Showing 90001 words to 93000 words out of 119109 words

Chapter 31 - MAGAJIN IZZAH! COMPLETE Writing Mai Dambu.txt

07 Aug 2025

8154

tayi musu wankin babbar riga, sannan ta bar falon abin ta, tana zuwa ta amshi wayar hannu na, tare da kashewa.

   Bayan tafiyar ta, nan suka shiga fadan abin da yayi musu, har da cewa.
"Matukar  Aanih ta auri yaron nan babu mu babu ita. Taje can su kara ta, dan bazata  ja mana faduwar daraja ba, daga masarautan Zazzau ba."

                      "Hmm! Ban san me yasa Rahil take takama ba, ban san me yasa take jin ita wata ce ba, ko ce mata aka yi muma sakarkaru ne da zata zauna yana gaya mana magana, son ranta wato d'an Yar uwanta shine abin burgewa ta kare laifin shi.

        Toh Wallahi duk abinda take ji zata samu, dan.."

Shiru tayi sakamakon haÉ—a ido da suka yi da Ummi tazo gurin Baabi.
"Hajiya kenan! Da fatan na barki da ɓaɓatu! Duk ba laifi bane, amma kin san kome lalacewar gawar Giwa tafi kwando tara,"
Gaban Baabih taje suka yi magana sannan ta d'ago kanta. Mik'ewa yayi sannan ya basu hakuri da abinda ya faru.

......
.  Haka da yayi musu ya masifar d'aga musu hankali, nan suka fita daga gidan. Aka shiga yawo damu a cikin Zuri'ar mu.

   Su lallai Baabih ya min fada tare da Ummi, shi kuma bai ce komi ba, sai ma zuba ido da yayi.

    Abun ya zama rikici da ya janyo aka hanamu shiga cikin gidan kakanmu, hatta wasu abubuwan an hanamu shigar cikin shi, balle kuma irin su Suna da wasu abun.

..... Matar kanin Mamana ta haihu dan haka nayi ta rokon Baabih ya bar ni naje, ni da Hanisah. Muka tafi mun je an karb'e mu hannu bibbiyu. Muna zaune a dakin Ayyah kakanta ta gurin Mahaifiyata.

Sabirah da Hoor, suka shigo y'ay'an maza muke dasu, Baban su ke bin Mamana, suna gani na suka fara dariya tare da faÉ—in.
"Makara! Kece a gidan sunan bayan an hanaku fita sabida ana gaya muku gaskiyar da baku so?"

      "Shi yasa naga ganku cikin sanin ya kamata, zancen manyan na manyan ne, mu yara ina ruwan mu."inji Hanisah, wata irin B'oyayyen ajiyar zuciya na sauke tunawa da nayi ita din gwana ce a masifa, gyara zama nayi tare da zuba musu ido.

         "Ke karki min rashin mutunci!" Inji Sabirah.

Budar bakin Hoor tace mata.
"Ai gado ba karambani bane, abinda aka sha a non..."

   "Ni rawa gadon mai kyau ce? Wasu tasu gadon har abada ba zasu iya sakewa da mutane ba, Ni Yanzun idan Uwata ya zo nan an santa da zafi yanayinta kenan, uwar wata kuwa sai dai kaga ana tattara kome saboda dabi'ar bera gareta."

      "Kan uban can! Ni kika zaga?"  Inji Hoor!
                "Bafa zagi nayi ba, wai ina gaya miki gadon da muka yi ne, ke baki fahimtar Yaren ne."

    Ai kuwa suka fita, can sai gasu tare da dangin Mahaifiyata, suka shigo zasu dake ta, kallon su tayi sannan ta girgiza kanta, tace musu.
"Ko kunya baku ji ba, kun dibo jiki zaku wulakantata sabida an gaya muku karya da Karerayi akan yar yar uwan ku, ko tausayin rashin uwa da bata dashi baku yi. Kun zauna akan abinda aka gaya muku sabida ranku yana sosuwa da SOYAYYA da ta samu a gurin mahaifinta.

