Showing 87001 words to 90000 words out of 119109 words

Chapter 30 - MAGAJIN IZZAH! COMPLETE Writing Mai Dambu.txt

07 Aug 2025

8140

ka shiryawa yaki akan ta."

Shiru yayi bai bar Najim Amsa ba, sabida zasu shiga cikin gidan, bayan sun shiga cikin gidan, aka gaisa sai raba idanu yake ko zai ganta, amma babu ita babu labarin ta, nan yayi ta kame kame, yana wasa da Jannart din Ummin shi, dan ta kure shi tace mishi.
"Ina Khatoon? Da fatan tana lafiya"
Dakyar ya iya amsawa da cewa,
"Tana lafiya! Tace a gaishe ku!" Yana fadar haka ya mike tare da cewa zasu wuce dama sun zo wani abu ne suka ratso nan, suka shiga shashin Baabi suka gaida shi sannan suka fita, a waje ya hadu da Muhammad kanin Aanih nan Jay ya ja shi da hira dan yana sane da Muhammad yacewa Noorie yana son irin ipad ɗinta, har take gayawa Jay, yace idan ya samu lokaci zai saya mishi irin nata, aikuwa Mutumin Najim na kallon shi ya dauki Muhammad suka nufi cikin gari, acan yayi ta latsa Muhammad bayan ya saya mishi ipad din ya gaya mishi inda Addah take, nan kuwa yaron ya sake baki ya bashi labarin abinda yake ji abakin su Ummi, amma yacewa Jay.
"Hamma don Allah karka bari a san na gaya maka domin Ammihnmu hannunta zafi idan tana zaneka wallahi."

"Babu ma wanda zai ji sirrin mu." Haka ya dawo da yaron sannan Najim ya shiga motar Jay na tuka su, sai wani gudun gangancin yake musu, tunda Najim yaga haka ya fashe da dariya yana faɗin..
"Hala baka san wacece Mamah Raihanah ba ko? Allah ya bada sa'a!"
"Yayar Abbana ce ita! Sai dai nima muka baka san waye ni ba, Jini Insha Allah zan dawo maka, nan da karshen wata naje na kuma dauko Matana." Ya fada yana wani jin nishadi.

"Baka ce kome ba akan Fulani?" Najim ya tambaye shi.
"Bata da wani amfani sosai, nima ina jin ba dad'i akan riketa da nayi, amma wanda nake son ya fito yaki fitowa, shi yasa na ajiye ta, kuma naji wasu bayanai na ban mamaki, ashe kafin a haife ni Ammina tasha wahala a hannun Wani wai Shamaki tare da Dan shi Abdul, shi yasa nake son datse wanda yake saka su aiki." Shiru yayi..Najim yace mishi.
"Kasan wanda yake sasu kenan?" inji Najim.
"A'ah ban ce na san shi ba, kawai ina kintatta muryan wanda ya kirani da wayar Fahad."

"Jay! Anya baka aiki da mutanen boye!?" Inji Najim,
. Dariya yayi sannan ya isa tashan jirgin saman, ya fita da komin shi, sannan suka yi musabaha da Najim, kafin suka yi sallama.

...... Jirgin Abuja ya nima kuma Allah yasa aka samu, dan haka yana shiga ya a sauke ajiyar Zuciya, tare da fadin.
"Yan matan Saraki ga sarakinki nan zuwa gare ki." Ya sake wani kad'aitaccen murmushi, yana hango yadda zai yi wasan kura da yar tsohuwar matan shi.

