Showing 120001 words to 123000 words out of 163788 words
Chapter 41 - KYAUTAR ALLAH COMPLETE by Amina umar faruk.txt
kinkai sa bango yagaji da hakuri dake kai! inbashi ba ma dayake mutum mai tsananin hakuri wane zaya iya zama dake da wannan mugun kazamin halin naki eyeee?...
Ace wai da'auren ki kike bin wani namiji anya Murjanatu kinsan bala'in dakika sakanki Cikin kuwa?...ido tazaro kin tsanani tsoro domin bata taba zaton Baban ta yasan abinda take aikata wa, wani mugun kallo yasake watsa mata, yace kina tsammani bansa mugun halin dakike aikata wa agidan auren ki bane?...wanda tabbas yaji labari ne shiyasa yasake ki.
Cikin kukan munafurci tace yanzu saboda Allah kazafin daza'a...Cikin tsawa yace keeee! rufe mun baki munafukar banza munafukar wofi, ke! aigara ma daya sakeki karkije ki kwaso mugun cuta kisama shi haka kawai, to barikiji yanzu ni bazan dauki wannan shashanci ba agidana, don haka zaman idda zakiyi kuma wlhy narantse KO" zaure ki kataka sai na yankaki, idon tazaro cike da azababben tsoro.
Wani mugun murmushi yayi yace kina ganin kamar bazan iyaba KO?...to barikiji a yadda nakeji bakin cikin abinda kika aikata, billahillazi kika fita daga gidan nan ba tareda kin gama idda ba tabbas sai nayi maki yankan rago, ki mutu kowa yahuta Da mugun halin ki.
Sannan ya kalli Dije wacce tayi tamkar butun butumi cikin tsawa wanda yadawo da'ita hayyacin ta, yace ga Murjanatu nan zaman idda zatayi duk ranan datasa kafarta tafita gidan nan narantse da mahaliccina sai nayi maki mummunan hukuncin daza kisha mamaki idan kuma kuna ganin bazan iyaba to bismilla! sannan yafita rai bace.
Wani irin kuka *Jana* tasaki me cike da tsantsan tsoro jin abinda Baban ta yafadi, tabbas zaya'iya abinda yafada domin ta hango hakan akwayar idon sa, cikin masifa Dije tace to kukan uban me kike tunda kin kashe auren, ke adole kin samu gidan daula shine harda kaurace mana saboda kina shashasha,
in banda ma Allah yasa "yaron kirkine dan gidan mutunci kusan koda yaushe yana yomana sako da shikenan babu abinda yadameki damu, hmmm kindai ji haushi wlhy kin kumayi hasaran yaron kirki to ai ga gidan daki ke gudunan yanzu kindawo banza kawai, wawuya sannan tashiga daki tabarta nan Cikin bakin ciki da takaicin rasa *BB,*
Nima dai nace *BB* yai mata nisa lol.
*******
Bayan su *Deeya* sun gama cin abinci saita gyara gurin sannan ta kwashe kayan takai kitchen ajiye ta koma falo, kishingid'e ta iske *Habeeb* akan kushin 3 siter lallausan murmushi ya sakar mata me cike da zallar kaunarta, ita ma tamayar masa sannan ya mika mata hannun alamar tazo garesa ba musu takama tareda zama kusa dashi,
Tadora hannun ta daya akan kirjinsa cike da shagwaba tace Hmm na to matsamun nima na kwanta kaji?.., cike da zolaya yace tab! salon kimatseni gaki gudan katuwa dake ido tazaro sai kuma ta turo bai, cike da shagwaba takai masa duka kad'an akirji tareda fadin kai! Hmm na nice katuwa?...
Yace "eh mana dubeki fa gudan katuwa har madai nan ya kareshe fadi tareda shafo hips dinta yana kashe mata ido daya, fadawa jikin sa tayi tareda cigaba da dukan sa sai kuma takin kukan shagwa ba, tace gaskiya niba katuwa bace to aikai ma katone kalli fa kirjinka Da hannun kamar na samuda wa tafadi tareda kallon damtsen shi dayake murde kamar dan dambe, kasan cewar jallabiyyar dayasa me gajeren hannun ce.