       Da yau dukiya tana dawo da mutum tabbas Hassanah Ummina zamu bada duk abinda muka mallaka daga masarautan daura har zuwa masarautan shehun Borno, tun duniya tana kwance ahalin mu suke taka rawan gani a kasar nan.

          Dukiya mun gan shi mun kuma san shi, soyayyar da Zuri'ar mu takewa Hammah Jay, ya wuce yadda kuke tsammani..akan shi kuke tsanar Mahaifiyata? Sabida son kai da son zuciya, toh ku dake ni, sabida nice nayi magana ba mareniya ba.

Ko kunya baku ji ba, ku iyaye kuna fadan abubuwan da basu dace ba akan yan uwanku, wallahi matukar Fatima ta shiga cikin Zuri'ar mahaifiyata sai kun gane cewa shi mulki da dukiya al'amarin Ubangiji ne, yau muna kallon Hammah Jay a matsayin Mahaifiyarshi ce, sabida shi daya ta bari.

   Bamu da madadinta sai shi, mahaifiyarta ta rasu ta bar muku  ita, domin idan kun tuna da ita ga madadinta sai ku mata addu'a, amma sai gashi babu wacce kuka tsana sama da ita, da yau ana mutuwa a dawo baku ji kunyar Mameeh ta dawo ta ga abinda kukewa Yar ta ba. Burin ku sunan ta ya b'aci ace sabida rashin amana mahaifinta ya gaza bata tarbiyyar da ya dace. Ku ji tsoron Allah akan zalunci da kuka mata. Allah sai yabi mata hakkin ta, karku manta akwai rayuwa akwai mutuwa.".
Daga haka ta riko hannuna zata fita ta kalli Hoor tace mata.

"Kuskuren ki tab'a min ji kimata! Shi yasa na tab'a naki, ba kare bin damu!" Daga haka muka bar gidan. Ina kuka Allah yasa ita ke jan motar dan dukkan mu Baabi ya saka an koya mana mota.

             "Nagode kanwata Kawata." Na faɗa mata cikin kuka, girgiza kai tayi sannan ta cigaba da tuka mota tana faɗin.
"Ban san me yasa baki iya karban kanki hannun mutane ba, nifa ba zanyiwa kowa kuka ba"

       "Sabida kuka da gadon taurin zuciya ba! Kuna iya boye kaunar abinda kuke so ba! Da zaki ji yadda nake son D'an uwanki da sai kin tausaya min."

  "Mun sani mana, toh ya zamu yi da dangin Baabi? Kin san Ummi ma ba sha tayi a hannun su ba, kawai tafi su baki ne. Wallahi kaf dangin Ummi babu wanda baya mutuntaki, ana ganin darajarki fiye da yadda baki zata ba, ko jiya sai Da Kaka Bana ya tambayi Hammah Jay, akan da gaske yana sonki? Yaki bashi amsa.
.da ya bashi amsa toh ina gaya miki sisin gwal ne sadakin ki.

     .ko Ni bana tsammanin zan sami sadaki sisin gwal, amma ke naji har kowa ya gama hada kome na sadakinki.. amma mara kirkin nan ya ce baya sonki."

     Lumshe idanuna nayi sabida kalmar baya sona ba sabon kalma bace da zan ji haushinta, kalmar ta jima da zame min Alakakai. Bude idanu nayi lokacin da naji ta ja burki.

          Ikrama ne ya sha gaban mu, da sauri nace.
"Ke tadda motar mu bar nan mahaukaci ne."

Sai da ta barshi ya kusan zuwa dab damu, kawai ta finciki motar da masifar gudu, ya kuma koma cikin nashi ya rufa mana.

  Da sauri na shiga lallubar Number Saif, ban san na fada kan Number Jay ba, kawai na shiga kiran shi.....

