Showing 72001 words to 75000 words out of 99609 words

Chapter 25 - CAPTAIN SADIQ COMPLETE BOOK BY Salma Mas'ud Nadabo.pdf

sannan anbiyawa mutun
30 kujera maka , kabara wajan ya dauka tare da hamdala, sannan Kuma ga muhimiyar sanawa
ita ce majeed ya samu matar da zai aura, sadiq dake zaune saman kujera gaban shi ya qara
yankewa ya fadi, muryar Alhaji babba ce ta dawo mai dodan kunne, ba kowa bace sai yar gidan
ibrahim wanda yake ruqu fatuha Kuma har gidan iyayan ta muje munyi bin cike ashe ma akwai
sanaya a tsakanin mu Kuma sun aminci sun bada. wani irin gumi ne ya karyo ma sadiq mai
matsanan cin zafi take nan ya fara ji wutar shi na dauke wa ba sadiq ba hata mom sai da ta
girgiza da wannan furin cin, wata kalmar ya qara jefowa a karo na biyu sadiq Kuma mun yanke
shawarar bashi kanwar sa basma tare da sharadi idan har ya kawo wadda yake so nan da sati
daya kamin asa biki to za'a basa dama ya auri wadda yake so basma ma kuma ta hakura zabin
shi wannan shine hukuncin dana yanke. sannan ya kalli baban basma Alhaji khabiru cika mana
taro da addu'a.

Gabaki d'aya parlour juyawa sadiq yake da kyar ya samu ya miqe, majeed in ban da washe

baki da yake ba abunda yake dan ko ta kan sadiq bai bi ba haka basma baki har kunne sadiq
ne ka dai da mom basu farin ciki sai hanan. yana fitowa d'aga parlour parking space ya nufa
cikin sauri ya bale murfin motar ya shiga da gudu ya fisgi motar ya harba kan titi gudu yake
tsulawa kamar zai tashi sama yana isowa gida ya danna horn bala mai gadi na bude mai geta
yace "Subhanalal " saboda yadda sadiq ya shigo da motar yana shigowa ko dai-daita parking ya
kasa ya bale murfin motar ya fito cikin sauri ya wuce part din shi yana shiga ya zame bakin kofa
tare da dafe kanshi‍♀ maganar Alhaji babba na dawo mai. mikewa yayi ya shige bedroom
saboda har yanzu bai dai na ganin jiri ba, wani irin kuka sadiq ya saki mai tsuma zuciyar mai
saurare kneel down yayi a wurin can Kuma ya mike yashiga fatali da kayan d'akin kamar saban
kamu. sai da yayima d'akin fata fata ya shiga toilet da kayan jikin shi sakar ma kanshi shower
yayi, maganganun Alhaji babba namai yawo a brain wata zuciyar tace "Wato jiya fatuha tabama
majeed izinin turawa gidan su?" hadeye kukan da yake yayi tare da fitowa sharkaf ya zauna
kasan carpet be damu da kayan dake jikin shi ba.

Bangaran fatuhu ko tunda su mom suka fita gabanta ke faduwa, ta rasa dalilin haka ta rasa
suku nin ta jin an bude kofar d'akin ya sata waigowa mom ce tsaye bakin kofa murmushi fatuha
ta saki wanda iya karshi laban ta, mom har kun dawo da wuri haka? eh tace tana qoqarin danne
damuwar ta tare da qarasa shigowa zama tayi kusa da fatuha cikin sanyi murya tace "Fatuha
gobe da safe ki shirya zaki je wudil baffa nasan ganin ki?" sannan ta tashi ta fita kallo fatuha
tabi mom da shi take nan jikin ta ya haubari da tsoro tsoro ko dai uncle ya kai qarata kauda
zancan tayi tasan ma ba zanyi hak'a ba ,amma zuciyar ta na cike da tanbayoyi, ganin bata da
amsa ta hakura.


Ola sadiq ya kira a waya bugu d'aya zuwa biyu ya dauka ina san ganin ka sadiq ya fada a
taqaice ,ko da ola ya zo ganin Watsin da akayima dakin tsoro ya bashi kallan sadiq yayi da
magana a bakin shi ganin fuskar sadiq ba annuri yaja baki ya tsuke. nuni ya mai d'aya gyara
d'akin shi Kuma ya shigida saman sofa hawaye daya na bin daya kamar ba soja ba,

Gabaki d'aya gidan Alhaji Ibrahim ba wanda ya rintsa, d'aga angel sai abba ne kawai suka
samu bacci bangaran sadiq inban da kukan zuci ba abinda yake, fatuha tunanin me yasa baffa
ke neman ta? take ko dai inna ce ta rasu? ba'a San fada mata girgiza kai kawai tayi.

