Showing 27001 words to 30000 words out of 84412 words
Shiru nayi kamar bazanyi maganaba sannan ahankali nace babu komai ammadai dady
yanzu idan ya ganni ya dinga tabani kenan kuma nasan babu kyau.
MURmushi tasaki kamin tace"oh kuruci danhin hauka to ai mijinki ne jidda Wanda baka
auraba shine babu kyau ko jikinka yaganima balle akaiga maganar tabawa danhaka kisaki
jikinki kibawa mijinki kulawa duk abinda yakesoshi zaki dinga mishi,Hakanne zaisa yaitak'arajin
kaunarki koda yaushe sannan bazai kawo wata wadda zata fikiba. Kinga dole ki dainajin kunyarshi koda yaushe domin jin kunyar miji koda yaushe yana
tauye soyayya,Danhaka bakoda yaushe zaki dinga jin nauyinshiba tunda kinga shi yana kokarin
ganin yajaki jiki,To kema ki dinga kwatanta hakan misamman idan dagake sai shine kinji ko?
Kaina nadagamata ahankali dan har lokacin inajin kunyarta.
"Yana Neman hakkinshine wajanki?
Abazata naji tambayar danhaka a gaggauce na daina kallonta inajin kamar in nitse awajan
kawai.
"Kai gaskiya kunya taimiki yawa jidda gayamin akwai abinda zan bakine shiyasa naimiki
tambayar kinji ko?
"Nima bansan ko yana nemaba ammadai ni komai inayimishi.
"To shikenan hakan ma ai yayi kina k'okari danhaka duk abinda ya nema wajanki kisaki jikinki
kinji ko!Kuma kadda ki gayama kowa sabida sirrin junanku ne haramunne ki bawa wani labari.
Yanzu ban shiryaba sosai amma bayan bikin zahra Zan kawomiki sako kinji ko?
"To aunty nagode sosai,Amma ke baki da yarane naga bakizo dasuba?
"Hahhhha da alama kinadason yara to kiyi k'okari ki haifamana sabbi,Mukam yanzu Hutu
mukeyi yarana uku babban yana makaranta biyun kuma suna wajan mama can suke zaune
wajanta mahaifiyar megidana Saikuma inda rabo idan Allah ya kawo wasu,Bari intashi kadda ya
jirani,Hannu tasa cikin jakarta tazaro wata kwalba ga wannan humra ce saiki dinga amfani da ita
kamin inkawomiki me yawan.
Yamma lis sukabar gidan domin tun inajin kunyar hirar da sukeyi har saida nasaki jikina
akacigaba dayi ina dariya.
Zama yai gefena har yana gogar cinyata da tashi,Kamin yace" 'yammata nazo hira kinsan
dole muyi k'ara'in wacce bamuyiba ko?
Cikin murmushi nace to ai dady ba haka zakaiba gayu zakasha saika tsaya waje ka aiko
kirana. Nikuma saikaga nafita wajanka,Amma haka ai ba hira kazo ba.
"Au Allah da gaske? To karki damu aiko zanyimiki duk yanda kikeso yanzudai gayamin mene
labari.
Manyan idanuna na juya gefe da gefe kamin na zubesu cikin nashi ina sakin murmushi,Abun
da yai matukar yin tasiri cikin zuciyarshi da gangar jiki.
Jiyai kamar ya Kai wata babbar runguma saidai beso ya dinga zakewa din.
"Babu Amsa kenan?
Uhumm nace ina dan kauda fuskata daga kallon dayake bina dashi,Saidai idan in dauko hijab
Dina ka kaini wajan hajiya nima.
Murmushi yasaki "naki wayon yau nan zamu idasa yininmu dagani saike nima inji dumin
amaryata,Amma nagode sosai jidda kin iya abun tarbar baki.
Sadda kaina k'asa nayi so nakeyi inyimishi maganar auren zahra amma kuma bansa yaga na
dameshi tunda dai bemin maganarba.