Acct: 0472282105
GTBNK Ramlat Abdulrahman Manga 300â‚? katin mtn 300 normal posting 21/October Insha Allah
Zahrahn Addah Ramlat domin nuna shaidar biya! ita za a turawa....
07035133148/ +22784506476 yan Nijar zasu iya samun A'isha Indo Nijar....
#Mai_Dambu...
10/23/20, 10:05 AM - Ummi Tandama: *_Shiru kake ji... Malam yaci shirwa_*

A hankali ya fito cikin motar ya rike hannuna muka shiga cikin gidan. Tana zaune akan daya daga cikin kujerun falon, tun da muka yi sallama ta amsa tare da  kauda kan ta.

"Shine kika bishi! Bayan ya gama tozarta ki, a gaban jama'a ya wulakantaki, sannan yace ya sake ki,
...... Idan har yana da damar da zai wulakantaki ba kowa bane ya bada damar haka sai ke! Sabida baki san Darajar kanki ba balle shi yasan naki, ya dibo jiki yazo ke kuma kika bishi wannan wani irin hauka kike yi ne da sunan so? Ka fita ka bani guri, idan na kuma ganin ka, ranka zai b'aci sosai wallahi."

"Allah ya huci zuciyar ki! Ayi min afwa amma wallahi ina son Mata ta," ya faÉ—a a sanyayye, d'ago kai nayi ina kallon shi. Ya gyada min kai. Sannan ya juya ya bar gidan. Ni kuma Mamah ta cigaba da min fada.

Daga nan gidan bai tsaya ba, ya wuce katsina, ta jirgin sama, yana sauka, ya kira Murad ya kai shi har gidan da Baba Galadima yake kakan Husnah yaba son suyi magana akan matsalar masarautar su. Daga nan suka juya zuwa cikin gidan sarautar Katsina, anan ya wuni yana ta wasu shirya shiryen yadda zai zauna gana yaƙe. Dan yana son fidda mutum na ƙarshe.

Yana zaune yaga wasu yan mata zasu wuce, daya tana cewa.
"Ina son zuwa kwatarkwashi, naga jikin Kakata Sahurah."

"Kai Aminatu! Itace wacce ta zauna a masarautar Daura ba?" Cikin jin dad'i yarinyar ta gyadawa yar uwarta kai,, har suka wuce. Sauka yayi ya shiga motar, ya nufi garin.

----
Dakyar ya same ta, koda ya isa gabanta, jan tsaki iska tayi sannan tace mishi.
"Sun nisanta ka daga Ziryana! Sun hanaka fahimtar inda matsalar take.

Sai dai kash sunyi kuskuren, domin yanzun haka kome zai iya faruwa daga zarar ita wacce take haÉ—e da rayuwarka ta mike da kafarta."

Daga nan ta shiga mishi bayanin abubuwan da suka fara da abin da ta aikata, sannan ta kuma jadadda Mishi irin abubuwan da suke faruwa da wanda zasu faru ma nan gaba, ta kuma gaya mishi dole ya nimo mutanen da suke niman rayuwar shi.

"Ko zamu tafi sauran dake?" Girgiza kai tayi sannan tace Mishi.
"Ni mahakauniya ce! Bani da karfin da zan iya kare kaina, itama Fulani da take hannun ka ba lallai ka koma ka sameta a raye domin sun shirya maka yadda baka yi tsammani ba."

Daga haka ya mik'e tsaye, sannan yace mata.
"Ni zan tafi!"
"Nagode ranka shi dad'e, kayi ƙoƙarin gano waye ki bibiyar ka!"
"Insha Allah!" Ya furta a hankali.

----
Washi gari.

Ya samu ganin Baba Galadima. Sun tattauna sosai, har ya mike zai bar gidan Baba Galadima yace mishi.
"Ka shirya niman wanda baka sani ba?" Juyawa Jay yayi sannan yace mishi.
"Yallabai tsaf na shirya niman shi, na shirya cin kaniyar shi, sai na gyara mishi zama, idan na kama shi sai na haramtawa Zuri'ar shi mulki baki daya, sai na fitina kome na shi muje zuwa."

Daga haka ya fice daga gidan..
Kai tsaye daura ya wuce abun shi.

