Showing 69001 words to 72000 words out of 175796 words

Chapter 24 - AMIR DA AMIRA Complete by Maman Nusaiba.txt

07 Aug 2025

3347

jin hayani


Ikram tace lafiya kuke daga murya haka, bata " lura dasu ameera ba " tana karaso wa kusan su nan ameera ta fada jikin ikram tasaki kuka



Da mamaki ikram ke kallon ameera,, tace baby wani mai " tsautsayin ne ya taba min ke yar lelen ameer da momsy ta,, tana bubuga bayan ta,



Fatima da jamila suka karaso wajan su,, nan ikram tace kai amma ina da amare agidan nan "


Ameera ta dago tana turo baki gaba kamar zata sake , fashewa da kuka tace momsy ba waccen bace ta zageni wai zan zanje " room dinki




Ikram kallon inda take nuna mata "" tayi kanwar ta sumayya tagani, tace ke sumayya " waye yace ki zageta " kinsan ko su waye su,, kinsan wani matsayi garesu a wajena " amma har kike zaginta to kishiga,, hankalin ki " duk wanda yakeson zaman lfy to karya tabamin baby


Baki asake sumayya take, kallon antyn ,, nata tace to ai ni bansan itace " babyn da kike fada ba



Banza ikram tayi mata,, ta jasu suka zauna " nan suka gaisa tana tambayar " ina mazajen nasu


Fatima tace ai momsy suna waje " sunce sunason gaisawa " dake



Ikram tace to bari na kira ameer ,, nace suje dakin baki " zan tarar dasu




Mutanen falon kuwa sai kallon su ameera sukeyi " suna cewa wai a ina, ikram tasamu kyakkyawan yara " haka



Ikram tace mama " ga baby wadda nake baki labarin ta "


Wadda aka kira da mama ta washe, baki tace kuzo nan dukan ku,,


Kusan ta suka matsa nan suka gaisheta ,, tukun suka koma,, inda suka tashi nan aka kawo musu baby's din




Mace da namiji ne, ameera ji tayi kamar ta hadiyesu, saboda sosai sun shiga ranta



Fatima ma rumgume namijin tayi,, tana murmishi


Macen ameera tabawa,, jamila kallon babyn jamila ,, tayi tana cewa muma wataran " mune muka haifi namu "



Ikram taje sun gaisa dasu,, Ameer kuma taji dadi harda su bilal



Sai bayan isha"i tukun su ameera akazo daukarsu


Kullin Haka suke zuwa su yini, gidan ikram har lokacin suna yayi nan sukayo siyayya tagani tafada su ukun, hadda mazajen su




Ranar suna yara,, sukaci sunan


*AMEER DA AMEERA*


aikuwa lokacin,, su ameera kamar ,, tayi ihu dan dadi ansaka " sunan ta dana mijinta kai amma momsy tabiya su


Haka shima ameer,, yayi farin ciki marar musaltuwa, jin ansaka,, sunan shi dana wife dinshi




Haka akasha suna,, kamar aure ne ake gidan yacika dam


Su anty haleema anzo suna tana ganin ameera nan da nan ta rude,, ita a tunanin ta ameera aljana ce ba mutum,, ba saida, taga dai mutum ce tukun tasaki jikinta,, amma bataso suhada ido da ameera


Su ameera kirjin biki,, ansha kwalliya ita da Fatima da jamila ,, ga kayan da suka kawo,,Ikram kamar ta goyasu saboda murna



Haka akayi suna taro yatashi lfy,, aka bar mai jego da jariran ta



*BAYAN SATI BIYU*

Yau ne ummi mufeeda zata,, koma dubai su ameera sunzo rakiya " suna zaune a falo hajara tafito,


Da mamaki ameera tace hajara dama,, kina nan dariya tayi tace "tace ina, nan ai Dubai zamu tafi,, nida ummi mufeeda




Ameera tace, wai ummi da gaske zaku " tafi dubai da hajara


Mufeeda tace eh, ameera da ita zantafi,, bayan angama bikin ku, ne na samu " yaya ahmed da ,, zancen abani "" Hajara babu muso " yace yabani ita


