai ta bari taga yanda hali zai yi goben.

……..

Ko da gari ya waye Khadeeja bata ma San lokacin da Ummi ta zo ba don tun daga bakin gate ya tareta yace ta koma kada ta sake zuwa sai bayan Sallah.

Sai wajen Sha daya sannan ta fito ta dan gayggyara gidan, wanke-wanke ne ma ya bata mata lokaci don yana da yawa sosai. Haka ta wankesu gaba daya a famfon waje sai da shigo kifewa sannan Afaf ta tayata.

Tana gamawa ta shige dakinta ta kwanta; bata taba jin gajiya irin wannan ba a rayuwarta, gashi duk wata gaba da take jikinta ciwo take yi.

Tun 3pm ta shiga kitchen ta fara kokarin hada kayan Shan ruwa; dankali da kwai zata soya sai jollof sphagetti sannan ga peppersoup din nama. Da akwai ragowar zobo na jiya don haka ba zata sake hada wani ba.

Yaran suna zaune a parlor ta zo ta wuce ta shiga kitchen, tana wucewa Afaf ta bi bayanta. Ta so ta Koro Afaf din daga kitchen amma dai ta hakura ta barta, suna yin aikin. Basu dade da farawa ba Habib ya shigo kitchen din, ya kalli dankalin da aka ajiye a tsakiyar kitchen din yace ‘Anti wannan ferayewa za ayi?’

Tace ‘Eh, so nake na dora kifin nan sai na zauna na feraye shi.’

'Kawo wuka na feraye Anti.' Ya fada yana Bude cabinet, ya zaro roba ya tara ya debu ruwa.

Tace ‘Ka barshi Habib zan feraye.’

Ya sa hannu ya dauki wuka a kan sink yana cewa ‘Na iya feraye dankali fa Anti, idan na feraye miki sai ki yanka.’

Bai saurari amsarta ba ya tsuguna ya fara feraye dankalin.

Afaf ta ajiye kayan miyan da ta gama wankewa a kusa da Khadeejan tace ‘Anti na wanke kayan miyan.’

'To ki yanka mana albasar nan, Rabi slicing za ki yi rabi Kuma ki yanka kanana sai a saka a soup da fried egg.’

PAGE 42

MIJIN MARIGAYIYA

A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

Ta dauki albasar ta wanke ta zuba a chopping board ta fara yankawa.

Ba su ji lokacin da Mustapha ya karaso bakin kofar kitchen din ba; a dai-dai lokacin nan wukar da Afaf take yanka albasa ta goce ta Yanke mata hannu. Ta dire albasar ta make murya tana cewa ‘Waiyo Anti na yake.’

Da sauri ta saki abinda yake hannunta ta nufi wajen Afaf din tana murmushi cike da kulawa tana cewa ‘Sorry, garin yaya Afaf. Ki…’

Da sauri ya karasa ya kama hannun Afaf din yana cewa ‘Garin Yaya kika yanke, me ya sa kika dauki wuka?’ Ya juya ya dubi Khadijan yana cewa ‘Na gaya miki sai kin san aikin da Zaki dinga sa yaran nan Amma ke gani kike kamar kawai bana son su taya ki aiki ne. Yaushe Afaf zata iya wani yanka albasa.’

Afaf ta zare hannunta daga nashi hannun ta juya ta wanke a sink, ta dubeshi tace ‘Ya ma daina jinin Abba bari naje na daure.’

Yana juyawa ya dubi Habib wanda yake ta ferayar dankali ya daka masa tsawa ‘Ka ajiye wukar nan ka tashi, namiji da kai kana wani feraye dankali. Tashi ka bani waje.’

Ya juya kan Khadeeja wadda ta riga ta cigaba da aikinta kamar ba da ita yake magana ba, yace ‘Na gaya miki ki daina sa yaran nan aikin da ya fi karfinsu, bana so. Shi Habib ma da yake namiji me ya hadashi da wani harkar girki? Bana so.’

