Showing 39001 words to 42000 words out of 119109 words
Chapter 14 - MAGAJIN IZZAH! COMPLETE Writing Mai Dambu.txt
nan kuma, muka so gaya maka waye kai sai muka fahimci kana farin ciki da yadda kake rayuwarka, dan haka muka bar maganar bamu ne muka haife ka ba.
Abun da muka so shi kake mana, dan haka muka sanya ka koma mataki na biyu na digirin ka, tunda a bangaren da ka karanta, duk wannan abin da muka yi shine zaka saka mana da lalata mana Yar mu? Mun gode amma zaka iya tafiya tunda mun gaya maka waye kai zaka iya tafiya don Allah ka bar mu karka lalata mana rayuwar ta."
Ta karshen maganar cikin Kuka, da ban tausayi.
"Bani da inda yafi nan! Amma dole zan tafi naji me yasa aka min haka, nagode kuma ina baku hakuri da abinda nayi muku."
Daga haka ya fice daga gidan baki d'aya, tafiya yake da kafa. Idanun shi jajjur. A wani ƙwana suka haɗu da Najim!
Inda suke ta tafiya a tare.
"Saraki!"
Juyawa yayi tare da kallon Najim, mai da hankalin shi yayi gaban shi, har zuwa wani shagon coffee. Zama suka yi Jay yace a bashi coffee me zafi, Najim yace a'a me sanyi dai.
"Saraki! A yadda kake a tafashen nan idan ka sha ruwan sanyi, yafi na zafin da zaka sha. Ai sai ka iya tadda gari guda."
Bai ce kala ba, haka ya cigaba da shan shayi me sanyi, har suka gama Ya mike zai tafi.
Najim yace.
"Ranka shi dad'e! Idan aka cigaba da haka wallahi muna cikin wani yanayi, ka taimaka min na samu gurin fakewa."
Iska yaja sannan ya zuba mata ido, yace.
"Ina cikin damuwa!"
"Na sani, amma al'ummar daura da Mahaifinka tare da kakanni ka, suna zuba ido tare da saka tsammanin Magajin Izzah!
Ban san me yasa kowa yake dauki da son ganin ka ba, amma Shehun Borno da wasu daga cikin dangi suna maraba dakai, Sunana Brrst Najim Aswad Magaji, ni ne lauyan masarauta.
Da fatan zaka Duba alamarina. Ga takardan jirginka bazan iya zama na wasu lokuta ba, idan ka shirya jibi zamu sauka a Lagos."
Cikin hasala ya kalli Najim,
"Umarni kake bani?"
"A'ah Saraki! Abinda ya dace nake, Saraki tun ranar da ka b'ata nake tare da Abba Jaamal, dan bana son ya duba gurbin ka, ya ga baka nan, idan kayi ra'ayin tafiya shi kenan, amma zukatar mutane suna dayawa akan ka. Sa ran su yayi matukar tasiri akan zukatar su.
Ya zaka ji labarin Jarumar Uwar da ta tabbatar da kaine zaka kawo karshen rikicin masarautan da Insha Allah, faffutika tayi tare da sadaukarwa. Ko kasan ciwon da miji yake ji a lokacin da ya rasa matar da yake matukar kauna! Sannan abin da tabar mishi aka wayi gari ya b'ace, ka san nauyin da zuciyar Wannan uban yake dauke da shi.
Ka duba yadda duniya take, ka dubi yadda kowa yake tattalin abin da yake na shine.
Zaka iya rasa yau a rayuwar ka, amma gobe idan kayi ƙoƙarin gano bakin zaren zaka rike shi da daraja. Mu ahalin sarauta an san mu da tsage gaskiya,.tare da fadar ta, bama gudun abokan gaba. Domin da su aka halicce mu, abinda muka sani zartarwa.
Hukuntawa, adaltawa Dai-daiton laifin tsakanin talakawan mu da attajiran mu, don Allah idan kana son Ahalinka su kare rayuwar su cike da kunya bismillah idan zaka iya zuwa ka tsayawa mutanen da suka saka rai. Da zuwan ka, koda yaushe mafarkin su Magajin Izzah zai dawo. Ashe ba haka bane domin sarakin da nake gani a gaba na lusari ne."
A fusace ya makure wuyar Najim.
"Toh idan har zaka iya fusata kamar yadda kayi a nan. Saboda kimar ka ka bi mace har nigeria, toh lallai Jarumin da ya wurga yarinyar nan wancan ranar a cikin kashin dawakai! Ya kuma sake nasarar sanya ta cikin kashin aladu.
Wannan jarumin da ya kalli idon Sa'i yace mishi ya kiyayye harshen shi da fadar magana ga mahaifin shi, ba tare da yaji d'ar ba. Toh gobe da karfe biyu na yammaci ina jiran shi a tashar jirgin sama, nasan Saraki baya sab'a magana, amma naga isa da ikon nan da na sani a da. Ina nan ina jiran mai martaba sarkin Daura."