Cike da farin ciki ameera "tace to yayi kyau,, gaskiya, naji dadi




Nan aka soma fiddo da, kayansu waje ana zubawa ", a mota


Hajara mike,, kamar wani abu zatayi tace ", tace to jama'a mu zamutafi,, kasar turai sai adarul samalu tana koma ta zauna



Dariya su mom sukayi,, sosai

Mom tace hajara kinsan ina ne kuwa darul samalu kike cewa, sai acen


Tace, ina nufin sai wani lokacin dan saina zama injiniyar computer,,


Ameera tace to lahira cedai darul salamu ba wani wajeba,, ko idan kika koma,, dubai din bazamu,, zake ganin kiba


Da sauri hajara, ta koma jikin,, ummi mufeeda tace " a a gaskiya inason na sake ganinku,, mana


Dariya suka mata,, nan suka " fita kowa yahau mota " suka nufi airport suna zuwa,, babu jimawa" jirginsu,, ya yazo nan aka soma kara " babu bata lokaci suka shiga saida su mom sukaga tashinsu " tukun suka dawo gida su ameera ,, sukayi gidan su


Suna zuwa tayi kitchen ta daura,, musu abinci " dawowa tayi falon taga ameer " yana nan kusa, dashi tadawo tace yaya gobe fa zamu koma school da islamiya,, hutun,, mu ya kare


Kallon ta yakeyi yace, yanzu kenan gobe sai, school da islamiya ko


Tace eh yaya insha Allah

Yace to Allah yakaimu goben insha Allah

Tace amen yaya bari naje magama girkin kar yunwa, takama min, kai


Ameer yace to bari na kwanta , kafin kigama tace to


Nan tamike tayi kitchen



Da dare,, suna " zaune bayan,, salla " isha"i saiga fatima tashigo da sallama amsa mata sukayi,, nan ta karaso,, zama tayi tana gaishe su suka amsa mata


Fatima tace, anty ameera momsy ta kira tace nahada, ku video call nan ta danna,, kiran


Babu jimawa", Ikram ta daga kiran tana cewa hello Fatima ina baby take,, tin dazun nake kiran ta bata dagawa


Saurin, matsowa " Ameera tayi tace waiyo Allah yau nayiwa,, momsy na lefi " wayar ce a room take na saka ta a caji ne, ni kuma ina falo " ga yaya



Murmishi ikram tayi,, tace ina yake,, wayar suka , gyara suka saka ,, Ameer a tsakiya " nan ya gaishe ta



Ameera tace , momsy ina takwara,, da mijina suke bangansu ba ko suna wajan uncle ne


Ikram tace ,, a a gasu nan ta rungumosu, tana gyara " musu kwanciya ajikinsu,, suna tsaye basuyi bacci ba


Ameer yace anty kinga wife tashi kyau, kalli har dariya takemin taga mijinta,,


Ameera ta harare shi ta kallo wayar, tace momsy wllh mijina yafi kyau kinganshi hadadden,,, gaye dashi saima yagirma,,


Fatima tace,, dukkansu,, suna da kyau " sosai



Dariya ikram tayi jin yadda suke muso ,, tace duka suna da kyau kamar ku, kunga fa sunan ku garesu,, saboda suyi kamanni "" kamar ku yasa nasaka musu,,, sunanku dan haka kubari,,, su girma tukun sai,, a tantance"


Ameera tace to shikenan momsy

Haka sukaci gaba da hira , har wajan taran dare,, tukun suka kashe kiran " fatima, ta koma sashenta



Washe gari duk sun, fito mazan,, zasuje wajan aiki matan kuma,, school " haka suka fita su dukansu,,


Suna tashi,, daga school din gida suka nufo,, bayan sallar la'asar sukayi shirin islamiya,, dan yau akwai , taron malamai a islamiyar, tasu kuma,, za ake daukar dalibi daya acikin,, aji yayi wa'azi ko wani jawabin mai kyau ko labari sahabbai ko na innabawa ,, da sauransu,



