Showing 129001 words to 132000 words out of 163788 words
Chapter 44 - KYAUTAR ALLAH COMPLETE by Amina umar faruk.txt
yahau kadan,
hakan yanuna kina danyi tunani sannan kuma kamar kina tsallaken shan maganin ki KO?...
kallon *Habeeb* tayi wanda shidin ma ita yake kallo, murmushi yayi yace hey Queen of beauty answer my question don't look at u husband,
baki ta turo ba tareda tace komai ba dariya yayi cike da zolaya yace allura biyar zanyi maki yanzu, saboda tsallaken da kikeyi na shan magani.
Wani irin runguma ta yiwa *Habeeb* tareda sakin kukan shagwaba tace wayyo sweet Hmm na banaso, shikam *Habeeb* ido yazaro baki bude yana kallon *Harees* sai kuma hade fuska yace haba dai allura goma alokaci daya sai kace abin hauka, dariya *Harees* yayi yace to ni wasa nake mijin ragguwa daga cewa za'ayi mata allura goma duk kun wani rikice mun dakai da'ita,
Hararan shi yayi yace kai ne dai mijin ragguwa gata can yanzu zakaje iske ta, dariya yayi yace naji amma dai dole daina yimata allura daya yanzu yafadi yana bude dan box dinsa dakyar ta tsaya akayi mata alluran, sannan yasake rubuta mata wasu magungunan sannan yafita yabar *Habeeb* da lallashi.
*Harees* bai dade dafita ba bacci ya kwashe ta daukar ta *Habeeb* yayi cak!, yakai dakinsa yakwantar sannan yafito yanufi part din su Hajiyarmu.
Washegari *Habeeb* yakoma Abuja gurin aiki bayan ya tabbatar *Deeya* taji dama.
*_Bayan sati biyu_*
**********
Aban garen Ado kam sosai yake shirin daukar fansa akan *"Habeeb* kamar yanda yace, lallai kam yana shiri matuka wanda ni kaina bansan irin ba, yayimda shi da *Jana* kam sun zama tamkar mata da miji sosai suke aikata masha'arsu.
Yayinda agefe daya kuma ta tuni *Jana* tabaje kolin harka da maza bayan Alh Barau dashi Adon sosai take harka da duk wani namiji da, yatare ta idan zaya bata kudi to magana takare,
Haka zalika duk yanda Babanta yaso killace ta agida tadaina yawon tazubar din datake abin yaci tura, don haka yazuba mata ido amma yace duk uban dayayi mata tsaye dole tafito da miji cikin satin nan tayi aure idan kuma ba haka ba ya aura mata duk wanda yaga dama,
Hakan ne yasa hankalin ta yai mugun tashi a ranan bata iya bacin kirji ba.
***
Washe gari yakama jumma'a kasan cewar duk idan Baban *Jana* yaje masallacin Jumma'a sai bayan la'asar yake dawowa gida,
shiyasa Bayan yatafi sallar Jumma'a sai *Jana* tayi suluf tafita daga gida tanufi gidan ado.
Saida suka gama tsiyar su sannan tace adona yaka mata muyi auren hakanan kaga Baba yace" idan ban fitarda miji acikin satin nan ba zaya aura mani wanda yaga dama, wani killed smile yayi tareda shafo fuskarta yace karki damu yaune shirina nakarshe, don haka kije gida cikin satin nan zan turo neman auren ki saidai banida sadakin dazan biya,
cike da farin ciki tace karka damu zan baka sai ka biya yace Ok" sai ki yanke dai-dai yanda zaki bani, tace to ga dubu biyar zanciko maka dubu biyar ai goma yayi ko?.. karba yayi yace "eh aibaki fi hakan ba to haka zakibar nibako sisi?..,dubu daya tasake ciro wata bashi tace yau banida kudi sosai sannan ta maida kayan jikinta tayi masa sallama tafita yayinda yabi bayan tada wani mugun murmushi, sannan yadauki wayar sa yafara daddanwa.
*_Yau tun_*
misalin karfe 12:00pm su *Habeeb* suka iso Bauchi bayan sun dawo sallar Jumma'a sun ci abinci sai suka tafi, soro da gudun fulani ziyara kamar yanda suka saba Bayan tafiyar su ne sai *Deeya* tanufi part din.
Misalin karfe 5:00pm
*Deeya* ce ita kadai kwance akan kushin me zaman mutun uku dake falon Hajiyarmu,
sai shafan cikin ta take tana yamutsa fuska domin tunda ta tashi daga bacci take jin wani irin yinwa takeji sosai gashi gashi koda tashi yanzu taji batasan cin girkin da Hajiya tayi har dama na lnnan ta duk bata ra'ayin cin.