.......
Sosai na sake amma bawai dan Jay baya raina bane, kawai ina jinjina yadda ya iya furtawa ya sake ni ne! Sai naji abin yayi min girma, a hankali na gama abin da zanyi na fito daga cikin dakin girkin, ina fitowa na dauki yar jakata tare da hijab dina na saka, na haura zama da sauri na gayawa Mamah zan tafi inda ta biya min ina koyan girki, dan tace.
"Ni gidana ba a zama babu abin yi, dan haka ki shiga makarantar koyan girki, zaki kara kwarewa." Kuma nasan gaskiya ta faɗa, dan Jay yana gaya min shi yana son abincin gargajiya da rana, da dare kuma ya samu tuwo kadan sai Y'ay'an itace,

Ina shiga na zauna jin tana dan faɗa, tana idarwa ta kalle ni, dan waya take.
"Har zaki tafi? Toh gashi nan Baba na ya baro Sokoto, kuma da Alamu niman ki yaje." Da sauri na dube ta, sai kuma nayi kasa da kai na.

"Ki tsaya kiyi mishi girki, gobe sai ki tafi, dan bazan bashi ke ba, sai na zabga mishi rashin mutunci, dan ko Ubanshi bai isa ya wulakanta mace ba balle shi.." Ban kuma ce mata kome ba, ta gaya min abin da zan mishi, nace toh.

Tun da na fara aiki, nake jin raina babu dad'i, kawai aikin nake har na kusan kammalawa, sannan naji muryan su,shi da Khalid, nan kuwa Mamah tayi mishi wulakancin da ya damu da kan shi, sannan tace.
"Kaci abinci kayi gaba akwai abokin Khalid yace yana sonta tunda ka saketa. Dake ka ga baiwa tana binka kana wulakanta ka, ka godewa Allah da gwiwata take ciwo, da ban san haka ba wallahi sai na baka kashi ka tambayi Ubanka shima ban kyale shi ba akan Jannart da Sarah balle kai dan banzan me idanun a tsakar ka, sai anyi magana kai ta hura hanci kai gaka mara kunya, toh ba zata koma ba kuma sai ka sake min ita na nima mata mijinta gangariya wanda ya fika a kome mara kunya, maza kaci abinci kabar min gidana"

Shiru yayi tare da saukar da kan shi, yayi ta lallashinta. Tare da gaya mata shi fa dama bai sakeni ba, kawai ya fadi haka ne ba tare da sanin shi ba, amma tayi mishi Uzuri idan ya kuma ta hukunta shi.
"Don Allah Mamah karki manta ni Maraya ne! Ki taimaka ki bani ita, wallahi bazaki kuma jin kan mu ba. Wallahi ba zan kuma b'ata miki rai ba. Don Allah ki taimaki takwaran baban naki!" Daukar matashin kujera tayi ta wulla mishi, tare da nuna shi da yatsa, sannan ta share shi. Karshe ma kin kula shi tayi tare da cigaba da abin da take yi, karshe bayan na gama jera abincin nima nayi wuccewa na d'akina na fada wanka, ina fitowa na sama shi a zaune a bakin gadon, tasowa yayi zai tab'a ni na kauce mishi.

"Amma dai kin san babu wanda baya kuskuren, sannan kuma da sani na bazan ce kina wari ba, wallahi haka ba zai kuma faru ba." Tab'e baki nayi na cigaba da gyara jikina, nan kuwa kamar Mayye yake manne min, kasa magana nayi bayan na ture shi.

"Don Allah ka kyale ni, ina dalilin wannan abin da kake min, kasan zaka dawo kana yar murya ka d'aga hannu zaka mare ni, ko Uban da ya haife ni bai dake ni ba, ga jaka an haifa maka. Toh don Allah ka rabu dani ai kace ka jima da sake ni don Allah ka bar ni na sami Yancina. Kaje Jay bana son ka, bana son ganin ka. Na gaji da damuwarka. Kayi min matan ka suyi min, ina zaune da kaine sabida kar Dangina su sami abin gorantawa a gare ni ashe kai da kanka zaka goranta, gaya min meye ban maka? Meye laifin na, ba zaka tab'a sona ba. Sabida ka fadi haka, don Allah ka sake min mara nayi fitsari, dan na hakura da gidanka koda zaka min kome ba zan koma ba"

Daga haka nayi wuccewa ta, na karasa shiryawa zan fita ya ci da zuci zai fita kallon shi nayi, sannan nace.
"Dama kazo rena min hankali ne, ba canzawa zaka yi ba! Dole na rabu da kai. Wallahi sai na baku mamaki da kanta zata dawo min dake kamar yadda ta dauke ko" A masifance ya juyo min jikin shi na rawa.

