Showing 3001 words to 6000 words out of 175796 words
Chapter 2 - AMIR DA AMIRA Complete by Maman Nusaiba.txt
kizoba saboda wannan shedaniyar jikar taki ta kakkarya mana jiki gata kamar kara amma sai shegen karfi kamar na doki
Inna ta hade kirar sama data kasa tace wllh a shirdinka karka kuma cewa jikata shedaniya dan ba karamin aiki na bane nayi tsukiya muci dambe awajan nan tana aika masa da harara
Mai gari yace dama ai nasan da haka ke kike daure mata gindi take fitsararta son ranta
Nan inna ta rufesu da ruwan masifa tace ba'a isa ya aibata mata jika ba
Su ameera kuwa suna gefe ita da kawar ta suna kwasar dariya harda rike ciki , Ameera tace Inna tace bazata bari a dakeni ba a
kofar mai gari
khadija tace aikuwa naga alama yanxu dai da dare zakije dandalin ne
ameera tace zanje mana
Ankawo mai gyara mai gari yace inna tabiya kudin gyara ko kuwa ayima su ameera bulala ashirin
Inna tace wllh baka isaba kace zaku zanemin yarinya , ta fiddo kudi dubu biyar ta watsa ma mai gari tace gashi nan anbiya to ko harara kamata saina sakata ta rama tace musu muje gida kunji suka kama hanya
Wata mota ce take shigowa layin sainaga tayi gidan su ameera ina lekawa naga wani mutum da bazai wuce shekara 47 yana dravin sai wani saurayi kyakyawan gaske wanda yake kamar sa da baban sa fari ne tas bazai wuce shekara 25 sai wani shan kamshi yake ameer kennan suna isa gidan yaran gidan suka fito suna ga baba na birni cikin fara'a baba na birni yafito yana dariya suka ce sannu da zuwa yace yauwa yarana nasameku lfy suka amsa a tare da lfy lau
Ameer ne ya fito daga motar ganin yaran yasa yasaki fuska nan sukayo kanshi suna yaya ameer sannu dazuwa yace yauwa kanne na nan sukayi sashen inna lokacin bata jima da dawowa daga kofar mai gari ba tana ta fada
ganin su ameer yasa ta washe baki tana lale barhabin mutanen birni suka shigo da sallama ta amsa musu ameera ce tafito da gudu tana cewa oyoyo baba taje rungume shi yana dariya yace a a kaga yar inna an girma
cuno baki gaba tayi tana shagwabe fuska tace Allah baba ban girma ba ni
yace to shikenan naji
Tana juyawa wa zata gani ameer aikuwa da sauri tayo wajan sa ya tsaya yana kallon ta yarinya har tayi saurin girma yana zancen zuciya yaji ta a jikinsa suka sauke ajiyar zuciya a tare
ta dago kanta ta marairaice fuska tace yaya ameer shine ka wani daure fuska ko bason zuwa garinmu kake ba
Sai lokacin yasaki fuska yace waya ce miki ai ina son zuwa sosai naga granny tsohuwa da ke dasu abba da umma
Ameera tace to na yadda yaya
Inna tace mai gida na ni manta ni kayi ne kodan kaga ameera ne,
Yace a wane ni hajiya inna mai duniya taya zan manta ki, dariya inna tayi tace to zo ga abinci da ruwa sadiya tayi girki irin naku yan birni
dariya yayi yace to suka zauna ameera na manne da ameer tana ta zuba mishi surutu shikuwa sai murmushi yake yi dan baya gajiya da surutun ta
Ameera tace daddy yau saida aka kaimu kara wajan mai gari
daddy yace kara kuma ?
