Showing 138001 words to 141000 words out of 175796 words

Chapter 47 - AMIR DA AMIRA Complete by Maman Nusaiba.txt

07 Aug 2025

3337

taga , karima na motse hannun ta


Murmishi tayi tace to kiyi hakuri mana ameera ki kyale ,, muje waje doctor dazaizo yana hanya inaga aikin dare ma zaa mata ,


Fita zukayi , waje suka zauna amma ameera taki dena kukan ,, kallon umar keyi ,, cike da tausayi " yace muje gida idan tasamu sauki saiki zo ", dama saida nace bazakizo ba saboda , wannan kukan naki maza shige muje gida yana mikewa


Doctor aisha ce tafito tana kallon su tace ,, to bata dena kukan ba , umar yace inafa gida zan kaita " da dare zan dawo

Kin binshi tayi , juyowa yayi yace wai ameera ina wasa dake ne nace kishige muje gida ,, yanzu saboda wannan kukan saiki jawa kanki ciwo , to muje



Binshi tayi suka tafi suna , , fitowa daga hospital din motar su ameer na sayo kai ,


Ameera taji gabanta ya fadi kallon motar tayi , har suka shiga ciki ,, su kuma sukayi gida


Ana sauke ameer ,, ya fito yabiya mai motar kudin shi , kafin yayi cikin hospital din

Da farin ciki doctor aisha ta ,, tareshi tana fadin oyoyo jikana , gaskiya kunyi sauri

Murmishi yayi yana gaishe ta , amsawa tayi nan sukayi office din ta


Saida yadan huta tukun,, yace muje naga marar lfyr , nan sukayo dakin da karima ke ciki


Shiga suka , baki sake ameer ke kallon fuskar karima " yace kakata ,, kinga abinda nagani kuwa

Kallon shi tayi kafin ta kalli karima , itama sai yanzu taga yadda suke tsananin kama da karima , tace ikon Allah wllh kamar ku daya Allah buwayi gagara musali ,


Ameer yace gaskiya , Allah mai iko , nan yadauki kayan aiki yaduba ta nan yaga dai sanyi ne ya tsayar mata daduk wasu abubuwan dake mutsi ajikin dan adam, , kallon doctor aisha yayi yace gaskiya wannan akaita dakin da ake gashin basu shanyayyen ,, jiki a mata gashi kuma yau da dare saboda sanyi yashigeta , sosai , yanzu zanje hotel , na huta bayan sallar isha"i " sainazo muyi aikin



Doctor aisha tace to shikenan ,, Allah yakaimu daren lfy nan suka fita


Ameer ya wuce hotel nan yakama daki ya shiga wanka yafara yi kafin yabatar da sallar isha"i karfe 9:00 PM dai dai tamishi a cikin hospital ,, dama tuni doctor aisha tazo shi take jira ,, nan aka turo karima zuwa dakin da za'a mata aiki


Koda su ameera sukaje gida sai tunanin motar data gani takeyi , ganin abin zai bata wahala yasa tayi watsi da tunanin ,, ta dauko alqur"ani mai girma taringa karantawa,, saida tasoma jin bacci tukun ta ajiye , tayi addu'a ta kwanta ,


Su ameer nashiga,, nan aka zonawa karima kayan aiki tukun suka soma ,, aikinsu ,


Umar da muhammed na waje ,, sai zarya sukeyi suna addu'ar Allah yasa ayi a sa'a


Bayan awa uku aka bude kofar,, da sauri suka kalli kofar ameer ne yafito , doctor aisha na biye , dashi ,, tsayawa sukayi a wajansu umar


Umar ko kallon ameer yakeyi kamar yasamu tv , yace doctor wllh kana kama da matata

Murmishi ameer yayi yace ,,haka ne nima nagani wllh haka Allah yake mutane ,, masu kama daya

Umar yace hakane ya jikin ,, doctor aisha tace Alhamdulillah munyi nasara ", insha Allah tana tashi nomal zata tashi


Cike da murna ,, sosai umar ke musu godiya , hadda dan kukan shi ,

Ameer yace tinda angama aikin,, ni gobe insha Allah zan koma kano idan ta tashi saiki ,, dubata " doctor aisha tace ,, ok amma gobe zaka tafi baka barin zuwa jibi sai ka tafi

Ameer yace no inada aiyukane sosai agabana barinsu nayi nazo to tinda angama ,, saina koma gida ko


Doctor aisha tace to shikenan Allah yakaimu goben , amma kabiyo tanan kafin katafi ,,,Ameer yace to insha Allah nan ya tafi zuwa hotel din daya kama mamakin " wannan kamanni daya gani sunayi shida karima ,, ahaka har bacci yayi gaba dashi


Umar ko cike yake da farin ciki yana dawowa yafadawa mama da ameera ,,anyi aikin lfy gobe zata tashi ,,dan haka da karfe goma sutafi su duka asibitin ,


Ameera ko kan murna har sujjada tayi na mika godiyar ,, ta ga Allah sosai taji dadi zata ga anty karima dinta


Doctor aisha ma tayi farin cikin samun nasarar ,, dasukayi na aikin nasu


Washe gari tin karfe 8:30 am , ameer yabar hotel din yaje hospital din ,, yana zuwa yaga muhammed ,, a zaune wata yarinya na kuka a gaban shi yana , rarrashin " ta amma taki dena kukan

