Showing 165001 words to 168000 words out of 175796 words
Chapter 56 - AMIR DA AMIRA Complete by Maman Nusaiba.txt
jikar mu ta hada familyn masha Allah kuma mundazama musulmai Alhamdulillah zamuce
Daddy da abba da ubbu suka amsa da ameen gaskiya munji dadin haduwar wannan family ashe batan ameera alkhairi garemu masha Allah
Muhammed ne ya mike yace to daddy zan tafi gida ga ikram nan bayan kwana biyu zanzo daukar ta
Daddy yace baka tsayawa akira la'asar da yamma sanyin marece saika tafi
Murmishi muhammed yayi yace a a zanje gida nayi wanka ne ko wanka banyiba nazo to zan wuce
Inna tace dan kan uba shiyasa ashe nakejin falon yana tsami ashe kaine kazami , shiyasa ka kasa samun matar aure , yowama zai auri miji kazami ,saidai irinka kalle ka kamar wani dodo duk kayi baki kamar kayi birgima a toka tana banka mishi harara
Dariya sukayi yan falon ameer yace kai inna ke yanzu wannan ranar ma bazaki hakura da masifar nanva koda yake anyo gado ai , yana rufe baki
Inna ta hannu biyu aka ta innalillahi wa inna ilaihin raju'un Allah ameeru yau ni kake zaki shikenan yanzu Muhammadu kana ganinshi yake zagina , tana goge fuska da sharen zaninta
Daddy yace yi hakuri ai yau bamai rabani dashi dukan kawo wuka zanmiki tinda ya tabaki , da hancin sa kamar karas irin na naki
Inna tace kaima kaci bindin ubanka , nice mai hancin kamar karas to wllh na kare zama daku agidan ai Alhamdulillah tinda Allah yakawo min dangina , saimu koma asalina cen nazauna ana gama bikin fauziya da safiyanu zan tafi ,,badai ni kukewa baa ba zaku ga hukuncin dazan yanke
Abbu ne yace yi hakuri inna bafa haka yake nufiba kiyi hakuri innar ameera
Murmishi tayi tace kunci darajar ameera , saida tafi amma na fasa zanje dai ziyara
Muhammed yasake cewa to sai anjima mommy natafi nayason hajara ta rakashi amma yana jin kunya
Mommy tace to kabar mana ikram anan yace to gatanan ,
Harya kai bakin kofa ikram ta waiwayo ai da dan gudun ta ta bishi tasoma fadin daddy , nima daddy
Dariya sukayi mommy tace a a mai sunan daddyn yara tafi da yarku ,wannan koka barta saidai ta duma mana gida da ihun kukanta
Muhammed yace to mommy nima fa bafa zuciya ta ta yarda na barta ba kawai dai namuku kara
Murmishi mommy tayi tace kuje bama so ma ka gaishe da doctor din ,yace to nan yadauke ikram tana dariya ganin ya dauke ta suka tafi gida
Kowa tashi yayi inna taje aje ahuta da dare sai ayi hira nan kowa yabar falon
Da sauri ameera ke taka stars din dan so take ta je tayi dan bacci kan ayi la'asar tana zuwa ta kwana ko numfashi bata kaiba ameer yashigo
Yace wannan sauri haba wife na , ameera tace na gaji ne yaya bacci nakesonyi
Murmishi yayi yazo bayanta ya kwanta janyota jikinsa yayi yaja musu blanket , nan bacci yayi gaba dasu
*nima nace bacci nakeji bari naje wajan inna ta baffa*
[30/10, 19:24] MRS. MU'UTASIM: *🌟𝐀𝐌𝐄𝐄𝐑 𝐃𝐀 𝐀𝐌𝐄𝐄𝐑𝐀🌟*
*𝙎𝙩𝙤𝙧𝙮 𝙖𝙣𝙙 𝙬𝙧𝙞𝙩𝙞𝙣𝙜 𝙗𝙮*
*𝐌𝐀𝐌𝐀𝐍 𝐍𝐔𝐒𝐀𝐈𝐁𝐀 𝐂𝐄 ✍🏻*
💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*
https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl
_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_
*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*
Wannan shafin na sadaukar gareki *ummu shukhura* antynmu kiji dadinki da wannan fage 🥰🥰🥰🥰
*89—90*
Muhammed tinda yatafi yake ta tunanin hajara sai murmishi yake tayi yana dravin , Ikram na kiranshi baima jitaba saida tasa kuka da sauri yadawo daga tunanin dayake yi ,yace yar mommy maifaru ,,bata fuska tayi kamar zatayi kuka tace daddy wannan tana nuna mishi sweet din hannun ta takasa budewa ,amsa yayi yabude yabata takoma ta zauna tana dariya anbude mata ,nan sukaci gaba da tafiya
Inna tafara fitowa falo tana zama kan kujera ,ganin baba laraba tana zarya tana gyaran inda suka zauna takeyi inna akace kai gaskiya kudi sunyi arayuwa kana zaune saidai a gyarama gida amaka girki ,ba ruwanka
Baba laraba tana jinta ta girgiza kai taba murmishi tace kai tsohuwar nan badai neman magana ba
Inna tace ke larai dani kike magana
Baba laraba tayi tace saurin fadi a a inna badake nake ba
Inna jin abinda ta fada sai tasoma tafa hannu tana fadin Muhammed rasulullahi S.A.W ni maryama a kai jama'a dama kema ciwon aljanu gareki bamu saniba saidai kike surutai idan abun yatashi a ni jikar mutum hudu gozoma ta biyar to bari Muhammad ya fito a samu yakaiki asibitin mahaukata ,ko zaki samu lfy acen
wannan abu haka kike zance ke kadai , wannan kawai a abubuwan masu hauka ke dukane bakiyi ko?