Inna tayi caraf tace wllh kuwa Muhammadu wai ameera tabi wajan da gudu ta taka mai gari shine fa akace kona bada kudin gyara ko ayi mata bulala ashirin
Daddy yace ashirin fa,
Ameera tace eh
Ameer yace yanzu kun biya kudin
Inna tace nabada ai bazan bari a tabamin naman jikin ameera ba
...Ameer yace to shikenan nan suka ci gaba da cin abincin su suna hira cikin nishadi
12:30PM abba yadawo daga kasuwa yana shigowa yaga mota agidan yace a ashe Muhammad sunzo ya wuce sashensu yashiga su Ibrahim suka tarosa da oyoyo ya rungume su yayi
Suna dariya hajara tace abba daddy yazo
Abba yace ai naga motarsa a tsakar gida
Umma tayi masa sannu da zuwa ta cedasu su tafi dakinsu abba zaiyi wanka idan yagama shesuci abinci suka tashe da gudu suna murna .Umma tace muje abbansu kayi wanka kaci abinci kafin muhammad yashigo
Abba yace to yau kuma kodan oyoyo dinma babu, Umma tayi murmushi tace akwai mana amma sai anjima , abba yace to shikenan , matata yafice yana murmushin shima
Abban su Rashida ne yashigo shima gidan yaga mota yayi murmushi yace yau munyi baki ashe yayi sashensa yashiga da sallama yaran nasa suka tareshi suna abbu sannu da zuwa yace yauwa
Mama nana ce ta fito tasha waka ta kashe dauri ta iso wajan su tana yiwa abbu sannu da zuwa
Abbu yace yauwa yana kallon ta yace wannan duk ni aka yiwa ,
Mama nana tayi farr da ido tace sosai makuwa , yayi dariya yace aikuwa kinyi kyau sosai
tace ngd mai gidana nan suka shiga ciki
Ameer tinda yagama cin abinci yaja ameera kauye suka dasa hira yana kwasar dariya tana bashi labarin damben dasukeyi idan mutum yakawo mata reni tana ta zuba kamar kanyar data nuna
Ameera tace kaga yaya akwai wani da yake tareni idan zanje makaranta wai sai yake cewa yana sona ta shagwabe fuska
Ameer ya b'ata fuska yace ke kuma mai kika ce mishi
Ameera tace ai ni bana sonshi sbd k'azami ne ranar a makaranta koroshi akayi sbd kazantarshi baya wanka ga kafar da kaushi kamar bayan bishiya
Murmushi ameer yayi sai kallon ta yake yana ta sak'a da warwara da zuciyar shi
taci gaba da cewa kasan yaya wllh adamu dan iska ne tana dariya
Ameer yace kamar yaya ?
tace wani lokacine naganshi a dandali yana taba nan din budurwar sa ta nuna mishi kirjinta
Ameer ya zare ido
kwashe da dariya ameera tayi tace shine nida khadija mukayi sanda muka karyo bulala biyu muka shafa gawayi a fuskar mu muka saka mayafin inna da dare mukaje gidansu har dakinsa yana bacci,
Na tsula mishi bulala da sauri yatashi yana kallon mu yana cewa dan Allah kuyi hakuri ku kuke ganinmu bamu muke ganinku ba
khadija tace wato kaine dan iska mai taba jikin mata ko toyau zamu tafi barzagu da kai
.yana kerma yace waiyo Allah na shiga uku wllh bazan sake ba
ameera tace shiiii bamason kana daga sauti idan wani yajika to mutuwa zakayi
Adamu na zare ido baki na rawa yace nadena wllh bazan sake kama hannun wata ba inba matar dana aura ba
khadija tace ai kasan idan anje barzagu walakiri zaiyita jibgar ka,
Adamu saboda tsoro baisan lokacin daya saki fitsari ba
sarai ameera tagani tana dariya kasa kasa..Ameera tace yanzu abinda zakayi mu kyaleka shine kayi tsallen kwado guda dari saimu barka da ranka
ya fitoda ido waje yace dari kuma
Ameera ta hade rai tace eh haka nace idan kuma ba haka ba saimu tafi dakai
Cikin kaduwa da tashin hankali yace zanyi kuyi hakuri mutanen boye zanyi
khadija tace to soma yanayi harya gaji kuma suna zuba mishi bulala ga sunce idan yayi ihu mutanen gidan su suka fito shima yasan gabar ya rufe bakinsa da hannun sa saida suka miki dukan tsiya tukun sukace miki rufe idon tinda kayi biyayya zamu barka
Haka adamu jin ance za'a barshi sai ya ji dadi yace na rufe
Ameera tace idan kasake ka bude da wuri to zaka ganka a k'ungunmin daji mai kuraye
Da sauri yace bazan bude da wuri ba
nan suka fita da sond'a suna fita suka kama dariya,
khadija tace wllh ameera ke muguwa ce kinfini dukansa Ameera tace ai yabani haushi ne yadda yake tare yan mata yake taba musu kirji ko wani kalar iskan ci ne wannan oho?