Dariya ce takwace masa har yana rike ciki sai dayayi me isar shi, sannan yace Kai! *Leemah* ta yanzu kirjina da hannun nane kamar na samuda wa?... kwantawa tayi akafadar shi tareda turo baki tace "eh nima aice mun kayi katuwa kuma kasan niba katuwa bace,
Murmushi yayi tareda rungume ta yace wasa nake maki aike ba katuwa bace, *Leemah* ta yar shilace irin yadda nakeson matata ta kasance dama kuma aike bame irin jikin nan bane kato, dasauri tace da gaske Hmm na?... yace Allah my Honey *Leemah,* cike da farin ciki tace yeee naji dadi ni ba katuwa ba ce dama wlhy banason nayi katuwa.
Yace uhumm shine kikace ni kato ne har ina kama da samudawa KO?.. dariya tayi, yace au! dariya maki ke mun ko?.. to ba ruwa na dake yafadi yana kaudakai gefe tareda turo baki like small boy, dariya tasake yi sannan tasa hannuta dubiyu tajuyo da fuskar tace soweey Hmm na aida wasa nake baka kamada samuda wa, saida Allah Hmm na kirjinka da hannun ka kaman na yan boxer jifa tace tareda nunawa,
Dariya yayi tareda kallon hannun nashi dayake amurde kamar na yandaben, sannan yace *Leemah* ta kenan naji amma faban hakuri ba dasauri tace kai! Hmm na, yace "eh zanyi hakuri amma sai kinyi wani abin, dariya tayi domin tagane abinda yake nufi tace to rufe idonka yace na rufe.
Bakin su tahade tafara tsotsa aikam da sauri yasake rungume ta gam tareda fara mayar mata da martani azafafe, sosai yake tsotsar bakinta kamar yasamu sweet har yana shirin sakin layi hakan ne yasata saurin cire bakinta a nashi tana dariya, idon shi lumshe yake murmushi Cikin kasalalliyar murya yace *Leemah* ta fadamun yaushe zaku gama jarabawa ne?...
tace next week yace shikenan sai mutafi honeymoon KO?.. Dasauri tace honeymoon Hmm na?..yace "eh ko bakison muje ne?...cike da farin ciki tace Ina so mana, yace yauwa tofadi kasar da kike so muje saida tagyara kwanciyar ta ajikinsa sannan tace India yace uhum sai Ina kuma?.tace China da saudia yace da'ina kuma?..Dasauri tace kai!Hmm har kasa nawa zamu?...
Yace ko kasa nawa kika lissafo zamuje, tace to Hmm na nidai kasa uku ya'isa yace to shine *Leemah* ta yadda duk kike so haka za'a yi, haka nan suka cigaba firarsu har karfe 5:30 tayi *Deeya* tace Hmm na bari naje na shirya maka dinner kaji?.. murmushi yayi me cike da zallar kaunar ta, sannan yadagata tareda cewa tashi muje nata ya ki.
Dasauri tace "a ah Hmm na ka zauna ka huta, yace naki ai da'ina nan tare muke yi shine yau zakice baki son nataya ki?..tace ayya Hmm na ba wai banason ka tayana ni bane, yace to mene?..tace kaga yau fa kadawo kuma nasan har yanzu akwai sauran gajiya atareda kai shiyasa nake son ka zauna ka huta nikam naje nahada maka special dinner, KO takareshe fadi da yin dariya tareda Shafa sajensa tana me kashe masa ido daya.
Shima dariyar yayi yace *Leemah* ta kenan to aikinriga kin gusar da gajiyar tun dazu, tace to nidaika kara hutawa su yace "a ah nidai muje nataya ki nashiga tace to naji amma idan mukaje zama zakayi kana kallo na KO?.., gaskiya nidai idan ba haka ba.... saita fara buga kafa cike da shagwaba dariya yayi tareda dagata cak yaba akafada yana fadin to muje *Leemah* ta na yadda.
Bayan sun shiga kitchen yasauke ta saita jawo wani kujera tace to zauna fuskarsa dauke da murmushi, ya zauna sai tadora hannu wata duka biyu akafadar ta shikuma ya rungumo kugunta hakan yasa suka kalli juna sukai lallausan murmushi sannan tace Hmm na, bayan wanda zan girka maka to ina so kuma ka fadi kaima wanda ka ke son nagirka maka?...
cike da kaunar ta yace *Leemah* ta jagwalgwalon nan nakeso kiyi mun, dariya sukayi gbdy saboda tuna wa da abinda yafaru can baya, tace to Hmm na angama.