Tunda safe fatuha ta tashi ta shirya cikin riga da sket din ta na atamfa yellow mai ratsin
white a jiki masha Allah kayan sun hauta sai fuskar fayau, bayan ta kamala ta fito parlour cikin
natsuwa ta gaida mom da abba d'ake ta break angel na gefe itama ganin bata ga sadiq ba yasa
gaban ta ya qara faduwa a karo na biyar jiki ba qwari ta zo ta hada tea kurba biyu zuwa uku ta
aje , mom ce tace "Fatuha har kin koshi?" eh mom dama in zan yi tafiya bana wani cin abinci to
mom tace , sannan ta qara da cewa ga driver nan zan h'ada ku da shi in ya kai ki yau zai maido
ki ki gaida mutun gida sannan inkin Isa ki kira ni ki fada min. lagwabe kai fatuha tayi tace
"Wallahi mom jiya wayar ta lalace" garin yaya? fadowa tayi d'aga dressing mirror ta dauke, eyya
to bari na baki baby Nokia in kin dawo a sake wata to fatuha tace tare da shi ga daki ta dauko

sim din ta miqa mata wayar .mom tayi ta zura sim din ciki har ta kai bakin kofa ta dawo tare da
haurawa sama part din sadiq ta nufa a hankali ta murda handle din kofar taji Kule gam tsoro ne
ya kamata amma ba yadda ta iya haka ta dawo tare da yima mom sallama angel ko sai rigama
take sai tabi fatuha mom ta hana.
Shigewa mota tayi driver ya harba da su kan titi cikin dan qanqanin lokaci suka Isa wudil.
cikin kwatan can fatuha har driver ya kawo ta gidan fitowa tayi a hankali tana qare ma gidan su
kallo gabaki daya gidan ya canza a yadda ta San sa mamaki ne ya bayana a fuskar ta qarasa
Shiga tayi cikin sallamah inna d'ake parlour ce ta fito tare da yima fatuha maraba da zuwa duk
da fatuha ba'a cikin jin dadi take ba bata yadda inna ta gane ba, parlour ta janta suka Shiga har
yanzu mamaki ne shifide a fuskar ta tace cikin sanyin murya "inna waya gyara gidan nan?"
murmushi inna ta saki ina yaran nan sadiq wallahi shi ya mana abin arzikin nan murmushi
fatuha ta saki mai cike da jin dadi baffa ne ya yaye labilan ya shigo har qasa fatuha ta tsugunna
ta gaisheshi amsa mata yayi a taqaice sannan ya samu wuri ya zauna. itama fatuha qasa
tayima kanta mazauni tana jiran jawabin baffa gyaran murya baffa yayi tare da cewa "Fatuha
nasan cewa na maki laifi amma kiyi hakuri ina fatan bazaki watsamin qasa a ido ba? ina fata
bazaki bani kunya ba ?duk wannan jawabin da baffa keyi kan fatuha na qasa ,d'ago kai tayi tace
"insha Allah baffa bazan baka kunya ba" yauwa diyar albarka, dama dan uwan sadiq ne ya zo
neman auran ki tare da iyayan shi jiya da dare, mukanmu munyi mamaki da wannan zuwa
fatuha ganin halacin da zura'a suka mana gashi nasan baban yaran hakan yasa na amince dan
na lura yaran mai natsuwa ne Kuma dama neman auran budurwan anso iyayanta su zaba
mata miji Na gari da wannan nayi la'akari na zaba maki majeed a matsayin miji. dagowa fatuha
tayi a razane dan sai yanzu ta fahimci inda aka dosa idanuwan ta tap da kwalla suka ciko nan
take hawaye suka fara anbaliya a fuskar ta me yasa mai kyau zai mata irin wannan horan me
yasa fita tayi d'aga parlour da gudu ta fada dakin inna ta saki kuka mai tsanani mai ban tausayi,
inna ce ta dafa bayan ta tana lalashin ta, haba fatuha bai kamata ki watsawa muta nan qasa a
ido ba Kuma kowani mutun da qadarar dake zuwa mashi .fatuha idan dai majeed alkairi ne a
gare ki Allah ya tabatar haka inna ta riqa bitana tausar fatuha har ta samu tayi shuru tana sakin
ajiyar zuciya ko ruwa kasa sha fatuha tayi sai bayan sallah la'asar suka dau hanyar kano wayar
tace dake cikin jaka taji qara message sai a lokacin ta tuna da mom tace ta kira ta curo wayar
tayi ta karanta message din kamar haka,

_Sister ina matukar farin cikin Sanar d'ake yau buri na ya cika, tun jiya nake qoqarin kiran ki
wayar takin Shiga ba wani albishir bane ila yaya sadiq ya kusa zama miji a gare ni ,sannan ina
taya ki murnar zama inlow a gidan mu cikin family din mu d'aga basma._