Mommy ce tafito daga sashansu ,tace inna lfy kike rafka salati haka ? Inna ta kalli mommy tace ba dole nayi salati ba fadila ashe wannan yarinyar tana da tab'in hankali ban sani yanzu fa ina fitowa naji tana surutai ,kamar wata zararriya na tambayeta tamin wai badani takeba naga dai dagani sai ita a falon ba kowa to daga anjima akaita asibiti adubata ko k'usar kanta daya ta kunce
Inna na wannan zaro maganar sauran yan gidan suka fito kowa najin abinda inna ke fada saidai yayi dariya ya zauna
Su ameera da ameer ma saukowa sukayi jin inna na daga murya
Ameera tace kai inna daga yin sallar bazaki barmu mu hutaba kin wani damemu da surutu waya tabamin ke ne yau agidan nan yaga baccin ran jikar inna ta baffa ikon Allah tana danne dariyar ta
Inna na murmishi tace yauwa yar albarka shiyasa nake sonki ba kadanba wannan yarinyar ku kaita asibiti tasamu tab'in hankali ne
Yar dariya ameera tayi tace to shikenan gobe da wuri zamu kaita nida yaya sai adubata
Inna na murmishi tace yauwa yar albarka nasan dama ke kadaice daki fashimceni nima zan rakaku goben insha Allah
Ameera tace da safe tazumu tafi saidai inzamu sake komawa inna ta ,,da haka dai aka rufe bakin inna tadena cewa baba laraba tasamu hauka
Suna hira anass ya kira fatima dauka tayi tana tashi daga falon tashiga dakinsu
Tace hello sweetheart dina barka da yamma
Lumshe ido anass yayi jin muryar fatima ta daki dodon kunanshi yace lfy lau sweetheart I miss you very very much fa wllh duk nazama maraya , kamar banida gata a duniyar nan inason zuwa wajanki amma ina tsoron inna tarufe da fada , ranar kutafima kinga maganar data ringa yab'amin
Dariya Fatima tayi tace aikuwa yanzu aka gama a ita wai dole sai ankai baba laraba asibiti yasamu ciwon hauka
..murmishi yayi yace hajiya inna mai duniya kenan ai zanje gobe amma saina done kunne na kisan mai tacemin ranar?
Fatima tace a a sweetheart saika fada
Dariya yayi tunowa da maganar yace cemin tayifa wai kaci kan ubanka bak'i kamar tukunyar daddawa
Dariya sosai fatima keyi tace ai jiyama tayiwa yaya muhammed dan yace zaije yayi wanka ,nan tafada mishi abinda tace miki
Aikuwa anass yaringa dariya yace kai inna ta iya wulakanci wllh yanzu dai bari na kyaleki karta shigo tadauke min lodin zagi kishafa min kan iman dina
Fatima tace to ga inna nan zata shigo bey yanzu saita hadamu nidakai , dariya yayi sukayi sallama ta kashe kiran
WASHE GARI
Ameera tafito daga toilet da alama wanka tayi , tana tsane jikinta da towel taji an rungume ta murmishi tayi tace yaya please ka bari na shafa mai mana gidan momsy zanje fa
Kin sakinta yayi saima kara manne mata dayayi yana aika mata da sak'onni
Ameera babu yadda ta iya ta saki jiki tana amsar sakonshi ,ganin zai wuce gona da iri ta rike hannun shi tace haba mana yaya kai baka gajiyane wai please , shiryawa zanyi fa
Sakinta yayi yana dariya yace to shikenan bazanyi komai ba nida matata
Murmishi tayi tacigaba da abinda takeyi karar wayar ta ya dakatar da ita
Ganin mai kiran tace to anty jamila kuma da ranar nan dako tayi tana fadin hello anty jamila
Daga cen bangaren bilal yace ba ita bace nine batada lfy munzo asibiti nayi ta kiran ameer baya dauka please kice yazo ,da sauri ameera tace to gamunan zuwa
Kallon ta ameer yayi yace lfy , Ameera tace anty jamila ba lfy suna hospital din ka muje sauri
Mikewa ameer yayi yana daukar wayoyinsa nan yaga kiran bilal yafi sau ashirin baijiba saboda wayar a silent take da sauri yahada kayan shi suka fita
Ameera hijab din ta a hannu yake batama sakaba saboda gaggawa, k'asa suka sauko
Mommy na zaune a falo tagansu duk suna saurin fice ta , tace son daughter lfy kuke sauri haka
Ameera na saka hijab tace mommy anty jamila ba lfy suna hospital zamuje cen
Mommy tace haihuwar ce to Allah yasauketa lfy sai munzo ,to ameera kawai tace suna fita
Mota suka shiga da da mugun gudu ameer yafita a gidan ko a titin ma haka yaringa gudu Allah ne kawai yakaisu asibitin da sauri ameera tafito shima ameer yafito suka nufi ciki a tare
Bilal suka gani shida ammi suna tsaye
Da sauri ameera ta karaso tace ammi ina anty jamila
Ammi tace tana ciki sunce bazasu iyaba sai ameer yazo
Ameer wucesu yayi yashiga office dinsa yahada kayan aiki yatafi dakin da aka kai jamila ,bai jimaba yafito ,wajanshi sukayi suna tambayar shi
Kallon su yayi yace zata haihu da kanta to bani zan karbi haihuwar ba kasan inba C.S bane bana shiga karban haihuwa ni ba mace bane yanzu zan kira doctor aisha zatazo ta karfi haihuwar saboda naga da sauran lokaci kan haihuwar tazo ,
Ammi tace to ba matsala kirata
Kiranta ameer yayi tana dagawa yace kakata please kizo nan matar abokina na nak'uda zata haihu