khadija tayi dariya tace ai ya fitini kowa a garin nan yaudai munyi maganin dan banza
Suna tafiya a hanya wasu mutanen sun taho suna hira ameera tace khadija bari mu baiwa wadancen mutunen tsoro tace to
suka rakube a jikin wata bishiya suka saida mutanen suka tunkaro kawai suka fito fuska bak'i k'irin jiki kuma fari kamar fatalwa
Mutanen sukayi baya ameera ta makale murya ta juye hannu tace idan kuka kuskura kuka gudu to zaku mutu
Ai da sauri suka dunk'ule a waje daya suna mazurai suna kerma
......Ameera tace daga ina kuke ? wani acikinsu yace daga dandali muke shine muka taho gida
ameera tace kune marassa kunya har kuka tsaya har wannan lokacin baku dawo gidaba ko
nan suka soma cewa dan Allah kuyi hakuri bazamu sake zama dare ya mana ba awaje
khadija tayo kansu tana wani gurnani kamar wata aljanar gaske tace daga yau idan kuka sake bari dare yamuku to zamu tafi daku duniyar aljannu
Cikin tsoro sukace baza musake ba amana afuwa nan dai basuyi muguntar ba suka barsu suka tafi....
khadija tace bacci nakeji mutafi gida .....
Ameera ta dawo daga labarin da take baima, Yaya ameer shikuwa sai dariya yakeyi harda rike ciki yana jin mugunta irin tasu
ameera ita ma dariyar tayi tace amma yau zaka bini muje dandali ko yace sosai makuwa dan naga adamu
Dariya tayi tace zan nuna maka shi
*SHIN SU WANENE AMEER DA AMEERA*
Mlm shareef shine asalin baban su abba auren gidan aka musu shida matarsa maryam wato inna
Ahmed shine dansu na farko wato abba. Bayan shekara uku maryam tasake haihuwar namiji muhammad wato daddy na birni bayan shekara biyu tasake haihuwar wani namijin Abubakar wato abbu sai autar su Mufeeda ..Abba shi yafara gama makarantar sa yasoma kasuwanci yana da shekara 27 years suka hadu da sadiya wato umma nan suka saba da juna basu wani jima ba suka yi aure
Bayan aurensu da shekara uku muhammed yagama karatun sa yace shi birni zaikoma yaci gaba da karatu nan aka bashi dama mlm shareef yanada abokin a cen kano nan ya mishi waya yace mishi ga muhammad nan wato daddy na birni
yana karatun nan yar gidan wadda ake kira da fadila suka kulla soyayya aikuwa babanta yaji dadi nan da nan akayi auren su
sai Abubakar wato abbu shima yagama karatunsa ya kama kasuwanci Allah yadashi da nana yar cikin garin katsina suna fara soyayya babu bata lokaci aka musu aure
Abba yana yara hudu
safiyan
ameera
hajara
Ibrahim
Sai daddy na birni yana da yara uku
Ameer
Fauziya
Fatima autarsu
abbu kuwa yana da yara biyar
Rashida
Usman
Abdul rashid
Nasser
sai kausar auta
.....yanzu mlm shareef shekarar sa goma da rasuwa lokacin ameera tana yar shekara 2years ya rasu
*wannan kennan*
CIGABAN LABARI
Abbane da abbu da daddy na birni suka shigo sashen inna nan suka gaishe da inna ta amsa
Abbu yace inna dama munzo ta wata magana ne
Inna ta gyara zama tace to ina jinku
Sai abbu yace ameera da ameer ku je wajan umman ku na kiranku
nan suka mike suna fita abbu yajuyo kan inna yace,Inna munaso za'a daura auren 𝙖𝙢𝙚𝙚𝙧 𝙙𝙖 𝙖𝙢𝙚𝙚𝙧𝙖
Gobe saboda ta koma birni taci gaba da karatun ta acen
inna ta dago tana bankawa abbu harara tace....