Wani irin kuka fatuha ta saki mai cinrai ko ida karanta sakwan ba tayi ba wayar ta fadi jikinta in
banda bari ba abin da yake. ashuru driver ya juyo haba fatuha komai yayi zafi maganin shi Allah
bai kamata kina kuka irin h'aka ba ,duk wannan magana da ashuru yake fatuha ba jin shi take
ba kalmar sadiq yazama miji Na kawai qwawalwarta ke fada mata har suka iso garin kano
fatuha na sheka kuka kamar ranta zaifi ta, ko da ashuru yayi horn aka bude geta kafin ya tsada
motar ta bale murfin motar ta fita da gudu sadiq da yanzu ya ji Qarar shigowar mota d'aga labila
yayi tare da koma ya cigaba da zarya a bedroom din.

Da gudu fatuha ta haura sama ko kallan muta nan parlour batayi ba part din sadiq ta wuce
Allah ya bata sa'a tana bude kofar ya bude, ganin bata gashin a parlour ba yasa ta shigewa
bedroom da gudu . fadawa tayi jikin sadiq tare da sakin kuka mai cinrai ,rintse ido sadiq yayi
yana jin yadda fatuha ke sheqa kuka cikin sarkewar murya tace "Uncle dan Allah karkamin
wannan horan wallah bazan iya dauka ba, dama ace mafarki nake abin da nake ji ba gaske
bane ta ida zancan tare da sakin saban kuka ta zame kasa.......



*Taku har kullun salma mas'ud nadabo*.
*CAPTAIN SADIQ*
‍♂

*Writing by*
*Salma mas'ud nadabo*


*Edit by*
*Raheenat*


*REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM*
★We are the best★

http/mobile.Facebook.com/Real-Hausa-fulani-writers-forum
RHFWF-173984973194167/?refid=52&red=opera_speed_dial_&yn= H-R

*Email* realhausafulaniwritersforum@gmail.com

*Facebook* www.Facebook.com/REALHAUSAFULANIWRITERS FORUM.COM



77_78
Kuka fatuha ke rairawa Kamar ranta zai futa. gabaki d'aya jikin ta rawa yake qafafuwan sadiq ta
riqe cikin shashekar kuka tace, "Please uncle I beg u in the of name of God a janye maganar
auran nan wallahi ban shirya yin aure yanzu ba taqara rushewa da wani saban kuka" har yanzu
jikin fatuha bar'i yake ,uncle ya zanyi da karatu na? bayan duk duniya ba abinda nake so sama
da shi, wallahi uncle ba abinda ke tsakanina da majeed kaji ta qara sakin kuka mai cin rai ( *ko
ni salma sai da na matse kwalla*) da kyar sadiq ya sai ta kanshi tare da hade hawayan d'ake
maqale a kwayar idanuwan shi ya juya, d'ago fatuha yayi d'aga zaune da take ya zaunar da ita
zaman bed amma duk da h'aka ba daina kukan tayi ba .fridge ya bude ya curo robar ruwa ya

tsiyaya a cup ya miqa mata .kuka kawai take baji ba gani, aje cup din yayi bedside drowe ciki
cool voice din shi sadiq yace "Fatuha!" tsagaita kukan tayi tana kallan sadiq , lalashin ta sadiq
ya shigayi cikin sanyi murya yace, "Fatuha ina so ki sani ko kadan bani na maki haka dan na
hora ki" daura hannu shi yayi a fuskarta, h'aka itama fatuha ta daura nata saman hannu shi tana
sauke ajiyar zuciya. ya cigaba da cewa "Bayan na dau alqawarin samamaki farin ciki har
qarshan rayuwar ki fatuha? dan meyasa zan rusa maki mafarkin ki? ina so ki kasan ce mai
daukar qadara mai kyau da mara kyau, da anyi shawara dani fatuha ba abinda zai sa na
amince a katse maki karatun ki? ko yanzu nasan majeed zai barki kiyi karatu kinji, ki kasan ce
me yima iyayan ki biyaya zaki ga riba haka, kuma insha Allah zaki so majeed saboda majeed
nada kyawawan hali kuma yana sanki zai b'aki duk wata kulawa .ba zai bari ki taba zubar da
hawayan ki a kanshi ba, ki daure ko so d'aya ne ki sama ranki son majeed ko dan yana dan
uwa na" wasu zafafan hawaye ne suka gangarowa fatuha tana bin sadiq da kallo, dan ko bakin
magana ta rasa, sadiq ko in ban da daurewa ba abinda yake dan numfashin shi neman
yankewa yake ,sai ya numfasa yake cigaba da maganar saboda zafi da quna da qirjin shi ke
mai, glass cup din sadiq ya miqa ma fatuha ta kafa kai ta shanye ruwan a hankali taji sanyin
ruwan na ratsata, shiru suka dauka na mintina ba wanda ya tanka, can sadiq yace "Fatuha
kimin promise baza ki tada hankalin ki ba, da kyar fatuha ta iya furta to wasu hawayan suka
sulalo, jiki ba qwari ta tashi tana qoqarin fita sadiq ya bita da kallo dan bejin zai iya tsaida ta
saboda ganin tama qara famamai ciwo a ransa".



