Showing 111001 words to 114000 words out of 175796 words
Chapter 38 - AMIR DA AMIRA Complete by Maman Nusaiba.txt
tayi,, kunya,, ita dai Allah yana gani,,Anass irin mazan ne da basa barin matan su , suhuta,, ko wanka , yayi idan yaga fatima " ta tube zatayi wanka tofa saidai tayi biyu
Shiyasa har yanzu takasa sabawa,, da nacin anass baya barinta tayi bacci da dare,, amma bata nuna mishi ta gajiya duk da , tana da karancin ,, shekaru amma , jurewa takeyi saboda ", nasihar da ikram ke mata ,, shiyasa bata korafi koda kuwa yaushe zasukai yaune ma bakinta ya subuce mata ta fada,,, shima bata so ya fito ba
Shafa bayan ta yayi yace,, kiyi hakuri dani matata,, kedin ce kike rikita ne da salon ki, nasan kina kokari amma ki kara akan wanda,, kikeyi haka Allah yayini " nasan kema wata rana zaki zama irina " am so sorry shiyasa kike zazzabi ko dan kwanan nan na takura miki,, to zan rage
Dagowa tayi tana kallon shi tace da gaske , sweetheart, amma,, yau ninake nemanka " kaji yadda cikina ke motsi da kazo
Dariya anass yayi yace to ikon Allah , yau kuma har nemana kikeyi to ai gani duk abinda kikeso,, zan miki
Fatima tace nagode sweetheart,, dina " ta koma jikin shi
Shafa cikin, nata yayi yace , wai anya kuwa banyi ajiya ba a wannan shafaffan cikin,, kilama,, baby nane keson ganawa " da babanshi
Baki , da hanci fatima ta saki tana kallon mijin nata,, tace , menene kuma ajiya har kake wai baby ina yake babyn
Hancinta yaja yace to bari na fito miki a mutum , ina nufin, nabaki ciki nayi ajiyar baby na anan yana,, shafo ,, marar ta
Wani yanayi,, Fatima taji jin yadda yaje yawo da hanun shi,, a kan marar ta,,
Shima haka yakeji danshi,, abu kadan yake daurashi akan hanya
Da sauri fatima ta koma jikin sa tana sauke numfashi ,, tace sweetheart please mana
Bude idon shi yayi yana saukesu,, akan ta,, harya soma cenja launi saboda tsabar jaraba irin ta anass ,, murya cen kasa yace menene mai kikeso namiki
Fatima tace yunwa nakeji kuma banyi girki ba please kaje ka siyomin kaji
Janyota yayi yace,, yanzu zan baki " zaki dena jin yunwa
Kallon shi tayi tace to ina abincin ,,,, kanshi yanuna mata , yaja bargo ya rufesu
Misalin karfe 1:00PM doctor aisha tazo gidan su ameera ita da, Muhammed
Da murna ameera ta taresu tana oyoyo momma ,
Itama doctor aisha taji dadin ganin yadda jikin ameera ya warware sosai
Nan suka zauna sosai suke hira doctor aisha tace kunga bamuzo ba sai yau wllh aiki ne yayi min yawa shiyasa kukajimu shuru
Ameera tace ba komai momma ai irin aikin ku baa samun lokaci sosai , mama tace hakane daughter
Joshow yace yauwa dama so nake kuzo,,, munason " nida mama da yarana zamu musulinta,, mu zama irin ku ,, zaman ameera agidan nan idan naji tana karanta wannan littafin naku sainaji nutsuwa ,, tazo min ina sha"awar shiga musulinci ,, da zuciya daya " kuma inason annabi Muhammad s.a.w. da zuciya daya duk muna sonshi nida family na ,, yakai karshen maganar yana kashewa " da kuka saboda ubangiji ,, ya saka mishi tsoron sa a ranshi
Mama tace nima nayi imani da ubangiji daya , inason,, son annabi Muhammad s.a.w munason ,, musulinta nida dana da jikoki na
Marus ma yace nima inason nashiga nakeyin irin na mommy na "
Kabbara su ameera sukayi ,, Ameera tazo ta rungume mama tana hawayen , samun karuwar da musulinci yayi
Muhammed yace,, Alhamdulillah masha Allah ,,Allah yabin godiya ,, munji dadi, sosai da Allah yasa kuna da rabon musulinci a duniya lalle ubangiji yana sonku da rahamar sa,, yanzu zan ke fadin kalmar shiga musulinci ,, duk abin na fada mu fada ,,, sukace to
Zama Muhammed yayi yace soma ,, fada musu kalmar shahada da guda ,, guda har suka fadi " a daidai muhammed na murmishi namikawa,, joshow hannu yace assalam alaikum .