Ahankali tashi tayi daga kwancen tadauki wayar ta *Habeeb* zata kira sai gakiran shi yashigo, dasauri tadauka tabude kara kamar zatayi kuka tace sweet Hmm na kun kusa karasowa?.., dasauri yace "eh honey *Leemah* ta ga munan shigowa sorry kinji?.tace to sannan ya kashe wayar, dai-dai lokacin da Hajiya take saukowa idon tana kan *Deeya.*
Zama
Hajiya tayi kusada ita tadafa kafadar ta cike da tausaya wa tace hali dubu na yanzu me kikenin ci?.,
cike da shagwaba tace shawarma tace to bari nasa direba yaje yasiyo maki ko?...tace a ah Hajiya ta kibari gasu Hmm na nan zuwa zamuje tare musiyo, tace to shikenan basu rufe baki ba su Abba suka shigo bakin su daukeda sallama *Habeeb* na biye dashi abaya amsawa sukayi tareda tashi suna yi masu sannu da dawowa, *Habeeb* kam sai kallo *Deeya* yake yana sakar mata lallausan Murmushi itama cike da kunya take matar masa damartani, cike da kunyi ta duka tana gaida Abba ya amsa yana nufar dakin sa yayinda Hajiya tabi bayan sa.
Dasauri suka rungume juna tareda sauke ajiyar zuciya, sai kuma suka saki dariya me cike da kaunar juna tace sweet Hmm na sannun da dawowa yace yauwa my honey *Leemah* yakike?..tace lafiya yace good haka nake soji yanzu me kike jin ci?..ya kareshe fadi tareda shafa cikinta, saida tayi fari da ido sannan tace ummm shawarma kaza gasassa da tsire with ice cream dariya yayi yace duk zaki ci?..tace "eh Allah duk inajin marmarin su yace kin samu *Leemah* ta muje.
Suna fita Saminu yanufo su cikin girmama wa yace Sir za'a fita ne?.yace "eh amma bana bukatar escorting dinku so bani key veezer, yace Ok" Sir tareda ciro key din cikin keys dasuke hannunsa yamika masa tareda fadin a dawo lafiya yace Allah yasa, saida yabude ma *Deeya* kofa tashiga ya rufe sannan yazaga yashi ma yashiga ya tayar megadi yabude suka fita.
Duk abinda *Deeya* tace zataci saida sukaje *Habeeb* yasiya mata, ahankali yake tuki ita kuma tana cin kaza shawarma kuwa da tsire tuni taci wanda zata iyaci tamayarda sauran gefe, yayinda *Habeeb* sai kallon ta yake cike daso da kauna dan bakinta gwanin sha'awar kallo idan tana cin abinci.
Idon tane yasauka akan megasa masara agefen titi aika dasauri tace Hmm na zanci masara gasassa gata can, dariya ce takufce masa yana kallon ta ganin ta'ajiye kazar tadauki ice cream tana sha yanzu kuma tace masa zataci! Oh! Oh! Allah sarki ciki me kwashe-kwashe cike da tsokana yace Ohhhh! Allah ka taimaka ni kar cikin *Leemah* ta yau yafashe domin dai lodin nan yayi over, cike da shagwaba tace "a ah,
dariya yayi yace yes wasa nake babu abinda zaya samu cikin *Leemah* ta Insha'allah dai-dai lokacin da yai fakin gefen titi, yace bari nasiya maki dariya tayi tareda fadin thanks Hmm na Love you yace love u two dear sannan yafita motar.
Hannun sadauke da ledar masaran yabude mota yashiga dai-dai lokacin da wayar sa take kara, mika mata masaran yayi takarba shikuma yadauki wayan, sunan *Harees* ya gani
Dauka yayi tareda fadin ya akayi ne dan'uwa?..
Cike da farin ciki yace ah! kai haba yanzu nan?..to Alhamdulillahi tunda an sauka lafiya Allah yaraya
akan sunna,
gamunan zuwa yanzu insha'allahu sannan ya kashe wayar fuskar sa dauke da matsananci farin ciki.
ya kalli *Deeya* wacce itama shi take kallo fuskar ta dauke da tambaya, tallabo fuskar ta yayi yahada da tashi yagoga hancin sa anata sai kuma yai kissing din lips dinta sannan yace my honey *Leemah* sweet *Feeyar* ki ta haih....wani irin ihun murna tasaki tareda rungume shi.,
Cike da farin ciki suka isa gida direct part
din su *Feeya* suka nufa wanda tuni *Deeya* tariga *Habeeb* yingaba, tabarshi da kwasar tarkance ciye-ciyen ta murmushi yayi tareda girgiza Kai, yana kokarin daukar tarkace sai wayar sa tayi kara.