Daga haka ya dauki rigar shi ta sama, ya bar inda Jay yaƙe. Yana tsaye kamar bishiya. Tsigar jikin shi mik'ewa yake.
Wani irin jin kai tare da Izzah musamman wanda yake cikin kowani jinin sarauta, cikin ƙasaitar da bai zaci yana da ita ba yake tafiya, tare da wani irin yanayi wanda yake cike da mulki tsantsar ta.
Koda ya isa gidan. Ganin kowa yayi shiru, suna ta harkokin su, sai dai Munih da take bin shi da ido, har ya shige dakin shi, bai kuma fitowa ba.
.....
Har washi gari, yana dakin ya gama had'a kome nashi, sannan ya fito da manyan jakukkunan shi, tare da kallon agogon hannun shi, karfe biyu saura minti sha biyar.
Koda ya fito ya same su, suna cin abincin rana. Zama yayi har suka idar yana yi yana kallon agogon hannun shi, tare da sake murmushin takaici, dan ya fahimci sabida shi suke kin gamawa, amma bazai iya barin su ba, zai zauna dasu. Har su gama.
Koda suka gama kowa kama gaban shi yayi zai tafi yace musu.
"Ku dakata mana!"
Cak suka tsaya, kwaso takardun shaida karatun shi yayi, sannan ya mikawa Baba furofesa, ya mika mishi, kafin yace.
"Nayi Kuskure, kayi hakuri ka amshi ban hakurina, gasu kaine ka bani so cikin so da kauna, yau na dawo maka su a matsayin tsintaccen nan.
Nasan nayi kusakurai masu yawa, amma ina rokon Allah ya baku hakuri, zan tafi naga Ahalina Insha Allah zan dawo saboda shagona da yake nan, Bama iya shi ba, sabida ku zan dawo.
Nasan nayi laifi me girma, don Allah ku yafe min."
Daga haka yaja jakunan shi zai fita, da mugun gudu Munih ta rungume shi tana faÉ—in.
"Wallahi mutuwa zan yi idan ka rabu dani, don Allah ka dawo ina sonka."
Janye jikin shi yayi bai kuma sauraronta ba, ya fita abin shi ihu take tare da cewa a dawo mata da shi, shine abokin rayuwar ta,.
.........
Karfe biyu saura minti biyu, Najim ya hango shi, yana shigowa, cikin sauri ya isa gurin shi tare da rungume shi. Mara mutunci. B'ata rai yayi kamar ba shi ba.
Har inda aka duba kayan shi, sannan ya wuce abin shi suka nufi cikin jirgin.
----
Abuja..
Tunda Aunty Aina'uh ta zo min da maganar d'an mijin kawarta, naki bata fuska. Har dai ta gama damuwarta sannan ta kyale ni, yau da wuri na tashi sabida ina Son na fita, naje na duba mai na da sabuluna, sun kusan karewa.
Sosai na shirya sai dai fuskana babu kwalliya, sai man baki da na saka, ko kallon inda Aunty Aina'uh take banyi ba, nacewa karamar yarinyar ta, dan itama Aunty bata haihu da wuri ba, kuma tsakaninta da Maama wato Mamana shekaru uku ne, sai da ta shekara sha takwas, kafin Allah ya basu Haihuwa.
Babban yaron yana makarantar king Abdul Azeez riyadh, sai kuma wacce take bin shi tana nan turkish, na abuja.
Sai wanna yar karamar wacce taci suna Mamana, suna kiranta da Hanan. Dan haka na riko hannunta tare da janta muka fita.
.....
Sahad store muka je, Nan na sayi kayan amfani na, muka nufi gurin biyan kudi.
"Kowa yafita ga dan gidan ministan Abuja zai sayi kaya!"
Lokaci guda mutanen cikin, shagon suka fara fita ban dani da na ke biyan kudi.
"Ke wacece da ba zaki fita ba, ana magana."
Mikawa matar katina nayi, sannan na kwashi kayana tare da riko hannun Hanan, zamu fita. Kamar ance na d'aga ido na, sai akan Asood. Ban yi mamaki ba.
.kawai nasaka kai zan fita ya tsare hanyar fita, cikin isa ya iso gabana.
"Karuwar mu!". Rintsa idanuna nayi tare da kawar da kai na.
"Ina abokin ciniki ki? Koda yake naji ana min tayin auren wata bazawara, amma bazan ki tayin ba. Idan na duba yadda ko ina yake cike tam!"
Ya kai hannun shi kamar zai tab'a ni nayi baya, cike da bakin ciki.
.. ..".karki damu! Zan zo har gidan na kwashi rabona abin da Jay ya bari zan tattaro na karasa"
Takowa yayi gabana, tare da min kallon kaskanci.