Shima joshow yana dariya mai hade da kuka ya mikawa ,, Muhammed hannu yace amin wa'alaikum salam sukayi musabaha,, dama ya iya kalmar sallama shiyasa baiji wuyar amsawa, Muhammed sallamar " shiba
Muhammed yasake mikawa marus hannu yace assalam alaikum ,, Marus yace amin wa'alaikum salam , nan sukayi musabaha
Doctor aisha ma tacewa mama assalam alaikum ,, amsawa itama tayi kamar yadda taji sunayi
Ameera sujjada tayi na godiya ga Allah tana yima Allah kirari
Nutsuwa sukayi suna sauraron,, abinda muhammed yake fada musu akan musulinci ,, ya nuna musu yadda zasuyi wankan shiga musulinci ,, da yadda , zasuyi kuka tsarki da alwala da salla ,, nan yacewa yabishi gidansu ,, zaike koya mishi karatu acen zaiyi sati " danya koyi abubu ,, shida marus
Ameera tace yauwa yanzu kowa ya zabi ,, sunan da yakeso asaka ", mishi
Mama tace tana son sunan , zainab , Ameera tace masha Allah suna mai dadi
Beauty tace mommy ,, ni kuma mufeeda nakeso,, Ameera na dariyar farin ciki tace sunan kanwar abbana ,, masha Allah mufeeda mai babban suna
Marus yace ni kuma inason asakamin Abubakar sadeeq " suka masha Allah sunan sahabin annabi s a w kuma surukinsa
Joshow yace ni kuma umar nake so ,, Muhammed yace masha Allah shima sunan sahabin innaba s a w
Nan su doctor aisha suka yini har bayan isha"i muhammed yana munawa joshow da marus yadda ake salla wanda yanzu suka dawo umar da abubakar sadeeq
Su ameera kuwa na nunawa su mama da beauty ,
Farin ciki sosai sukeyi ba kamar ameera ma haka ta kwana tana nafilfili,, na godiya ga Allah tana , addu'ar Allah ya taimaketa " akan wannan jahadin dake gabanta ,, da tana ganin ita kadai yanzu su bakwai ne,, dan haka ta kasa bacci daboda farin ciki
Yau tinda wuri , Anass ya hirya fatima sukaje asibiti dan jiya kwana tayi ,, tana sheka mishi amai ajiki da tayi saita ce ,, mishi ruwa shikuwa " kawai saiya bata,, tana sha daga amjima zata maidoshi ", ya kamar , duk tayi laushi tafiyar ma bata iya yi
Shi kuma duk yarude ganin fatima a wannan halin,,
Suna zuwa babu bata lokaci aka kaisu dakin gwaji nan aka cemusu ciki ne da fatima harna wata uku,, amma yana bata,,wahala sosai dan haka ruwa za'a saka mata
Farin ciki awajan anass kamar yazuba ruwa a kasa yasha fadi yake Alhamdulillah , nima nagirma zan zama baba
Bayan awa daya ruwan,, yakare aka sallamesu " suka yo gidan maman anass. Yakira " ameer yafada mishi ,, sosai ameer ya tayashi farin ciki
Saida yatuno lokacin shima haka yaji, yanzu gashi basa garesa, hawaye ne yazubo mishi yana , sharewa wasu na zubowa
*thank you sosai masoya ina godiya da addu'o'i ku*🥰🥰
[28/10, 14:29] MRS. MU'UTASIM: *🌟AMEER DA AMEERA 🌟*
*RUBUTAWA DA TSARAWA*
*MAMAN NUSAIBA CE ✍️*
*wannan shafin na sadaukar gareku .JARUMAI WRITERS ASSOCIATION 📚🖊️* ina alfahari daku
💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*
https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl
_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_
*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*
*67—68*
Gidan , mama suka je,, da murnan mama ta taresu, tana fadin oyoyo yarana
Yar dariya anass yayi ganin mama ta rungume fatima, yace kai mama " ni baki ganni bane " kin wani shareni , sai fatima kika rungume
Buge mishi baki mama " tana dariya tace anki a ayi hogging dinka mai zakayi ni ta ya' ta nake ba kaiba , q'ato dakai,, har kake wani ,, andena kulaka wai yaushe zaka girma,, ne anass
Fatima tamishi gwalo tana boyewa ,, a bayan mama
Mama taji jikin fatima da zafi da sauri ta juya ta riko ffatima takaita kan kujerar falon ta zaunar ta,, tana fadin yarinya ta maiyasa meki naji jikinki ,, zafi
Boye fuskar ta fatima tayi tana yar dariya ,, dan kunyar mama takeji bataso a fada wa tana da ciki
Dariya anass ,, yace mama ai , wannan zafin jikin nata jikanki ne yasata haka bakiga " duk ta rame ba ,, jiya ko bacci bamuyi " kwana tayi tana kwararamin,, ajikina bakiji duk karnin amai muke " yana kallon fatima data ,, kara shigewa bayan mama
Da farin ciki kwance afuska mama tace , wai anass kana nufin kace fatima ciki da ita kai Alhamdulillah ,, Allah abin godiya " sannu fatima Allah yaraba, lfy kinji
Shi kam anass ko a kwalar rigarshi " sai kallon fatima yake " yana lumshe ido , saboda rajabar tashi ta motsa, so da yake mama ta tafi ,, ya dauke matar shi su shiga ,,daga ciki ya rage zafi
Fatima kam kuka tasa,, jin anass na zaro zancen,, kamar an jonashi ga kunyar mama da takeji " ga anass na tona mata asiri
Juyota mama tayi tace , a a fatima menene " na kuka keda zakiyi godiya ga Allah daya baki ,, kyauta " amma kike kuka
Cusa kanta tayi a cinyar mama tana kara sautin kuka tace mama,, ba yaya bane take cewa wai najikashi da amai " kuma wai " ina karnin amai
Shafa kanta mama tayi tace to shikenan kiyi hakuri kinji,, zan rama miki ne yanzu " mai kikeso kici na dafa miki
Dagowa tayi tana , kallon anass suna hada ido,, ya aika mata da kyakkyawan murmishi ,, mai sakata a wata duniyar, ta kara kallon shi ,, a karo na biyu " taga har idonshi ya cenja,, dage mata gira daya yayi " da hannu yake rokonta ta tafi dakinsa ta kwanta
Ba yadda ta iya haka , ta kalli mama tace,, mama bacci nakeji " idan natashi zanci , tuwo da miyar kuka yaji daddawa ,, da barkono shi bakeso "
Murmishi mama tayi tace to yarinya ta kije dakina ki kwanta
Kallon anass fatima tayi