Bai ga alamar zata bashi amsa ba don haka ya juya shima ya fice suka barta ita kadai a kitchen din.

Ta rasa me ma zata yi, ta goge fuskarta ta cigaba da aikinta.

Haka ta lallaba ta gama komai, zuwa magriba ta zubawa kowa aka sha ruwa.

Ta gaji iya gajiya don haka bata ma da kuzarin da zata iya wani musu da shi, ta dai riga ta gama yankewa kanta hukunci da zarar an bude gari zata tafi gidansu ba zata dawo ba sai ta haihu kuma ya dauki mai aiki.

…….

A haka aka cigaba da azumi, kullum cikin wannan yanayin Khadeeja take hadawa da hidimar gidan da ta yaran tayi ta fama.

Kullum sai ta yiwa Shukra da Nasreen wanka, tsarkin kashi tsarkin fitsari duk ita take musu. Duk wata fitinarsu itace me kulawa. Ga shi tana fama da Shukra wadda sai yanzu ne da suka kwana biyu ta fara hanata kashin wando.

PAGE 44

MIJIN MARIGAYIYA

A HAUSA NOVEL by Sakina Yazid (Innar su Amal)

'Don Allah kiyi mata a hankali, komai lokaci ne ai zata daina ne a yi mata hakuri.’ Ya fada yana shirin komawa dakin ya yiwo alwala.

Ta tsuguna zata dauketa taji kanta ya biyota kamar zai fado, ta dafe goshi ta koma ta tsaye tace ‘Kai! Ba zan iya ba fa.’

Ya juyo ya tsaya ‘Menene?’

‘Ba zan iya tsugunawa ba fa, jiri kwasa ta yake.’ ta karasa kan kujera ta zauna ta dafe goshi.

Ta dubi Afaf tace ‘Bani ruwa na Sha Afaf, ga kiran Sallah nan an fara.’

Nan da nan ta cika Kofi da ruwa ta mika mata, ta Sha kadan ta jingine kanta tana rike da ruwan.

Kukan Yusra ne ya katsesu tana cewa ‘Anti na daina ba zan Kuma ba, manatwa nayi daman.'

Ta yunkura zata mike Afaf tayi sauri ta dafeta. Abbansu ya dubi Khadija yace ‘Don Allah ki lallaba ki wanke mata kashin nan, Wannan wane irin abu ne? Yanzu wa kike so ya wanke mata kashin?’

Afaf ta aika Nasreen ta dauko fo a toilet ta cire wandon da yake cike da Kashi ta jefe a fo din sannan ta dauke Shukran ta nufi bandaki. Ta wanke mata sannan ta dawo ta gyara wajen, zuwa lokacin Abbansu ya fito daga alwala.

Ya zauna ya sha ruwa sannan ya mike zai tafi masallaci. A daidai lokacin itama Khadeeja ta dago kanta ‘A dawo lafiya.’

Yana jinta yayi banza da ita saboda yanda yake jin haushinta, Kuma tabbas sai ya kora mata bayani in an Sha ruwa. Daga yau ma ba zata sake yin azumin ba tunda dama Mai ciki tana da damar ajiyewa. Ta mike tana gatsina fuska, kawai sai gani yayi ta sulale zata fadi. Ya zabura zai tareta yayi fatali da casserole din dankali, a lokaci guda Habib ya saki jug din zobon da ya fito dashi daga kitchen ya tarwatse a wajen ya karasa kanta. Duka su biyun kafin su karaso ta zube.

Abbansu ya dago kanta yana jijjigawa ‘Khadeeja, Khadeeja, Inna lillahi wa Inna ilaihi rajiun, Khadeeja.'

Ko motsawa bata yi.

Ya sunkuceta ya kwantar da ita a kan three seater, ya kara gudun fanka sannan ya kunna AC. Ya cire mata dankwalin da yake kanta ya fara yi mata fifita.

Yaran gaba daya suka jeru a kanta suka yi tsuru-tsuru; Afaf ta leka fuskarta ta kafadar Abbansu tace ‘Abban itama mutuwa zata yi ta barmu ko?’