"Nima inaga zanyi wata tafiya zuwa China amma bazan wuce one month ba gida zai
kasance daga ke sai yaranki domin itama zahra zata kasance da Nata Mijin dan Allah ki kula
banda yawo jidda makaranta kawai sai kuma wajan hajiyata ko taki Zan dinga kiranku akai akai
insha Allah,Sannan zanyi k'okarin ganin ankawo miki wadda zaku zauna tare kinji ko?
Jinake kamar in doka tsalle sabida murna amma ban nunaba saima kaina Dana d'aga kawai
ina fadin to Allah ya temaka yasa asamo abinda akaje dominshi din.
"Yauwa madam jidda Ameen ya Allah nagode sosai.
Jefi-jefi yakemin hira duk dai dan insaki jikina dashi sosai yayinda nikuma hankalina yayi
gaba hango zahra gidan ya usi kawai nakeyi,To dama beda matsalar komai yanada wajan zama
domin ainihin gidan mahaifinmu babu abinda yai domin gidane mekyau da tsari nasan 'yan
gyare gyarene kawai za aimishi sai addua dan yajima babu kowa ciki,Sannan yana aikinshi
balle wani Abu yaimishi wahala.
Ganin yanda nai nisa cikin tunanine yasashi mikewa tsaye Bari in lek'a waje zanga wani
ammadai kadda kice zakiyi girkin dare zanshigo da wani Abu kinga kema kin huta ko?
Narai narai nayi da idona zasu zubo da hawaye,Danni gaskiya tsoro nakeji.
Rungumeni yayi jikinshi abinda dama yaketa kwadayi kenan tun Dazu"Haba mana jidda da
girmanki da komai zakiyi kuka ai sai in rainaki ko kinaso in rainaki?
Girgiza kaina nayi tare da share hawayen dan tuni sun Zibo.
Komawa yai ya zauna tare da maidani saman cinyarshi,"Kinga daina yimin asarar wa innan
hawayen naki gayamin mene abin kuka kuma?
Cikin shagwaba nace to dady ni kadai za abari cikin gidan tsorofa nakeji.
"Subhanillahi da yammannan kikejin tsoro to Bari infasa fita har akira magriba nasan kila
lokacin sundawo hakan yayimiki?
Cike dajin dadi na amsa mishi tare da kuma lafewa kirjinshi,Sabida Kalar k'amshin dady na
musammanne.
"""""""""""
"Zahra kaddai yau kunyata kikeji?
Girgiza Kai tayi tana sakin murmushi.
"Gaskiya nayi farinciki har bansan yanda Zan misiltaba wallahi banzaci dady zai bani aurankiba
adai yanzu saiga Kira kawai wai na turo kuma abin dadi saigashi daga zuwa har sadaki sunbiya
antsaida ranar aure ai kinga dole inyi farinciki abin yazomin abazata amma naga ke kamar ma
baki wani farinciki ko?
"Kai ya Usman inayi mana,Cewar zahra tana rufe fuska.
Dariya yasaki cike da nishadi "To shikenan nagode,Nanda kwanaki takwas insha Allah iwar
haka kina cikin gidana Danni da wuri za akaiminke ido'na ganin ido.
Murmushi kawai tasaki tana mamakin irin zumudin da yakeyi.
"Uhum ya Usman Bari inzo muwuce gida munbaro aunty ita kadai agida.
Hannuwanta ya rike yana murmushi"Ke share kawai waye yacemiki ita kadaice?Ainasan
dady na gida bazai barta ita kadaiba Ashe aunty kike cewa kema to idan mukai aurekuma ya
zaki dinga kiranta?
"Hannuwanta taso kwacewa sabida rashin sabo amma ya rike kam harwani mirzawa yakeyi
alamar dai hakan nayimishi dadi," Ai dole hakan Zan kirata dashi tunda ni dady na take aure
sannan nikuma yayanta nake aure ko.