"Naga dan iskan da ya isa rab'anki domin kece numfashina. Wallahi zan aikata kome domin samunki a rayuwata! Ki daina gaya min abinda ya fito bakinki" ya faɗa min a hasale. Nima kuma na saka dariya nace..
"Sai kayi amma aure nayi shi na gama, ai bazawara sai bazawari, saurayi sai budurwa."

Sannan nayi ficewa na na bar shi a gurin. Har dare rigima muke dashi, washi gari nice na shirya musu abin karyawa ina gamawa kafin ya tashi nayi ficcewar makaranta. Amma abin dariya ina shiga motar naga ashe ba driven mu bane Jay ne.
"Tsaya na fita."
"Daga baya kenan, Yar nan. Zamu je yawon cin amarci ne, yar guzuma ta" Ya bawa motar wuta muka bar garin, bai tsaya a ko ina ba sai a suleja. Wani karamin otel ya kama duk da maganar da nake mishi tare da masifa, bai sanya ya kula ni, haka ya kama mana daki, a ciki. Ya tasani a gaba har dakin sannan ya rufe kofar.

"Ka mai dani gida! Bana son abin da kake min ka maida ni inda ka dauko ni."

Bai kula ni ba, har yayi wanka ya fito, sannan ya tawo gaba na, ya tsaya, tare da cewa..
"Yau ina son mu raba reni ne!"
Banza nayi dashi, ina cika ina batsewa, Jay ya sani a gaba tare da tsara ni, tun ina kin biye mishi, har na tafi baki ɗaya, sai da muka zube a gado na fahimci, kuskuren biye mishi, domin ya shagaltar dani da Soyayyar shi ne shiga rai.

Hmmm! Wani kayan sai Amale, babban goro sai magogin karfe, gadon hari sai fana, ramin kura sai Ƴaƴanta, a yau Jay ya isa inda bai tab'a tsammanin ba, bai tab'a kawowa zai ji haka nake ba, bai tab'a tunanin cewa Ni din Casssssss nake, sai da ya dagargaje ni dan bakin mugunta ya zata bazawarar ce da gaske mutumin yayi ta wasan kura dani, bai kyale ni ba sai da ya sami nutsuwa fiyye da tunanin shi, a nan ne ya juya yana kallon fuskana, cikin tausayawa, kamar ya mai dani cikin jikin shi ya boye ni, dan wallahi tun da yake zai iya cewa, hmm! Babu wacce yaji ya dauki dogon zango da ita kamar ni, sai kallon fuskana yake wanda ya haɗa gumi sosai. Tare da wasu siraran kwalla da nake fitarwa.

"Gaya min taya haka ya kasance?" Ban bude ido ba balle Yasaka ran zan mishi magana, sai ma kauda kai da nayi, matsa min yayi da tambayoyi kuma yana makale dani, karshe da ya bani haushi na fashe da kuka, ina ture shi, da sauri ya rabu dani, tare da bani hakuri. Abun da Jay ba yayi ya baka hakuri tab, sai gashi rana daya Ubangiji ya sauya kome.

Duk da yana juna a ran shi, ya gaza furta yanayin da yake ji sai kallona da yake yi kamar zai mai dani cikin jikin, a hankali na sauko daga gadon, na nufi ban daki, ina jin abu na sauka a tsakanin kafana.

"Fatimah!" Ya kira suna na da karfi, sabida jinin da ya gani yana bin kafana, yaso ya taimaka min, naki. Amma haka ya nace min, har muka gama wankar, ina fitowa shima ya fito, shiryawa yayi sannan ya fita. Can sai gashi da leda, har nasaka kayana na zauna ya sani na cire mishi wandon, kamar zanyi kuka.