Sannan tajeta kunnan gas tadora tukunya tazuba ruwa tarufe sannan ta dauko kayanbiya tawanke tazuba a blander, duk yana kallon ta sai murmushi yake yayinda take matukar birgesa ganin yadda take aikin ta Cikin nutsuwa, sannan tadako albasa da wuka wanda *Habeeb* nagani saida yaji faduwar gaba aikam cikin tsautsayi tajeyanka albasar tayanke babbar yatsarta, wani irin zafine yaratsata wanda yasata sakin kara wanda yasa *Habeeb* mikewa Zumbur.
Jefar da wukar da albasar tayi tareda sakin kukan shagwaba tana fadin wayyo Hmm na zafi, Cikin tashin hankali ya'isa gurinta yakama hannun yarike yana fadin Sorry *Leemah* ta kamar zatayi kuka, ya rungumota tareda tura hannun dake zubar jini abakinsa yana tsotse jinin yana bubbuga bayanta alamar lallshi, ahankali tayi shuru tareda kwantar da kanta akafadar sa tana sauke ajiyar zuciya.
Sai daya tabbatar tayi shuru sannan yacire hannun daga bakin sa ya kalla tareda hurawa sannan yace sannu kinji yar aljanna, kaita gyada dukawa yayi yadauko albasar tareda wukar daya ballawa harara harda tsaki sannan ya wurgata kan table yace stupid knife shine kika wani yanke my *Leemah* ko?...kuta yayi, har saida *Deeya* tayi dariya ganin yadda yakeyi kamar da mutun yake shima dariyar yayi yana jin kaunar ta nasake ninku aransa sannan yakashe gas din, sai kuma yadauke cak!. ta dasauri tace Hmm na girkifa?...
yace tunda *Leemah* ta tayanke aisaida kuma abarshi har zata sakeyin magana, yahade bakinsu ahaka suka fita kitchen din suka nufi daki.
Har week din nan yakare babu abin da *Deeya* da *Habeeb* suke zubawa sai soyayya kuma tun ranan data yanke *Habeeb,* yace ba zata sake shiga kitchen saita warke don haka part din Hajiya dana lnna suke zuwa ci abinci, har hannun yawarke amma da lnna tayi magana sai yace ayya lnna mu ai hannun bai gama warke wa duka bafa,
tace humm anya *Habeebu* basokake kabata *KYAUTA* da ragganciba?..ko dayake aidama ragguwace, dasauri yace "a ah lnna ai *Leemah* ta ba ragguwa bace don dai tayanke ne kawai, tace lallai yanzu saboda dan wannan yankewar shine ba zata shiga kitchen tayi girkin ba?..takareshe fadi tareda hararan *Deeya* dake ta turo baki.
har *Habeeb* zaya sake magana sai lnna tayi saurin cewa to yayi Allah yabata lafiya saida safe, kasan cewar ranan anan sukaci abin dare yakama hannunta suka fita yayinda Baffa da *Hafeez* suka biyan su da dariya,
Suna fita yace kyalesu *Leemah* ta karkiyi girki sai hannun ki yawarke sumul kinji?..cike da shagwaba tace to Hmm na l love u so much, yace love u more and more my *Leemah* sannan yadauketa suka nufi part dinsu, ranan dazaya tafi kamar kar su rabu.
*_Bayan kwana goma_*
******
Ayau Monday kuma yaune jirgin su *Deeya* zaya tashi zuwa China kasan cewar tuni ta gama jarabawa,
misalin karfe 10: 50 am suka fito cikin shirin su kasan cewar jirgin 11:00am zasubi *Harees* da *Feeya* da *Hafeez* nezasu rakasu,
Wata babba jif suka shiga su duka sai motoci biyu escorts keciki kowani yana makale da matar sa, yayinda akabar *Hafeez* datuki har suka isa filin jirgin, suna isa anakiran fasinja don haka basu dade ba jirginsu yatashi yayinda su *Harees* suka juyo gida.
*******
Su *Deeya* sun sauka China lafiya a wani hadadd'an babban hotel suka yada zango, Bayan sunyi wanka su huta su ci abinci sannan suka fita shakatawa, saida sukayi sati daya sannan suka tafi India suka sauka a wai babban hotel dake Mumbai,
Nan ma sati daya sukayi suna shakata warsu sannan suka nufi saudiya, anan kam sati biyu sukayi suna bautar ubangiji sannan suka nufo gida Nigeria.