Idanunshi yakai kirjinta soyake yaga akwai abin kokuwadai dole saishima ya jira zuwa wani
lokaci,Saidai ga mamakinshi saiyaga wajan akwai d'an tudu alamun akwai fa,Besan lokacinda
ya sauke ajiyar zuciyaba dan shifa bawani jira ko raino zaiyiba kawai sunnar zai raya.
Dan yanzu haka jiyake kamar wani mayen karfe najanshi zuwa gareta,Shiyasa saiyai Mata
sallama akan zai Kira Waya anjima da dare danhaka ta kasance da wayar ahannunta.
Abayyane ta sauke ajiyar zuciya lokacinda tajita akan kujerun falon hajiya kaka.
"Uhumm Aifa Allah ya hadaki da aiki dan wallahi wannan yaron daga gani bawani kunya ko
kawaici zaiyiba danhaka zanbaki shawara saikita amfani da ruwan dumi dakuma 'yan kayakin
marmari yanda bazaki dinga galabaitaba tunda yanzudai bekamata aimiki wani cushe-cusheba
saidai dan Abinda ba arasaba tashi ga direba nan yazo yanzu dadynku yace ya turo amaidaku
gida,Duk hajiya kakace tai wannan maganar bawani ko hadiyar miyau,Batasan bama wani
fahimtarta zahra din tayiba.
******
Idanunshi alumshe saika rantse barci yakeyi tsabar lamo din da yayi niko wuyanane naji ya
makale sabida adokin wuyana ya Dora kanshi bansan tsawon lokacinda muka dauka
ahakaba,Sannan koya na motsa saiyakuma gyarawa,Ga hannunshi daya tallabo mazaunaina
dasu jina nakeyi duk atakure ammashi saina Lura ko ajikinshi ma.
Cikin muryar shagwaba nace dady anfara kiran sallah fa!!
"Uhum yace kamin yafara sassauta rikonda yaimin,Koda ya bude idanunshi sainaga kamar
ma yai kuka sabida Jan da sukayi.
Zameni yai daga jikinshi kamin yace"Bari nadan watso ruwa to ina zuwa suma ai nasan
yanzu zasu dawo.
YARDA.
Labarin YARDA na kudine idan kina buk'atar siye zakibi wannan tsarin domin samu,Naira Dari
biyune kacal,200.
Acct no
0005074141 Aisha sabiu Ja'iz bank.
Kokuma ta katin Waya zuwa wannan layin08142643253.
Tura shaidar biya ta wannan layiní ½í±†í ¼í¿».
27-28
Ajiyar zuciya na sauke kamin nima na tashi zuwa d'akina,Ruwa na watsa gamida d'auro
alwala,Uhum su zahra ansami yawo anmanta Dani zaki dawo ki sameni ne.
Doguwar Riga nasa mara nauyi sannan nai sallah,Inajin lokacinda ya leko d'akin lokacin ina
sallah danhaka koda nagama bamma fitaba dannasan be gidan.
Tunda naji tsayuwar mota nasan sune,Kamin infarajin ihun Mimi tana kiran sunana.
Wata wawar runguma zahra taimin tana murna,Murmushi na Saki nima tuni na nemi fishin
da nakeyi da ita na rasa,Sabida dama dadewar da sukayi itace ta dameni.
"Sis ki tayani murna nima nakusa shiga daga ciki Ashe har an kammala komai na bikina da
ya Usman ranar daurin aure kawai ake jira zakije kiyi kallon zazzafar love sis Nagode Allah
dayabani me sona nima.
"Alhamdulillah Zahra natayaki murna sosai ammadai bazanji dadiba idan naga babuke cikin
gidannan gashi dady zaiyi tafiya zuwa unguwa nasan zanshiga damuwa.
Bakinta awashe tace karki wani damu nasan ya usman zai dinga kawoni sannan ai muna
tare a makaranta ko!!!
Sadiq ne ya mikomin Leda "aunty gashi inji hajiya kaka tace wai ki kirata awayar nan gidan
zakuyi magana.
Amsar ledar nayi tare da budewa wasu itatuwane Kala Kala sai mazarkwaila da kayan yaji.