Tin kafin su kai islamiyar,, Nafeesa ta, kira ameera tace besty maza,, kizo nan da minti goma zaa fara program din ,, Ameera tace gani nan zamu shiga ciki nan ta kashe kiran suka fita,, a motar wajan program din suka nufa, suka zauna



Babu bata lokaci aka soma gabatar da program din , malaman suka fara jawabi ,, sai suka gama tukun aka soma kiran dalibai



Nafeesa,, aka kira,, aka ce tazo ta bada tarihin annabawa,, ko wata kissa



Nafeesa ta to ta amshi,, spikar tace assalam alaikum suka amsa mata da amin wa'alaikum salam ,,



Nafeesa tace yan uwana masu albarka da kuma,, iyayenmu laman mu ina mana barka da wannan lokacin da fatan,, duk kuna lfy Allah , yasa duk wanda yazo taron nan lfy yakaishi, gidan sa lfy,, suka amsa da ameen



Nafeesa tace wata rana, wani sahabi ya tambayi manzon,, Allah (S.A.W .) Yace wani aiki ne Allah yafi so acikin aiyukan, musulinci wannene yafi



Sai annabi Muhammad (S.A.W) yace (tud'u" imun d'a"ama) kaciyar ga mai jin yunwa ka taimakawa marar shi (watta q'ara"u salama ala man arabta waman lam"arifu) kuma kayi sallama, ga mutum koka sanshi ko baka sanshi ba ,,wannan hadisin ya koya mana mashimmancin, bayar da gudun mawa ta abinci

Ko kayi kunu ,, ko kayi tuwo ko kabada ruwa sanyi,, ko kayi kosai duk zaka iya basai kace,, sai abinci mai tsada ba ,, a a koda ruwan sanyi ne kabawa mai jin kishirwa, to ka taimakesa,, kuma zaka samu ladan sa


Dan haka yan uwa mu taimaka wa marayu,, masu bukatar taimako ko wanda suke kasan mu


Nagode nafeesa ta fada tana ajiye abin,, maganar



Mutanen wajan, sukace ce Allahu akbar


Nan malamin ya yace masha Allah nafeesa mungode da tunatarwa,, Allah yasa ka da alkhairi


Yanzu muna kiran ameera, tazo tadan bamu wata kissar, ko labarin sahabbai, nan ameera tamike " tazo ta amshi,, abin maganar


Tace assalam alaikum yan uwan mu da iyayen mu malaman mu " ina fatan kuna lfy ,, Allah yasa,, yadda kowa yazo wajan, nan lfy Allah yamaida" kowa gidan shi lfy

Amsa mata sallamar,, sukayi har da gaisuwar,


Tace wata rana antaba, tambayar mala"ikan mutuwa azara"ilu


Ka taba dariya


Na taba dariya sau daya

Kataba tausayi

yace na taba tausayi sau daya



Kataba mamaki


Yace na taba mamaki sai daya


To yaushe kayi dariya ya mala'ikan mutuwa azara'ilu


Yace wata rana nazo kabar ran wanii bawan Allah minti daya in karbi ranshi, shikuwa alokacin yabada dinki takalmin sa fadi yake kasamin fata wanda zai shekara goma ina anfani dashi bai lalaci ba , azara'ilu yace wannan maganar tasani dariya




Tausayin kuwa shine wata rana nazo daukar wata mata,, atsakiyar daji ga ciki tana cikin halin nakuda ga wurin babu kowa,, haka na zare ran baiwar Allah nan nabar jaririn yana kuka


Mamakin kuwa shine wata rana, nazo daukar ran wani bawan Allah sainaga kawashi tana shaske da kamshi ga wasu mala"ikun rahama zunzo tafiya da ranshi saboda tsabar,, aikin sa na alkhairi



sai aka fadamin cewa, jaririn nan ne ya girma yake aikin alkhairi



To kunga wannan yana muna nuni da mutuwa bata shawara,, dakowa idan lokacin ta yayi,, saidai kaga mala"iku a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login