Ahankali yadago tareda duba wa number ce ba suna be damu ba domin yasa ba ganin lambobi kala-kala,
saidai kuma jikinsa yabashi cewa wannan lanbar tana dauke da wani muhinmi abu, don haka da sauriya amsa kiran saidai me amsa wayar ke dawuya yafara hada gumi Cikin matsanancin tashin hankali yace....
*_Barkam mu da Jumma'a sannan Ina mana tafatan yin salla lafiya Allah yasa ameen._*
Muje zuwa
A
*_KYAUTAR ALLAH CE_* (Labarin Sadeeya)
Tareda
โ๐พ
๐นMeenart๐น
[11/9, 10:09 PM] My Ameena: ๐๐๐๐
๐๐๐
๐๐
๐
_*KYAUTAR ALLAH CE*_
_(Labarin Sadeeya)_
๐
๐๐
๐๐๐
๐๐๐๐
7โฃ1โฃ
WRITTEN
By
๐ *AMEENA UMAR FARUQ*๐
OR
๐ *MEENAT* ๐
SADAUKARWA
*GA SADEEYA SADEEQ UMMU (Haidar)*
___________________
ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_
___________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~
โ๐ฝ
_*Bismillahirrahamanirraheem*_
_NOT EDITS_
_What?...._ Kai! wai me kake fadi ne haka Kai! tsaya wanene ma kai tukun eye?...kittttttt! aka kashe wayar batareda ambashi amsa ba, cikin matsanancin tashin hankali yakiran lamba wai busy can kuma sai kaji, kiri-rin sako yashigo.
Cikin rawar jiki yabude abinda yagani ne yasake tayar masa da hankali, ahankali yafurta innalillahi'wa'inna'ilaihirraju'un,allahuma'ajirni'fimaseebateehi'wa'akiflini'fihairinmiha, sai kuma yasake kurama sakon ido afili yasake karantawa kamar haka.
*_Hhhhhhhhh! Senate Habeeb kenan kana nufin abinda kayi mun kaci banza kenan ko?... humm! to wlhy baka isaba saina dauki fansa, kuma kasani abinda nafadi maka ba karya ba ne eheee! na kuma sake fada maka matarka Jana fasikace koda yake kasan haka tunda gashi har kasake "ta, saidai nasan ba kasan cewa"Junior ba d'anka bane ko?...hhhhhh! to kasani shidin bad'an kaba ne idan kuma kana ganin karyane to kayi bincike zaka gane cewa shidin bajinin ka bane hhhhhhhhhh!._*
Sai kuma yaisauri ya kiran lambar saidai wai akashe take sosai yake try amma amsar dayace wato akashe wayar yake, hakan ne yasashi saurin kwaso tarkacen ciye-ciyan *Deeya* tareda kiran wani yaron dakeyi masu *Harees* wanki yace yakai wa *"Deeya* domin yasan zata bukata, yaron yace to tareda karba yanufi cikin gidan.
Sannan yashiga tada motar yafita daga haraban gidan dasauri yashiga nasu da sauri yafito daga motar, yanufi part din Hajiyarmu cikin wani irin takun kasaita me cike da tashin hankali yashiga falon kasa, saidai bako dan haka da sassarfa ya ke hawa benen.
zaune ya'iske su Lili suna kallon cartoon ganin shigowar shice tasasu tashi dagudu suka nufo shi suka rungume shi tareda fadin oyoyo Daddy sannu da dawowa, yace yauwa sannun ku yafadi tareda zama yakamo hannun wasu, kallon Lili yafara yi yanaji wani irin kaunar ta acikin jininsa irin wanda uba yakewa 'yarsa, kuma tun ranan da tazo duniya yakejin wannan kaunar kuma kullun jiyake kaunar na karuwa.
Sai kuma ahankali ya juya yaiwa Junior kuri da ido tsawon wani lokaci yana kallon shi tamkar be taba ganin sa ba, saidai kamar koda yaushe idan ya kalle shi bejin kaunar shi sosai kamar yanda yakejin na Lilin ko yanzu dinma hakanen beji wani kaunar shi ba, saidai ma wani irin fargaba dayaji wanda yahaifar masa da matsanancin bugawar zuciya, musamman akan abinda mutunin nan yace" aransa yake fadin to wai me yasa banaji kaunar Junior araina ne kamar yanda nakeji na Lili?...
wato hakan yana nufi da gaske shidin ba 'Dana bane kenan ko?..ido yarintse tareda furta yah! elahee! _Show me the true_ sai kuma yabude idan dasauri aikam har idan sunyi jajir, yace ina "Hajiyar mu take?...Junior yace tana part din "Daddy me allura taje ganin "Aunty *Feeya* tasamu sabon baby, shine tace" mubari tadawo sai muje KO?...