Nan fa muka dasa hirar yanda zamu kasance idan anyi auren yayinda yaran ke falo suna
kallo.
"""""""
Bansan meyasaba cikin kwanakinnan dady ko nauyin zuramin ido beji babu ruwanshi da
yaranshi indai wajan kallonane saidai kunya ta isheni.
Tunda ya ajiye ledar dake hannunshi falon ya bide da k'amshin kulin tsire danhaka duk muka
shirya kunsan abun kwadayi dai yanda yake.
Saida ya canzo kaya sannan yace ga abinci nanfa na ajiye duk kukayi banza dashi.
Mimi ta Dauko babban faranti na juyeshi dukanshi dan har dady yakanci abinci damu
dukanmu wasu lokutan, faruk nasa ya dauko lemuna da kofuna sannan mukafaraci.
"Kai gaskiya dady tsirenan yayi dadi wallahi kamar kadda mutun ya koshi, Cewar Sadiq
yana dariya.
Muna duk dariyar muka Saki,Dan dama kowa santin naman yakeyi cikin zuciyarshi.
Muna cikin Dakina har goma nadare ya wuce hira kawai muke hadda yaran yau babu
Wanda yai barci da wuri,Saida ya usi ya Kira Waya sannan hirar ta lafa kamin wani lokaci duk
sunyi barci saini da zahra wadda keta zuba hirar kauna ta Waya,Niko gabadaya nagama bude
kunnuwana ina sauraran komai,lallaima Ashe ya usi dinnan beda kunya shima,Musamman
danaji yana fadin bansan yanda zanyi inyi barciba babyna domin kewarki kawai ke nukuskusata
gashi kodan kiss na sallama bakiminba dazu.
"Kutt karuwanci"Abinda nafadi kenan ina zare ido.
Sunjima sosai suna hira sannan ya kashe idanuna na zubamata ina mamakin yanda akai
zahra ta waye da yawa dan Allah ji yanda take sakin kalaman soyayya saikace wata babba.
"Ni kadda mutun ya cinyeni da kallo tunda be iya yima mijinshi haka,Yoni Allah na tuba aka
dauramin aure ai inaga sati daya yai yawa nafara juyama mijina ruwan kai da zazzafar soyayya
amma ke kintsaya sanya,Kina nan zaune wata zata wonemiki miji Allah nikuma babu ruwana
wadda ke soyewa da dadyna itace tawa.
Wani uban dundu na sakarmata kamin ince kai zahra wallahi kinbani wai yaushe kika koma
haka? Garama da dady zaimiki aurannan wallahi dannaga alama gaf kike da kifara leken
mutane idan suna wanka tsabar sa ido kuma da kike maganar wata zata auri dady ni ina
ruwana.
Dariya tasaki tare da rufe bakinta ganin mimi ta motsa.
Kayan barcina na dinga d'agawa ina Neman wadda zan mak'ala dan duk nagama sa
masu mutuncin.
Wata 'yar yaloluwa Riga zahra ta mikomin dallah anshi wannan kisa nasan ba k'aramin tafiya
da dady zakiyiba.
Kwace rigar nayi na maida ina harararta"Baki da kunya wallahi,Wannan rigar zansa inje
wajan dady saikace wata 'yar iska? Lallai ma.
K'aramin tsaki taja lallaima to ki zauna tunda ke ba 'yar iska bace nagadai haka Mata Kecin
kwalliya dan zuwa wajan mijinta to Bari kiji ni wallahi nayi alkwarin duk abunda mamanmu tayi
saina kwatantashi idanma banyiba ita da wani lokacinma daga ita sai tawul take zuwa wajanshi
dan kawai yai farinciki amma ke kintsaya wasa zakiga yanda zan dinga yin shigata gidan mijina
wallahi.