TO ANAN ZAN DASA AYA SAI MUN HADU DAKU A GOBE INSHA AND kuyi comments da share ko like ngd🥰
[23/10, 09:25] MRS. MU'UTASIM: 🌟𝑨𝑴𝑬𝑬𝑹 𝑫𝑨 𝑨𝑴𝑬𝑬𝑬𝑹𝑨🌟
𝙎𝙏𝙤𝙧𝙮 𝙖𝙣𝙙 𝙬𝙧𝙞𝙩𝙞𝙣𝙜 𝙗𝙮
𝑴𝑨𝑴𝑨𝑵 𝑵𝑼𝑺𝑨𝑰𝑩𝑨 𝑪𝑬 ✍🏻
3
Inna tace amma kai kuwa bukari kazama mahaukaci taya zakace ameera yarinya da ita kace wai ayi mata aure
....Abbu yace inna bawai tarewa zayi ba za a daura auren ne idan takoma birni sai taci gaba da karatu tinda kinga sai ta zama likita da kike fatan zaman ta
Inna tayi jum kafin tace to shikenan na yadda tinda dan uwanta ne shi nasan zai kulamin da ameera
.....Cikin jin dadi abbu yace mungode
Allah yakara girma
tayi murmushi tana kallon diyan nata tace ku fada ma Mufeeda dai suka ce to nan suka fita daga sashen inna
Ameera kuwa tinda taja ameer suka fita ta kaishi wajan umma suka gaisa tana tambayar sa maman sa
Kasa yayi da kai yace suna gaishe ta nan dai suka fito suka nufi sashen mama
suka shiga mama tace a a ga mutanen birni isowa sukayi ya durkusa ya gaisheta
Mama ta amsa da fara'ar ta tana tambayar sa yan gidan yace lfy lau suke sunce agaishe ta
Su rashida ne suka fito daga ciki suna ga yaya ameer
Murmishi ameer yayi yace yan k'annan na
zama sukayi suna bashi labarin school yana dariya sun jima tukun suka fito
Waje suka fita ameera tace yaya kasan kawata khadija kuwa ?
Ameer yace a a ban santa ba
Tace to muje ku gaisa
Da yake yana son zaga garin yace ok muje
suna tafe suna hira har kofar gidansu khadija duk inda suka bi sai mutane sunce la kalli wani saurayi mai kyau kamar balarabe kuma suna kama da ameera
Ita kuwa babu ruwanta sai zuba zancen ta takeyi
......A hanya ne sukayi arangama da lado
aikuwa yayi kanta dama shi kullin da makamin sa yake yawo sbd karma ya hadu da ameera ta gudu
ameera na ganin lado ta labe a bayan ameer
Jin ta rikeshi yace menene ?
ameera tace yaya gashi nan zai dakeni
Ameer yace wanene da hannu tayi mishi nuni da inda lado ke tunkaro su
Lado yace yarinya wana kama dama nace miki duk lokacin da muka hadu saina karya miki kafa
Ameera na zare ido tace please yaya karka bari ya dakeni
Shikuwa ameer so yake yaga bakin kokarin lado
yana matsowa kusan su ameera ta kara kamkame yayan nata
ameer yace kai dakata cikin tsawa
Da sauri lado yaja birki ya tsaya
Ameer yace lfy ?