Lilin Dady tace "eh Dady Ina Aunty *"Deeya?...* na?.. "Ajiyan mu tace" kun tafi anguwa Daddy me kachiyo muna?...
Wani irin Murmushi yayi me cike da karfin hali yace l'm sorry my Lili bansiyo maku komai ba amma yanzu kusa takalmi muje nasiya maku abinda kuke so, idan muka dawo sai mushiga part din su "Dady me allura sai muga baby da Aunty *"Feeya* tasamu KO?...cike da farin ciki suka ce eyeeeee, dasauri sukasa takalman su yarike masu hannu suka fita.
Suna fita yabude masu Bayan mota Junior yashiga Lili tace ita kusada Dady zata zauna, ba tareda *Habeeb* yace komai ba yabude mata gaba tashiga yarufe,
Sannan yazagaya dasaurin zaya shiga sai wayar sa tayi kara yana dubawa sai yaga, *Harees* ne dasauri yadaga tareda bude volume din kafin duk *Habeeb* din yai magana sai *Harees* yace Dan'uwa yadai?... ga "Queen of beauty tashigo amma kai banganka ba lafiya?... yace humm! kaidai Dan'uwa bari wlhy akwai matsala babba yanzu dai ka iskeni asibitin ka, dasauri yace lafiya?...yace kadai zo pls karka fadawa kowa kaji?...yace Ok" babu damu wa gani nan zuwa Insha'allah sannan suka kashe wayar alokaci daya,
Saiga wani kiran yashigo wayar *Habeeb* dasauri yadaga dariya aka kyalkyace da'ita sai kuma akace, kai! *BB* karka yi tunanin ko daukar fansar danace zanyi akan ka shine nafara tun yanzu "a ah bashi bane saidai kar ka manta zanyi shi nan ba da dadewa ba, daga karshe kasake sani "Junior ba Dan'ka bane kittttttt! aka kashe wayar tsaki *Habeeb* yayi tareda fadin banza kome nayi masa yake wani kokarin daukar fansa akaina Oho!..
Mtsww! KO" anfada masa daukar fanka akan *Habeebullah* abune me sauki?...mtsww aidama ka tsaya nayi maka godiya akan tuni dakayi mun cewa "Junior badana bane, ni kaina dama zuciya ta tadade tana ko konto akan shidin 'Dana ne koba 'Dana ba ne domin banajin kaunar shi araina irin wanda uba keji akan 'Dansa,
Dasauri yashiga motar yafita daga harabar gidan da gudu har escorts dinsa suna mamakin yanda yafita da gudun haka anya lafiya?...gashi yace bayason ayi escort dinsa.
*Habeeb* kam suna fita yabiya ya siya masu ice cream da sweets sannan suka nufi asibiti, kamar yanda yace wanda suna shiga Lili tasaki kuka, dai-dai lokacin da yayi parking Dasauri yajuyo yace lafiya Lilin Dady?.. cike tsoro tace Dady bana chon allula kadi?..yace Oh! my sweet girl stop crying baza ayi maki allula ba kinji?..ya kareshe fadi tareda shafa kanta, kaita gyada tana share hawaye sannan yafita yaje yabude mu su suka fito dai-dai lokacin da *Harees* yashigo da motarsa,
Dasauri *Harees* yafito daga mota yanufe su yana fadin Dan'uwa wai meke *FARUWA* ne?.. *Habeeb* yace humm! kaida bari mu karasa office nan suka nufi office din.
Bayan sun zauna sai *Harees* ya kalli *Habeeb* yana neman karin bayani, cikin har shan turanci yace Dan'uwa inason kadibi jinina dana Junior dana Lili ka auna inason nasani shin su din ya'yana ne "KO ba ya'yana bane, cike da tsoro *Harees* yace Dan'uwa meya faruwa kuma?...yace Dan'uwa nadade ina zama da mazinaciya fasika tabbas kafin *Jana* tabar duniya saita ga saka makon abinda tayi mun, nan yafada masa abinda yafaru tareda nuna masa sakon.