*_Yau Jumma'a_*
Gaba daya family Alh Hashim Soro sun hadu Abban falon sa kowa ka kalli fuskar sa dauke tada farin ciki, kasan cewar yau *Deeya* da *Habeeb* zasu dawo, misalin karfe 12:00pm su *Harees* suka isa filin jirgin dai-dai lokacin da jirginsu
*Deeyar*
yasauka,
Sannun ahankali fasinja suka fara saukowa can saiga *Deeya* da *Habeeb* sunfito hannunsu sarke da juna fuskarsu dauke da farinciki, *Deeya* tana sanye da bakar abaya me shegen kyau saitayi rolling da gyalen abayar shikuma *Habeeb* yana sanye dawani farin yadi, sunyi wani irin kyau da kiba na ban mamaki, musamman *Deeya* da kirjinta da hips dinta sukayi kamar zayasu fashe gafatar jikinta sai sheki yake,
Dasauri suka rungume juna itada *Feeya* cike da murna ganin juna suma su *Harees* suka rungume juna da *Habeeb,* yayinda *Hafeez* yamatsa kusada *Deeya* cikin zolaya yace wlcm kyautar bera aikam tuni takwabe fuska zatayi kuka,
Dariya yayi tareda ma tsawa gurin *Habeeb* yanai masa barka da dawowa, sannan suka shiga mota suka nufi gida, *Feeya* sai fadin take kai! my sweet *Deeya* kinkara kyau sosai wlhy Allah yasa kin zo mana da tsarabar dan India,
Murmushi tayi tace kai my sweet *Feeya* kema fakin kara kyau ya my unborn child?. tace yana lafiya yayi missed din ki sosai, tace nima nayi missed nashi sosai a haka har sukai sa gida inda akayi masu yar bane kyau bayan sun ci sun sha sannan aka cigaba da fira me cike da kaunar juna, misalin karfe 1:30pm Abba yace Baffa yayi addu'a saboda lokacin salla yakusa bayan angama addu'ar sai kowa yamike,
zayafita saidai itakam *Deeya* tana mikewa wani irin jiri yakwashe ta tafi luuuuu! zata fadi,
Cikin zafin nama *Habeeb* yatare ta saidai kuma wani abin mamaki shine babu numfashi babu dalilinsa a tareda ita, hakane yasa *Habeeb* zaro ido cike da azababben tsoro tareda tsananin tashin hankali yace...
Muje zuwa
A
*_KYAUTAR ALLAH CE_* (Labarin Sadeeya)
Tareda
โ๐พ
๐นMeenat๐น
[11/9, 10:08 PM] My Ameena: ๐๐๐๐
๐๐๐
๐๐
๐
_*KYAUTAR ALLAH CE*_
_(Labarin Sadeeya)_
๐
๐๐
๐๐๐
๐๐๐๐
6โฃ7โฃ
WRITTEN
By
๐ *AMEENA UMAR FARUQ*๐
OR
๐ *MEENAT* ๐
SADAUKARWA
*GA SADEEYA SADEEQ UMMU (Haidar)*
___________________
ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_
___________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~
โ๐ฝ
_*Bismillahirrahamanirraheem*_
_NOT EDITS_
Karki sake kirana adonki wai! nizaki wulakan ta *Jana???..* ni ado za kikai asibiti kibari har tsawan wata daya har da yan kwanaki saboda wasu yan kudi kalilan, "eh mana yan kudi kalilan to ina tsiya ina naira dubu arban'in kacal abinda nasankin kinfi karfinsu, to kina matsayin matar "seneto me dubu arba'in agurin eye?....
Amma dayake ke muguwar marowaciya ce sai kika ki kai cikon kudin balle ayimun aikin na huta da azaba, sai kika barni asibiti a walakan ce, sai bakar wahala nake sha saboda tsabar mugun ta irin taki, shine yanzu zakizo kice waini nakine?..., saboda kin raina mun hankali KO?.....
Ai Inda ni naki ne abazaki barni inashan bakar wahala ba, Dasauri *Jana* tace don Allah adona ka saurare ni wlhy matsala...
tsawa yadoka mata tareda cewa dalla mlm rufemun baki sauraren me zanyi maki?..., aini kin ban mamaki wlhy *Jana* ban taba zaton zakiyi mun haka ba, kuma wannan ciwon ta dalilin zuwa gurinki nasa mesa amma saboda tsabar butulci irin na dan'adam shine zakiyi mun haka, har zatayi magana yakatse ta dafadi babu fa abinda zaki fadamun na yarda kinji,
kawai nadai gane kin mai dani matsiyaci ne aibari nima kwannan zanyi kudi wlhy kota halin k'ak'a ne kinji yakareshe fadi raiba ce tareda watsa mata harara.