Tana fita sadiq ya kafa rubar ruwan ya shanye yana maida numfashi tare da ganin wasu
taurari namai yawo,

Tsayawa tayi b'akin stairs ta share hawayan ta dan bata san mom ta gani cikin natsuwa ta
sako, mom da fitowar daga kitchen kenan ita da baba jinmai murmushi ta saki ah fatuha har kin
dawo eh tace tana qoqarin hadiye hawayan idanuwan ta, masha Allah ya su inna? lafiya lau
tace, sannan mom tace ina fata baffa bai maki dole ba d'aga kai kawai tayi alamar a'a, baba
jinmai ce ta shafa fuskarta tace "Alhamdulillah hajiya ni dai bani da abin cewa kun gama min
komai a rayuwa ta ida zancan tana matsar kwalla" d'aga kawo fatuha aiki sai gashi ta zama yar
gida har zaku aura da ita hajiya na gode na gode Allah ya bar zuminci baba jinmai ta fada tana
share kwalla idanuwan ta, haba baba ai duk mun zama d'aya ai fatuha ta cancanci abinda yafi
haka, haka baba jinmai ta rinqa zuba Godiya sannan tasa kai ta fita, fatuha kuma ta shige bed
ko da shiga d'akin sana'ar ta fara wato kuka dan ya zamar mata jiki d'aga shekaran jiya zuwa
yau. bedside drowe ta bude ta Ciro sarkar da sadiq ya bata tana kuka sai ta ci kuka ta gaji
sannan bacci ya dauke ta


Bangaran basma in ban da murna ba abinda take take, duk wasu qawayan ta ta fesawawa
zata auri handsome, har wani jin ta take a sama yanzu, majeed ko ya kira layin fatuha har ya
gaji yanke shawarar zuwa gidan gobe yaga sanyin idaniyan shi, sannan ya juya ya gyara
kwanciyar shi .

Kiran sallah ne ya tashi fatuha jiki ba qwari ta shiga toilet tare da sheqa waka ta dauro alwala
wani irin jiri ke dibar ta saboda kukan da tasha jiya ,da kyar ta iya gabatar da sallah ta zura
uniform dinta tare da daukar school bag din ta ta fito,

Ko da ta qaraso dining area mom ce da abba sai angel dake gefe cikin natsuwa ta gaishe su
kamar kullun taja kujera ta zauna .ruwan tea kawai ta iya hadawa tana sha kamar tana shan
magani kamshin turaran da taji ne yasata dagowa sadiq ne cikin uniform din shi yana riqe da
briefcase din shi yasha kyau har ya gaji sai dai fuskar shi ba walwala angel ce ta gaishe shi ya
amsa tare da yi mata pack, kallan shi fatuha take har ta kasa kauda idanuwan ta haka shima
sadiq ita yake kalla tuni idanuwan ta sun cika da kwalla girgiza mata kai sadiq yayi alamar kar
tayi kuka lumshe ido tayi tare da qoqarin hadiye kukan da ke niyar kuboce mata, sallamar
majeed ce ta doki dodon kunan ta. ware ido tayi tana kallan kofar sanye yake da uniform din shi
sai sheqi yake qarasowa yayi tare da gaishe da su mom amsawa tayi cikin fara'a, tare da cewa
yasu umma? umma lafiya lau mom , sadiq d'ake tsaye take fara'a shi ta dauke daurewa yayi ya
tataro natsuwar shi tare da sakin murmushin karfin hali, my man yau kai ne da safenan Sosa
keya majeed yayi tare da kallan fatuha kauda kai tayi ta cigaba da juya tea din dan ba sha take
ba.


Haka sadiq ya rinqa danne zuciyar shi, fatuha kuma haka ta gama juya tea din ta tashi tare
da daukar school bag din ta ta ja hannu jidda suka fice tare da yima mom sai sun dawo .tana
fita majeed yabi bayan ta haka shima sadiq kasancewar office zasu ,

Zata shiga mota majeed yace baki ji, daure fuska fatuha tayi dan wata tsanar majeed take ji
juyowa tayi a fusace dan ta gayamai mara dadi hango sadiq tayi bakin mota da alama su yake
kallo , kauda kai sadiq yayi yana wani jin suya a zuciyar shi da radadi bale murfin mota yayi ya
shige, murmushi fatuha ta saki wanda iyakar shi laban ta tace uncle majeed inakwana, cikin
zaquwa yace lafiya lau my love, cikin sunyi murya yace "Fatuha!" na'am

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login