'Ke bana son rashin hankali, ba wanda zai mutu’

PAGE 45

MIJIN MARIGAYIYA

A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

A take yaran suka saka masa kuka mai ban tausayi. Afaf ta rungume Nasreen da Shukra suka hada Kai suna kuka.

Habib ya taba shi yace ‘Abba ka Kai ta asibiti kada ta mutu ta barmu.’

'Kai rufe mana baki.’

Gaba daya Shima ya rude, jikinsa har rawa yake yi. Ya janyo jug din ruwan sanyi ya jika hannunsa ya Shafa mata a fuska. Ta ja numfashi ta bude idonta, sai kuma ta mayar ta rufe.

'Khadeeja.' Ya kirawo sunanta da karfi yana jijjiga ta.

Da gudu su Afaf suka karasa kanta suna kira ‘Anti, Anti.’

‘Khadeeja.’ Ya kara kiran sunanta a firgice.

Ta bude ido ta sake rufewa.

Ya mike tsaye ya dan tura yaran yana cewa ‘Ku zauna na dauko mukullin mota, asibiti zan kaita yanzu, babu abinda zai sameta in sha Allahu.’

Ba tare da bata lokaci ba ya dauko mukulli ya fito, ya je ya bude kofar motar ya dawo ya dauketa bayan ya yafa mata mayafi ya wuce yaran suna biye da shi ya kwantar da ita a bayan motar. Bayan ya rufe kofar motar ya juyo ya kalli yaran yana tunani; to yanzu ya zai yi da su? Wa zai barwa su? Ya san shi kansa ma sai ya amsa tambayoyi a checkpoints gashi ma’aikatan asibitin ma kamar tsoron mutane suke balle ya kwashi yara su tafi. Ya shafa kai sannan ya sake kallonsu cike da damuwa; da ace gari a bude yake da sai ya wuce da su ya ajiyesu gidan Hajiya to amma ya san ba zai yiwu don zai yi ta bata lokaci a checkpoint. A take dabara ta fado masa.

‘Ku tsaya a nan ina zuwa.’ Ya basu umarni sannan ya fice daga gidan ya turo gate din.

Yana fitowa ya karasa gidan su Ummi, yayi sa’a yana tsayawa maigidan yana dawowa daga masallaci. Bayan sun gaisa ya sanar da shi so yake Ummi ta zo ta zauna masa da yara ya je ya kai Khadeeja asibiti. Ya janjanta masa sannan ya shige gidan ya turo masa Ummin.

Haka ya sako ta a gaba ya dawo gidan ya bar mata yaran ya ja motar ya nufi Aminu Kano Teaching Hospital dake Kano.

________

Yana zuwa asibitin aka nuna masa gynae emergency inda nan ne ake karbar masu ciki wadanda suke bukatar taimako na gaggawa, nan da nan suka karbet aka fara duba ta; duk da dai su kansu ma’aikatan zaka gane cewa suna cikin yanayi na tsoro saboda Covid19.

PAGE 46

MIJIN MARIGAYIYA

A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

A nan wajen aka nuna masa benchi ya zauna yayinda ita kuma aka turata a kan gadon marasa lafiya aka shige da ita dakin bincike.

Tana kwance a kan gadon yayinda take amsa tambayoyin ma’aikaciyar jinya sai wata ma’aikaciyar wadda taji suna kira matron ta shigo, ma’aiakciyar ta juya tana kallon matron tana cewa ‘Matron wannan fa sai an yi mata scaning, cikin nan na jikinta kamar ficewa zai yi duk da dai tace bata fara bleeding ba ama dai tana jin alamunsa.’

Matron din ta karaso ta tsaya a kanta, tace ‘Ah! Wannan ai Khadeeja ce, wa ya kawota?’

Jin an ambaci sunanta ya sa ta bude idonta a hankali, ta yi murmushi a gajiye lokacin da suka hada ido ta gane wadda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login