TO GAREMU IYAYE MATA DUKKAN ABUNDA ZAMUYI YAKAMATA MUDINGAYIN WANDA
YA DACE MUSAMMAN IDAN MUNADA YARA DOMIN WANI LOKACIN ZAMUGA KAMAR
BASU FAHIMTA TO WALLAHI BA HAKABANE SUNA SANE KUMA TABBAS WATARAN
SAISUNYI KOKARIN AIKATAWA.
KUNGA DAI ZAHRA NATA KOKARIN GANIN TAYI ABINDA MAHAIFIYARTA TAYI DANYIN
KOYI DA ITA TO TABBAS. INDA ABUN TSIYANEMA HAKA ZATAI KOKARIN KWATANTASHI
GIDAN AURENTA.
Cikin sanyin jiki na mike da rigar ahannuna nakoma bayi na sawo rigar,Saidai da sauri na saka
hijab Dina dan sosai rigar taimin kyau saidai bata da wani rufin asirin daya dace, Dariya ta Saki
kamin tace kai wannan amarya bakauyace Allah.
Turare na fesa tare da komawa bakin gadon na zauna zullumin yanda zanje wajan dady
ahaka nakeyi wlh.
Wayarshi yajawo yakuma duba time kusan Karo na barkatai amma shiru kakeji"Kai anya
yarinyar nan Nada hankali kuwa nufinta yauma can tai kwanciyarta ta barni kenan?
Kayan da zaiyi tafiyar dasu yacigaba da shiryawa sabida Ada sai nan da kwanaki hudu zaiyi
tafiyar amma yanzu Dole zai tafi gobe domin wasu dalilai dasuka taso.
Saida ya kintsa komai Hatta da duk kudin da yasan za a buk'ata sannan yashiga
wanka,Haka yafito shar dashi sai tashin k'amshi yakeyi babu Wanda zaiga dady yai tunanin wai
yanada yarinya kamar zahra.
Duk a tunaninshi munyi barci danhaka da kwarinshi ya tura kofar saidai ga mamakinshi
saiya gammu zaune gabadaya mun maida hankalinmu akan wayar,
Yadanji kunya ga alamu amma abunku da wayayye danhaka kawai saiya k'arasa ya zauna
bakin gadon tare da amshe wayar daga hannun zahra"Bani nan wato wayace zata Fara hanaku
barcin wuri yanzu ko?
Tsumu-tsumu mukayi dan duk bamu zaci zai shigo d'akinba,Sosai yafara bincike cikinta
mukuma muka hade kai waje guda tare da zullumin kadda ya amshe wayar duk da dai babu
wani Abu na ashsha cikinta.
Mikewa yayi da wayar ahannunshi tare da kallona,Tashi kuje".
Wata irin mashahuriyar kunyace naji ta dirarmin Amma ganin yanda fuskarshi take ahade
yasani saurin gyara hijab Dina tare da mikewa ina dan kallon zahra kamin nace saida safe.
Ina gaba yanabina abaya besan meyasaba amma saiyaji ya k'osa yaga na tube hijab din
jikina musamman dayake ganin kwaurina awaje yasan cewa rigar bawani tsawone da itaba.
Zama nai gefen gadon akunyace duk nabi na daburce musamman danaga ya zubamin
manyan idanunshi yanamin wani kallo k'asa-k'asa.
"Dady ina yini"
Wata irin dariya yasaki jin ina gaidashi tsabar rudewar danayi,Hararata yayi kaminyace"Naki
na amsa din wato mijinki na nan yana jiranki kekuma kinacan kina hira ko?
Kaina aK'ASA nace kayi hakuri bazan kumaba.
Jawoni yayi jikinshi yanajin yanda laushin fatata ke ratsa hannuwanshi,"Karki damu aike 'yar
gatace sannan kuma amarya,Kawai dama inaso muyi sallama ne sabida wani dalili yasa dole
gobe zan wuce kinga bazan halarci daurin auren zahra bama kenan,Kamar yadda na gayamiki
Dazu da Rana yanzuma Zan nanata miki jidda,Ga amanar aurena nan akanki sannan gata
gidana gakuma ta yarana duk akanki