----
Tun da ya isa, ya shiga yiwa manyan masarautan, lokaci guda ya shiga amsar duk wani abun da aka yi ba bisa ka'ida ba. Wasu abubuwan ma kawai jin su ake amma Jay ya Bankad'o su.

Ana cikin haka Allah yayi wa Ajiya rasu, take aka mai da mutuwar kan Jay, inda suka ce da hannun shi. Sai dai bai ce musu kome ba.

Yana sane amma yaki magana abin da ya kuma basu haushi yadda yasa aka kwashe kayan fadar aka kuma saka wasu, abin ya basu haushi domin a garin cire wasu abubuwan aka yi zaro layyu, da wasu abubuwan murmushi yayi sannan ya bada aka kaiwa Baba Magaji. Gefe gudakuwa Ba komai ke damun shi ba sai kewar Yar guzumar matar shi, ta tsaya mishi a rai.

Ban da yana matuƙar kunyar Mamah Raihanah ba, da yake ya dauko matar shi, amma cike yake da kewarta. Nutsuwar da ya samu da ita, ba na wasa bane shi yasa yake kuma jin lallai zai koma Abujan.

..... "Jay jiya na sami wannan takardun a hannun Baba Hashim, ya bani kuma abun mamaki sunan Galadima ne ya fito a cikin. Meye alaƙar shi da mutuwar Ajiya dan Abba ya gaya min cewa akwai matsala a tsakanin su. Kafin wannan abun ya fito." Karb'an takardan yayi sannan ya duba kana ya dube Najim yace mishi.
"A bisa binciken da nake, Galadima yana cikin magadan masarautan nan! Domin shi kakan shi na uku shine Zulum, Ziryana itace kakar Ammih na uku.

Abun da na kasa anan wancan lokacin da lokacin Ammina akan ta akayi rigimar! Wannan lokacin kuma akan wacece za ayi rigimar?"

"Eh amma, ina ganin babu mace a wannan karnin da za ayi rigimar akanta shine ya koma akan karagar mulkin ka." Inji Najim,

"Nima na fahimci haka,"

Shiru yayi sannan ya cigaba da dube dube, har zuwa lokacin da suka bar fadar.

.....
"Fulani! Dama ina son muyi tsayayyar magana. Waye ya.."
.
"Jalal ban san kome ba!" Ta gaya mishi haka tare da kauda kanta, dan dole ya hakura ya fita, yana shiga gidan shi, ana kiran shi a waya yazo ga shi an shigo an kashe fulani.

Wannan tashin hankali yayi matukar tasiri akan shi, yasan suna fakon mutanen da yake zargi ne, shi yasa.

Haka ya isa yaga irin kisan da aka mata, sawa yayi a kama masu kula da kofar ta, yayi ta azabtar dasu, har sai sunyi magana.

.... Kusan mutane goma, aka yi ta basu wahala, kuma sun kafe basu bane.

---
Tun ranar da ya dawo dani, nake yawan mafarkin gani cikin jajjayen kaya, hannuna da kafana cikin jini ysna zuba. Kaina kuwa wani irin kambun jan zinariya ce, me katon tagulla a gaban kambu.

Yau kam ina zaune naga suna jan wani mutum, duba shi nayi naga Jay ne, anje an saka kan shi a saman katako, wani kato ya d'aga adda zai sare shi na fasa kara na farka.

Cikin tsoro na duba naga karfe biyu na dare ne, a hankali na sauka naje nayi fitsari na dawo na kwanta, a sannu barci yayi gaba dani.

---
Washi gari ina fitowa Mamah Raihanah take gaya min abin dake faruwa. Yaki sauraron kowa . Dan haka ina son nace mata ko zamu tafi can ne ina tsoron kar ta ce na cika damuwa da shi. Juyawa nayi zan fita tace min.

"Fatimah! Jay yana bukatar me taimako, barcin da kike yaci ace kin farka, ki taimake mu mana."
.kallonta nayi sannan nace mata.
"Insha Allah, zan tsaya mishi."
Daga haka nasa kai zan fita tace min.
"Ki shirya muje."