Haka na cire, ya gama duba ni sosai, sannan yayi min alluran kashe zafi. Kafin ya dawo ya rungume ni muka kwanta. Duk da na gaji, amma ina son komawa gida. Haka yayi ta lallabani har muka yi barci ina kwance a jikin shi.

Karfe biyu na rana muna farka wanka muka yi tare da sallah, duk abin da yake min na kasa sake jiki dashi, haka ya fita ya sayo mana kaya, wasa wasa, ya shiga min wani irin salo, wanda ya sani jin wani irin tsuma sosai a raina.

Bai nemi kome ba, amma Tabbas salon shi mai tsayawa ne a rai. Na kasa magana biye mishi nake, da zaran naga zai sab'a Number, sai nayi maza na dakatar dashi. A hankali muke ta shagalin mu, har dare. Kasa hakuri nayi na mishi magana akan ya mai dani gida, cewa yayi.
"Ni ban gama amarci ba, idan na gama da kaina zan kai ki."

Haka muka kwana, washi gari ne na fadi gaskiya na, domin Jay ya biyar dani, hanyar da ya dace sai da nayi kuka wiwi, sannan ya kyale ni, muna yi wanka. A hankali nake tafiya sabida yadda nake jin jikina. Kasa wani dogon motsi nake ina zubda kwalla. Har na shirya ce min yayi.
"Idan baki daina kuka ba wallahi bazan mai dake ba." Haka naja baki na shiru. Har yanzun lokacin ya gama mulkin shi sannan ya sani a gaba muka dawo Abuja, tun a bakin kofar nake tsoron shiga sabida Mamah da fadar da zata yi...🙄😸😹 Honeymoon honeywahala
10/23/20, 10:04 AM - Ummi Tandama: *Dole ne, cin kasuwa da maƙiyi*

Ban kuma tsinkewa da Jay baya yina ba, sai da na fito matar shi ta tsare ni zata min rashin mutunci, Rumah ta dakatar da ita.
"Kina wani abu kamar Jahila! Kina hauka akan mutumin da ya kusan kare minti arba'in a cikin d'akin ta.

       Haka bai ishe ki ba? Haka bai nuna miki ita ce abin da yake bukata ba."

"Rumah! Bana son damuwa, mata ta zo muje." Ya mika mata hannu! Cikin dauki da murnan ta mika mishi hannu. Yadda ya rike ta sai da ta kalle shi.

       Suna barin shashin, ya makureta a jikin bango, tare da zare mata idanu.
"Wallahi Munih kina kure hakurina, idan na kuma ganin kin zagi Aanih sai na karya miki hannun ki. Wacce bata san ciwon kanta ba."

                  Sake ta yayi ta fadi kasa, sannan yayi wucewar shi, sashin sa. Yana shiga dakin shi ya d'aga labulen da yake kallon inda su Aanih take, a sanyayye yake kallon yadda take niman shi. Tana duba ta inda zai ɓullo amma har ta shiga cikin motar babu shi babu alamar shi.

  .... Har ta zauna ta kuma fitowa, domin gyara zama. Kamar ance ta d'aga kai ta hango shi yana kallonta, sake labulen yayi tare da juya bayan shi, ga tagar.

     ---
Tunda na gan shi yana leke na abin ya bani mamaki da al'ajabi, kawai na shiga motar tunda ba zai min amfani ba.

          Tunda muka dauko hanyar gida, na shiga damuwa sosai. Domin naga sakon Saif da ya turo min akan gashi a gaban Dangina, ya kawo ƙara na akan abinda muka mishi ni da Jay.

        Tunda naga sakon jikina yayi sanyi, na rasa yadda zan gaya mishi abin da min bai kyau min ba. Haka nayi shiru, can naji Ummi tana magana a hankali. Tare da bawa Baabi hakuri.