Sallama yawa muhammed ,, ya amsa nan suka gaisa

Kallon " yarinyar yayi yace, Muhammed wannan mai kama dani , dinfa


Kallon shi yayi ya kalli ikram yace , gaskiya kuna tsananin kama ,, wllh wannan diyar sister din karima ce


Ameer yace , eh gashima suna kama da karima din , yace zo nan baby tana mikawa ikram hannu

Dena kukan tayi ta dago tana , kallon ameer dake mata murmishi sai kuma ta kalli muhammed ,, tace daddy mommy tana nuna dakin da doctor aisha tashiga,,


Dagota muhammed yayi yace , to kiyi shuru mommy yanzu zata fito kije uncle na kiranki , yana nuna mata ameer


Sauka tayi daga jikin shi ta nufi ameer , tana bata fuska kamar zatayi kuka ,, ,hannu ameer ya bude mata , tana zuwa ta shige jikin sa , ta kuka tace daddy


Wani sanyi ameer yaji na ratse shi daya rungume ikram , yana jin yadda sonta ke shigar shi,, wai shine ake kira da daddy ,, yanzu da ameera , na nan tashima ta haifa mishi ,, masu cemishi daddy ,, jin takara saka kuka ,, ya ce yi shuru baby yanzu zatazo " suna a haka saiga doctor aisha ta fito , tana nufosu ,

Murmishi tayi tace , yarinya ta ce zo inji waya taba min ke


Makale kafada tayi tana kara kwanciya jikin ameer


Dariya doctor aisha tayi tace ,, to kai ameer kasamu diya , takizuwa

Murmishi ameer yayi yace dan Allah kibani ita yarinya tashiga raina ,, doctor tace tab , aikuwa bazaka samu ba " muma rikonta aka bani , mamanta ", kanwar wannan marar lfy ce


Ameer yace eh muhammed ya fadamin to ni zan wuce ,, sai kuma wani lokacin yana ,, mike ganin ikram ta sauka akanshi

Ikram ko na ganin yamike ", takama hannun shi tana fadin daddy , daddy , daddy


Dariya sukayi jin tana kiranshi kamar waka , doctor aisha , tace to anturo kudin zan turama ta account bank dinka ,,


Ameer yace no basai anbiyani , kyauta na mata nizan wuce, kar jirgin mu , ya sauka banje ba


Da kyer aka raba ameer da ikram tana kuka tana mika mishi hannu fadi take daddy ,,Ameer ko ji yayi kamar ya sace yarinyar sutafo yadda take, kuka har cikin zuciyar shi yakejin kukan nata haka dai yatafi gida



Ikram ko tana kuka har tayi bacci , rungume ta muhammed ,, yayi yace kaji yarinya yar nema ,, kamar ta taba ganinshi ta ringa kuka irin wannan ,



Su ameera ne suka shigo ,, zama sukayi aka gaisa suna jira karima ta tashi

Wata nosee tafito tana fadin ranki yadade ,, marar lfyr mu ta tashi


Da sauri suka shiga ciki , ameera ta rigasu shiga tana son karima ta fara tozali ta ita , ganin karima ,, a zaune da sauri ta isa " tace anty na tana rungume ta


Itama karima sai kuka takeyi tana fadin kanwata ,, kece dagowa ameera , tayi tace eh anty nice gani


Zama tayi kusanta tana fadin kin gani ,, mafarkin naki danakeyi gashi yazama ,, gaskiya nazo garinku danginki sun musulinta ,, ga kuma yaranmu


Da sauri karima ta kalli ameera jinjina , kai ameera tayi alamar , da gaske take


Abubakar da mufeeda , ko wajan su suka matso , Abubakar " yace mommy wannan wacece mai kamarki , ko sister dinki ce " mufeeda ma kallon Karima tayi sai kuma ta kalli ameera ,, tace to mommy wannan tana kama dake , sister kine ko



Karima ko kallon su take sosai tana hawaye tace nima mommy dinkuce kuzo


Makale kafada abubakar , yayi yace a a ga mommy nan " saidai muce miki anty ,, mommy kinji tace itama mother , dinmu , ne wai


Murmishi ameera tayi tace eh mommy dinku ce ,, ita ta haifeku , kuje inda take


Zuwa sukayi ta rungume su sosai , take kuka umar ne yakaraso , shima rungume shi tayi tana godiya ga Allah daya kawota ahalinta ,



Su mama ma rungume ta sukayi sosai suke farin ciki ,, doctor ko tasha godiya sosai wajan su mama da umar har ameera , nan aka basu sallama sukayo gida


Sosai mutanen garin ke al"ajabin wannan lamari ,,wai ashe yan gidan abin bauta ne suka dauke karima sosai ake zuwa ganin karima,,


Yanxu karima na samun sauki sosai , Dan haka suka shirya tafiya kano kai ameera gida


Doctor aisha ma tace itama zataje nan sukaje kasuwa akaiwa su ameera sayayya sosai sai yamma suka dawo gida , da dare ko kusan kwana sukayi suna hira dan gobe zasubi jirgin safiya zuwa kano



Washe gari da wuri kowa yashirya ,, aka shiga mota zuwa legos ,, nan da nan sukaje ,, basu jimaba jirgin kano yazo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login