Kaina a sunkuye na gyad'a mata kai, sannan na koma d'akina nayi wanka na shirya, bamu bar Abuja ba sai karfe hudu, koda muka iso yana can gidan horo yaki fitowa. Matsawa Najim nayi ya kai ni har bakin kofar shiga cikin gidan.

Da sauri na shiga, na same shi a tsaye ya juya musu baya, ana ta zane mutanen.
"Ku dakata!" Na faÉ—a musu.
"Ranka shi dad'e! Meye amfanin haka?" A fusace ya juyo min. Tare da zuba min ido, tattare alkyabar jikina nayi na isa gaban shi, cikin damuwa nace mishi..
"Kazo muje kaci abinci."

"Taya? Ya kike son nayi? Ya zanyi da jinin da ake zubdawa ba bisa ka'ida ba?" Ya faÉ—a min a tsawace.
"Amma bayyana fushin ka, kasawa ce! Taya zaka biyewa mutane kana aikata kuskure talakawan kane fa! Kuma mutanen ka da ka yarda dasu don Allah kazo muje, taya za'a ce babu wanda zai dakatar da Kai."

Rigima sosai muka yi kafin ya riko hannuna a fusace, ya nufi cikin gidan sarautar bai zame ko ina ba sai a fadar shi, ya juyar dani yana faÉ—in.
"Kalli kujeran da ake zubda jini sabida dashi, ki duba ki gani sabida wannan ake kashe masu yunkurin gaya min meke faruwa, ya kike so nayi?" Naushi ya kaiwa bango Ya fita hayacin sa, sai illata kan shi yake.

A tsorace na shiga ƙoƙarin rike shi, kamar mara hankali haka yayi ta jima kan shi ciwo, yana yi yana faɗin.

"Sun meye ke damun su? Meye nayi musu, da basu son a fadi gaskiya, yau sati Uku da dawowa daga gurin ki, kin san yadda nake rayuwa kuwa, abu daya ya gaggara, sun Kashe Ajiya. Sunce ni ne, jiya na shiga gurin Fulani Hasiyah sun bi sahu sun kasheta meye nayi musu da zafi?"

Ya faÉ—a da karfi, cikin wani irin tausayi shi, na mike a hankali na isa gurin da yake ta dukar bangon na riko hannun shi, zan hana shi, juyawar da zai yi ya ture ni, Allah ya takaita ban fadi akan kome ba sai akan karagar mulkin masarautan. Mik'ewa zanyi naji kamar an mai dani, cikin kujeran da karfin tsiya.

Wani abu da bazan iya cewa gashi ba, yana bin jikina da mugun gudu, wanda yafi na fitar numfashi.

A hankali mafarkan da nake yi, ya shiga dawo min. Ji wani abu nayi yana haura min saman kaina, a hankali nake jin kamar ba dai-dai nake ba, ihun mutane da Hayaniyar dawakai suna kara kusanto ni. A sannu nake jin duniyar tana juya min, kome yana zuwa min daki da daki. Tun daga wasu karni har zuwa karnin goma sha tara, izuwa yanzun da kome yake faruwa.(wato tun daga karnin Ziryana zuwa karnin kwarkwarah)

Karan bushe bushen algaitu, nake ji. Tare da ganguna, a hankali na bude idanuna da suka rine zuwa jini, wani irin dakiyar zuciya nake ji, bana jin kome akan kowa musamman da na bude idanu naga wasu irin mutane sunyi sahu a gabana. Sannan suka dunkule hannun su, suka saka a gefen kirjin su na dama.

Sannan suka zube a gabana alamun girmamawa.
"Muna maraba da Sarauniya Aanih Fatimah Khatoon! Sarauniya ta hudu daga cikin al'ummar bani Adam! Kuma Matar korarren Sarkin mu, Jalaludeen Jamaluddin! Muna jiran cewar ki, domin isar da umarnin ki! Ranki shi dad'e shekaru dari uku da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login