"Karki manta nan ba Calgary bane! Nan birnin tarayyar mu ce! Muke fada muke yadda muka so!
Kudi mulki Izzah mun gaje shi, ki kalli Asood Ahmad Buba Yaro kika mara, idan zaki iya ki fara gudu, karki tsaya karki tsaya karki tsaya, domin sai na jiyar da ke, zafin da bazaki iya kwatanta ya yake ba.
Sai na gama miki azzabar da ba zaki iya kwatar kanki ba, kina da sauran lokaci, na gudu ki nime matsirata. Sabida shi wancan da na turo ya kasa min yadda nake so!
Fatimah Khatoon fara gudun ceton rayuwarki.
#Mai_Dambu
10/23/20, 9:55 AM - Ummi Tandama: Acct: 0472282105
GTBNK Ramlat Abdulrahman Manga 300â‚? katin mtn 300 normal posting 21/October Insha Allah
Zahrahn Addah Ramlat domin nuna shaidar biya! ita za a turawa....
07035133148/ +22784506476 yan Nijar zasu iya samun A'isha Indo Nijar.....
*Cusa Kai*
"Ba zan tab'a gudu sabida kai ba! Ba zan nemi maboya sabida kai ba, abinda na sani Allah yana tare da mai gaskiya kai baka isa kayi min abinda bai min ba, kai ba kowa bane facce mujirimi, baka isa ka tozartani ba, sabida Allah ya kare mutanen da suka yi imani da shi.
         Idan ka isa kabi layyin unguwar mu tukun sai na san kai na musamman ne! Har ila yau yarintar tana kwance cikin jini ku."
   Daga haka na wuce abi na, ban ma bin ta kan shi ba, sabida ba zan iya karar da wani abu bayan wanda idanuna suka gane min ba.
   .... Koda muka isa gida, Aunty Aina'uh taso fahimtar halin da nake ciki, amma naki bata fuska, dan na fahimci ita ke son b'allo min ruwa.
.......
  Ranar Laraba jirgin su Najim ya sauka a garin Lagos, cikin nutsuwa suke saukowa tare da jin dadi. Shaƙar iska yayi cikin nutsuwa sannan ya fesar yana me ɗauki ganin mahaifar shi.
     Kallon shi Najim yayi kafin yace mishi.
"Abba ya gaya min cewa, garin Lagos yana daga cikin garuruwa masu dinbun tarihin rayuwar ka, domin anan aka kafa soyayyar da ta samar da kai.
        Dan haka idan zamu dawo nayi kokarin ganin mun sauka ta nan, domin ka fara jin ƙarfin shigar masarautar daura"
      Tab'e baki yayi cikin ko in kula, kamar bai damu da yadda yake so garin ba, yanzun burin shi su isa garin daura yaga yadda mahaifar shi take. Wannan itace muradin zuciyar shi. Zaman minti goma suka yi sannan suka nufi wata jirgi da zata kwashi fasinjojin Abuja sannan ta ajiye su daga can su sami jirgin da zata dauke su zuwa daura.
           Tunda suka taso kirjin shi yake bugawa, tun yana zaune har ya tashi zuwa ban dakin cikin jirgin. Bai yi kome ba ya kuma fitowa.
     Ya zauna, har suka iso abuja, anan suka sake samun wani jirgin zuwa katsina, kafin nan jikin shi ya jike jagwa da gumi.
   Karfe biyar da minti goma jirgin su ya sauka a garin Katsina, suna isa suka sami. Fahad.
  Cikin wani irin farin ciki idanun shi cike da kwalla ya rungume Jay, duk da ya manta fuskar shi, amma ya rike shi sosai.
     A hankali ya juya ga Najim yana cewa.
"Aminin Arziki Barka da hanya. Babban lauyan mu!"
. Ya sake Jay ya rungume Najim, murmushi yayi sannan Najim yace mishi.
"Ni ba surukinka bane da bazaka gaishe ni da da'a ba?"
    "Banza Bakwai, ba zan gaida ka ba, mara mutunci. Jannart ce ko zaka mutum ka dawo sai an bani ita ko Saraki?"
   Murmushin yake Jay yayi tare da juya idanu, motar Fahad suka shiga.
    Suka fara tafiya, suna hira sama sama, tunda suka fara tafiya Najim ya fahimci ana bin bayan su, dan haka yacewa.
"Kai Uban Maganannu tsayar da motar nan"
Tsayawa Fahad yayi motar tazo ta wuce su da gudun tsiya, murmushi Najim yayi sannan yace.
"Kasan me zai faru? Mu koma gidan sarkin Katsina"
    "Malam Lauya!"
"Nace muyi abinda na gaya maka," ya faÉ—a da matukar muhimmanci.