       Can ta kashe wayar sannan ta juyo gare Ni tace min.
"Meye amfanin abinda kika yiwa mutumin da zaki aura? Kin ja min Bankad'a  a cikin danginki. Sunce nice nake sanya ki abubuwa saboda d'an yar uwata meye yayi zafi da Mahaifinki yake min barazana akan aurena?"

  Shiru nayi tare da sunkuyar da kai na ƙasa, har muka isa sokoto.. Ummi waya take cikin harshen kanuri, ban san meke faruwa ba, amma naji Hanisah tana ce min.

        Baabi ya haɗa Ummi da Babanta ne shi yasa take ta magana tana faɗin gaskiya.. har muka shiga cikin gidan. Inda na samu yan uwan Baabi da Saif ana jiran mu, Ummi bata tsaya ba tace zata yi sallah idan zasu iya jiran mu toh.
   Tsoto ya kamani musamman da naga dangin mu baki d'aya, har da kakata Ummi.

        Bayan mun idar muka nufi inda ake tattaunawar,.ina bayan Ummi. Dake ranta ya b'aci sosai zama tayi tana kallon kowa a wajen tarr.

          "Assalamu alaikum jama'a Barkan ku, ba wani abu ya hada mu anan ba, sai magana akan abin kunyar da Fatimah take shirin aikatawa a cikin masarautan nan! Jiya da dare Saif ya kirani yana gaya min Ya kama Fatimah da D'an Sarkin daura da ita suna masha'ar su."

Ba iya Saif ba hatta ni sai da muka kalli Bana Annuwar, jikina ya dauki rawa sosai, kamar wacce aka jona min lantarki.

          Kallon Baabi nake kam shi a sunkuye, tare da kallon Saif shima na shi a sunkuye, wani irin kuka ne ya kwace min.  Na shiga rantse rantse.

        "Wallahi babu abinda ya haɗa Ni da Jay, asalima fada suka yi Saif ka fada musu gaskiya mana"

  ..shiru yayi, sannan Baba Annuwar ya shiga fadar wasu abubuwan masu daure kai da muni, wanda sam ban aikata ba, kallon Baabi nayi tare da son ganin shin ya yarda da abin da suka ce, amma yaki kallona.

       Nan kowa ya shiga fadar albarkacin bakin shi. Daga nan suka min cin mutuncin akan Jay. Juyawa da suka yi zasu zagi Jay Ummi tace musu.
"Baku isa ba! Baku haifu ba, yar ku dai ku mata fada amma duk wanda ya Kuskura ya zaga min d'a ko ya sake kazamar bakin shi akan Jalaludeen. Toh na rantse da Allah sai masarautan nan ta tashi tsaye da kafaffunta.

     Sannan kai Annuwar da kake maganar cewa Jay da Aanih suna masha'ar su, kai meye ribar tozarta d'an uwanka a gaban jama'a?

  Meye amfanin cin fuska haka, sabida yana da hakuri ko? Sabida baya fada baya kome duk abinda zaku mishi akan ta bazai tab'a cewa kome ba.

       Toh wallahi ku kiyayye abinda zai sanya shi yayi magana, kai kuma Saifullah zaka aureta ko ba zaka aureta ba?"

    Bakin shi na rawa yace.
"Zan aureta!"

      "Tashi kar na kuma ganin me kama da kai sai ranar auren ku" da sauri ya mike, yana fita ta shiga gayawa yan uwan mu magana, tare da cin mutuncin su. Kamar yadda suka yiwa Baabi, cikin izza tace musu.

"Ban da nima a cikin nima, haramun ne da sai an nimawa Jalaludeen auren yarku muga ta karshen tsiyar ku, kuma a biya sadakin da ba'a tab'a biyan wata mace da shi ba a cikin masarautan nan ba."

Korata tayi sannan ta zauna

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login