Cike da tashin hankali yace Dan'uwa baka tunanin wanine yakeson bata maka suna?...kai *Habeeb* ya girgiza tareda fadin "a ah Dan' uwa kodan yanda Allah yamuna mun *Jana* tanacin amanata hakan zaya faru, sannan duk dacewa nasan inada makiya saidai ban taba tunani akwai wani Da'adam zaya iya bata mun suna ba, tunda Ubangiji na be bata mun bako?..
*Harees* yace haka ne to yanzu ka yadda kenan?...yace "eh domin zuciya ta tadade tana ko konto akan hakan wanda ban taba fadawa wani mahaluki ba, saidai kawai nabar shi araina amma yanzu inason kayi mun abinda nace wanda shi zaya tabbatar mun da gaskiya alamarin, *Harees* yace Ok" tareda fadin Dan'uwa amma wakake tunani kunada matsala "dashi da harya keson daukar fansa akan ka?..
Wata dariya *Habeeb* yayi me cike da bacin rai yace mutumin dana kama da *"Jana,* ido yazaro tareda fadin ya'akayi kagane shine?.. yace tun lokacin danake dukansa yana ihun fadin nayi hukuri har yanzu inajin sautin muryar sa a kun ne shiyasa nagane shine, Kai ya gyada tareda dauko abin diban jini yadibi jinin *Habeeb* dana Junior Lili kam da kyar aka diba domin sai kuka take tana zagaya office din,
tana fadin ita batason allula๐ saida *Habeeb* yadaka mata lafiyayyan tsawa tukun na, tareda rike ta aka diba sai kuka take tana kiran Aunty *Deeyan* ta, bayan ya diba yafara gudanar da aikin sa.
Cikin lokaci kankani *Harees* yagama duka yafitar da results ahankali yake duba wa, hankalin shi yai matukar tashi da ganin saka makon hakan ne yasashi dago kai dasauri yakalli *Habeeb,* wanda shidin ma kallon *Harees* yake kallo me dauke da kainake saurare....
Ahankali yace Dan'uwa l'm sorry to say result yanuna Junior ba jininka bane ma'ana ba 'Dan" ka bane, wani abin mamaki kuma result din Lili yanuna cewa ita din jinin kace wato yar kace, ajiyar zuciya *Habeeb* yayi tareda fadin ainasan haka zata faru, cike da mamaki *Harees* yace kamar ya kasan haka zaya faru?...yace kamar yanda wancan mutumin yafada sannan nikaina zuciya ta tadade tana tunani tareda tambayar me yasa banajin Junior araina?..
kamar yanda nake jin Lili amma ban samu amsa ba, sai gashi yau Allah yabani amsa tabbas Junior ba "D'ana bane, d'an wannan "mutumin ne domi yau naga tsantsa kamar da Junior yayi dashi.
Sai kuma yai shuru tareda furzar da iska taba kinsa cike da bacin rai yace Dan'uwa *"Jana* tacuceni kuma sai Allah ya'isar mun, ahankali *Harees* yace kayi hakuri Dan'uwa bakai *"Jana* tacuta ba kanta tacuta" kuma ita" da Allah *Habeeb* yace haka ne tashi muje gida,
Yafadi tareda mikewa ya saba Lili akafada kasan cewar tuni tayi bacci, *Harees* yace Ok" yanzu to me abin yi game da "Junior inanufin kar maganar ta bayyana wanda hakan zaya 'iyabata maka suna?... murmushi yayi yace nafada maka tunda ubangijina be batamun suna ba to babu wanda ya'isa yabata mun, koda maganar zata fita ne bazan damuba duk da nasan wasu zasu zageni amma bakomai tunda ban zalince taba asalima "ita ce ta zalinceni don haka ita duniya zata zaka, sosai kaga yakare kanta kenan KO?..
yace haka ne yace yauwa game da Junior karka damu nasan abinda zanyi, sannan Insha'allah ni *Habeebullah* baza'a ji abakina cewa Junior ba Dana bane, saidai aji abakin ta wanda na tabbatar amana tane zayaka mata tafada, *Harees* yace hakan shine daidai sannan yakama hannun Junior suka fita suka nufi gida.
Koda suka isa gida direct part Hajiyarmu *Habeeb* yanufa yakai su Lili ya'iske Hajiya tadawo, sannan yafito yanufi part din su *Harees* yana shiga *Deeya* tanufe shida kyakkyawa baby boy wanda tunda tashiga ta dauke sa yake hannun ta, mika masa yaron tayi tareda fadin sweet Hmm na sannu,
yace yauwa honey *Leemah* ta tareda zama yana kallon yaron yace masha'allah wlcm to the world