"Toh"
Da sauri ya sake hannun da suke, sannan ya koma daya bangaren, tun kafin su bar layin gurin Najim ya kira wayar wani kafin su isa wata mota kirar toyota, tazo tare da wani saurayi.
 Canza motar suka yi sannan Najim ya mika mishi kudin da zai hau wata yana cewa..
"Mansoor karka shiga motar ka bar shi anan, sabida wani dalili.
   Wannan kuma zamu tafi da ita, dan haka ka kiyayye yan sanda zasu zo nan!"
  Daga haka suka koma cikin motar, Jay na kallon su, har suka fara tafiya Fahad yace.
"Najim! Kaina ya daure da sauya motar nan, sannan kuma kace a nima mana me bakin gilashi. Me yasa?"
      Banza yayi da shi yana wani aiki da yar na'urar computer din shi.
"Saboda banzan surutun ka, baka san ana bibiyar motar ka ba, banza kawai baka san kome ba sai yadda kudi yake shiga da yadda kudi yake fita."
   Shiru yayi can ya kira wani a waya, suka sake magana..sannan ya kashe wayar. Tare da cewa Fahad.
"Kashe wayar ka, wasu babin didigin layinka."
Da sauri ya kashe wayar dan Allah ya daura mishi masifar tsoro.
 ......
  Sunyi dogon tafiya kafin suka kuma haduwa da mutanen suna jiran motar su, koda suka wuce su.
  Najim ya kuma kiran abokin shi ta intanet, daga nan suka ci-gaba da tafiya, har suka haɗu da wata motar kirar sieena, anan suka tsaya tare da sauya motar baki daya, sanan suka bar wannan toyotan a gurin.
         Suna shiga wannan motar Jay ya zuba mishi ido.
"Saraki wannan kallon naka damuna yake, don Allah tambaye ni kome zan gaya maka banda wannan irin kallon."
         "Me ke faruwa?" Inji Jay,
Shiru yayi sannan yace.
"Wato abinda yake faru, duk shiri ne na dakatar da kai, karka shiga masarautan."
 Kura mishi ido yayi, sannan ya kuma mai da kan shi yana fad'in.
"Suwaye suke son ganin bayana?"
     "Akwai mutane da yawa, matsalar wasu ba a san fuskar su ba."
    "Toh taya aka yi na bar gida?" Ya kuma wurgawa Najim tambaya.
"Bamu sani ba"
Najim ya bashi amsa a takaice.
  A hankali suka shiga garin daura, tare da sauke ajiyar zuciya. Dukkan su uku suna fadin Alhamdulillahi!
     Tun kafin su isa fada Jay yake kallon garin, cikin wani irin yanayin farin ciki, ya kasa fahimtar halin da yake ciki har suka isa cikin Masarautar, wanda aka shagali.
   Tsigar jikin shi ne, ya mike sakamakon busar alkaki da kakaki da ake, tare da buga tambura.
          A hankali yake sauka daga motar bakin shi dauke da addu'ar da Manzon Allah ya bada da zaran zaka shiga cikin jama'a.
      Kallon shi ake ana faɗin.
"Lafiya d'an sarki jikan sarki! Lafiya Sarakin Asali, taka lafiya me Shehun Borno me Sarkin Musulmi, Lalle maraba da namijin duniya! Murucin kan dutse baka fito ba sai da ka shirya! Zauna lafiya d'an karamin su kuma Baban su! Lafiya Kanin Ummu Rumana Jikar Ummu Rumanah! Takawar ka dodon su.
          Barka da zuwa Magajin Izzah! Barka da zuwa Magajin masarauta! Barka da Zuwa Yayan Gimbiya Jannart Yayan Gimbiya Jannart, An gaida D'a ga Gimbiya Sarah! Takawar ka lafiya Barde namijin zaki.
          Wuwuwu ina gwani ganawa ina maji kira ga nawa, Chau namijin Giwa."
    Duk sai yaji shi kamar bai cika mutum ba, a hankali yake takawa, yayinda Najim da Fahad suke taka mishi baya, dogarai suna rike da jakkuna shi, da gudu tawo tana fadin.
"Yaya Jayyyyy!"
  Ba tare da ya ganeta ba, ya tsaya cak yana jin kiran yarinyar har cikin kwakwalwar shi, da gudu ta faɗa kan shi ya rungume ta. Fashewa tayi da kuka, tana son magana kuka yaci karfinta, sai nuna mishi hanya take tana son tayi magana takarda saboda kukan da take dakyar tace.
"Ni...ce ....Ja...nan... Kanwar ka da ka tafi ka bari, Ga Raihanah can ga Kuma Ummu can muna kewar ka"
   Rungume ta ya kuma yi yana fadin.
"Ba zan yafe masu ba! Ba zan tab'a barin hakkin hawayen ki ba..gani nan