Kai! atakaice dai duk yanda *Jana* taso ado ya saurare ta yakiya daga karshema cewa yayi tafita tabashi guri, bayason ganin ta ba kuma zaya saurareta ba, dole badan ranta yasoba tafita domin tagano mugun bacin rai atareda shi wanda tasan ita Ce tabata masa rai gakuma Wani mugun tsoron shi dataji yaka mata, don haka tabar shi ya huce amma dole ne ta dawo domin suyi maganar auren kisan wuta,
don gaskiya dole ne takoma gidan *"BB* kota halin k'ak'a, beyuwa ace tabar gidan *BB* batareda ta mallaki komai ba, tafiya tai tayi akasa saboda batada kudin mashi har takai gida don haka tayi mugun gajiya kafin ta'isa gidan, domin rabon datayi tafiya dakafa harta manta Rana.
Koda ta shiga gida Kai tsaye dakin ta tanufa ba tareda tace wa kowa komai ba, saidai KO gama cire hijab batayi ba taji muryar wani yaro yana cewa wai ana sallama da *Jana,* cike da mamaki tafito tana kallon yaro tace kai wanene yake kiran *Jana* yace wani mutumi ne yana nan kofar gida tace amota yake KO amshin KO da kafa yake?...yaro yace da mota yake, shuru tayi na dan wani lokaci tana tunani to wanene yake kiranta?.. sai kuma da sauri tace Da yaron kai jekace tana zuwa yace to tareda fita.
Hijab din ta matar tareda sa takalmi zata fita sai ga Baban ta yafito daga daki yana watsa mata wani mugun kallo, yace danace kiyi maza ki dawo shine ban'isa ba sai yanzu kikaga damar dawowa KO?.. sannan kuma za kifita ba tareda neman izini ba saboda a dole ke ga bawazawa ra me ikon kanta KO?.. to "shikuma wanene yake yaaiko kiranki?...
Cike da bacin rai tace to Baba banida kudin mashi shiyasa nadawo kasa, shikuma wanda akace yana sallama Dani bansan "shiba dama dai zanje nagani ko wanene, tsaki yayi mtsss rai bace yace kin daije yawanki na banza dawofi idan ba haka ba yaza'ayi dari biyun dana bakin bai isheki zuwa da dawowa ba?.. wlhy Murjanatu ki kiyayeni idan ba hakaba zanyi mummunan sabamaki kinji KO?..
kuma ina sake tabbatar maki bazan sake daukar wannan shashanci banzan ba yauwa, sai kifita kiga wanda yake kiran ki wucewa tayi tana gunguni yayinda yabi bayanta da harara, sannan ya koma daki zuciyarsa cike da bakin cikin mugun hali irin nata.
Koda tafita tsaye ta iske mutumin yajuwa kofar gidan baya yana waya, don haka bataga fuskar shi ba tsaya wa itama tayi tana kallon bayan shi aran ta kuma tanajin kamar tasanshi,
Bayan yagama amsa wayar yajuyo suka hada ido aikam take *Jana* tazaro idon tareda bude baki saka makon ganin wani tsohon saurayin ta, wanda yana daya daga Cikin samarin dasukai tayin lalata da'ita a can baya, fuskar sa dauke da murmushin yaudara ya matso kusada ita har yana kokarin rungume ta,
Dasauri tadan matsa tareda cewa "a ah Alh Barau a kofar gidan mun fa muke, dasauri ya matsa tareda shafa keya yace "eh kuma fa haka ne to yakike?... tace dai-dai amma ya'aikai kasan aure na yamutu?...yace hmm *Jana* kenan nida kullum Cikin bin ciken ki nake, yanzu yaza'ayi ne inason mu cigaba da harkan nan fa yakike ganin za'ayi ne?...
ahankali tajuya ta kalli zauren gidan su taga babu alamar fitowar wani don haka tayi kasa da murya, tace nima zanso haka saidai yanzu Babana yasa mun ido sosai sannan kuma banida waya, yace karki damu Ina zuwa gurin motar sa yaje yabude yadauko wata sabuwar waya Nokia akwali yakawo mata, yace ga waya yanzu na siyota harda sabon layi duk yana ciki kuma anyi rejitster layin,