lado yace wannan yar iskan yarinya jiya saida suka yimin targade ita da kawar ta khadija yana nuna ameera data cakume ameer
Ameer yace to kayi hakuri nawa ne kudin gyara
......Lado yaji kudi saiya saki ransa yace raina dari biyar ne
Ameer ya ciro kudin a jakar sa yabasa yace karka sake koda ka ganta a wani wajan ka daketa
Cikin jindadi lado yace ai ranka ya dade bazan ma ko kallon taba bare duka
Ameer yace to shikenan tashi kaje nan yabar wajan
Ameer yace wai maiyasa ke bakijin magana ne kullin kina fada kamar baki gajiya
turo baki gaba tayi tace to yaya bashi bane yake zagina shine jiya muka rama
kunnan ta ya murde ta saki kara tace waiyo Allah yaya akwai zafi tana yarfa hannu
Harara ya aika mata yace ai daukeki zanyi mukoma birni kowa ma ya huta da wannan fadan naki
Da sauri ameera tace da gaske yaya tana tsalle
yace gobe kuwa zamu tafi nan ta kama murna suka yo gidan
Abba ne zaune shida umma yana fada mata shawarar dasuka yanke na hada auren ameer da ameera
Sosai umma tanuna farin cikin ta taji dadi dan ta gaji da wannan fitinar na ameera tace Allah yasa haka shine mafi alkhairi kaga idan ta kara girma saita tare kafin lokacin tayi hankali
Abba yace hakane kinga zataci gaba da karatun ta acen
Su Ibrahim ne suka shigo shida hajara na biye da shi suka haye kan cinyar abba
Ibrahim yace abba wai sai yaushe zan girma nima kamar yaya safiyan
Umma tayi dariya tace sai ka kara shekara ashirin
Ibrahim yace to umma yaushene gobe idan natashi daga bacci zanganni babba kamar malamin mu na school
Hajara tayi caraf tace hmmm dallah cen bakauye kawai waya cema gobe zaka girma kuma malamin school dinmu uncle mustapha kake hada kanka dashi wannan garjejen k'aton dashi ta karashe maganar tana cuno baki gaba
Ibrahim yace yarinya idan nazama babba jirgi zan siyawa umma da abba suke zuwa saudiya da Dubai
Hajara tace to sai kayi tayi ai yaro
Umma tace to ya isa haka kufice kuyi wanka duba kuga yadda kukayi da kayan jikinku
Ibrahim yace umma anty hajara ce tace muyi gini na kasa shine fa muka bata kayanmu
Hajara a masifance tace mai karya asaka mishi rigar fatalwa ya kwana yana bingel bingel
Abba yayi dariya sudai kullin sai shirme akama gardama nan suka fuce
Abbu ma gidan yanufa shima yafada ma mama cewa gobe za'a daura auren ameer da ameera
Itama ta nuna farin cikinta tace Allah yasanya alkhairi cikin farin ciki abbu yace ameen masoyiya
dariya tayi dan tasan mijin nata badai barkonci ba yace ni ina su rashida kuwa
Tace suna daki yace ok nan suka kama hirar su na miji da mata
Daddy masaukin su ya nufa nan ya tarda ameer da ameera suna ta zancen su yaji dadi dan kuwa yasan irin son da ameer yakewa kanwar tasa
Sallama yamusu suka amsa gaishe shi ameera tayi tace natafi
Daddy yace to yar gidan inna, nan ta fice abinta
Daddy yace ameer gobe zaa daura auren ka
A razane yadago yana kallon sa yace dad aure na kuma nidawa
Murmishi daddy yayi ganin yadda ya rude alokaci guda yace kaida ameera
Ai tuni ameer yasaki fuska yace to amma dad ai ameera