Showing 57001 words to 60000 words out of 119109 words

Chapter 20 - MAGAJIN IZZAH! COMPLETE Writing Mai Dambu.txt

07 Aug 2025

5473

ba rawaya ba. Kafin ya koma fari.

        "Lallai zaki mutu! Domin kuwa kina dab da zama fanko. Ki biyo ni domin kuwa ni ce bazan tab'a."
           "Fatimah!" Naji muryan Saif wani irin ajiyar zuciya na sauke tare da juyawa gare shi, ya ganin idanuna cike da kwalla ya kara leka inda na juya babu kowa, nima juyawa nayi babu matar babu dalilinta.

"Zo mu tafi!" Ya ce min.

     A hankali na isa gaban motar ya bude min na shiga tare da zama sannan ya rufe, ya dawo inda yake ya zauna sannan yaja mu. Kallona yayi sannan yace min.
"Ina ji a jikina kamar bazan same ki ba"

             "Hmmm!" Nace mishi,
"Zahrah!" Ya kira suna na a sanyayye.
"Ina sonki" juya kaina nayi sannan nace mishi.

" bai zama lallai na maida maka abin da ka bani. Amma ina mutunta duk wani alamarin ka."

     "Aanih ko dole nayi Miki ne?"

      Juya kaina nayi tare da kallon farce na, ina tuna lokacin da Jay ya sace ni, har ya mai dani dakin shi, na tab'a farkawa naga yana kallon zanen fulawar hannuna, tare shafawa. Koda na farka b'ata rai yayi sannan tare da barin d'akin.

    Yau ma sai da na saka aka min zanen lallen dake ja ne, kai hannun Sa'id yayi tare da shafa hannun, cikin jin haushi na harare shi. Sannan nayi fiki-fiki zan mishi masifa ya zuba min ido, karshe tamke fuska nayi cikin b'acin rai, har muka isa gida.

            Hannuna na kai domin bude kofar motar yace min.
"Ai ko babu kome zaki min sallama ko Zahrah?"

       "Sai anjima!"nace mishi a dakile, ya fahimci naji haushin abinda yayi min ne yasani jin ba dad'i.
"Toh kiyi hakuri bazan kuma." Ya faÉ—a min a sanyayye, zuba mishi ido nayi naga ya wani narke min.

   Sai ya bani tausayi, na sake murmushi nace mishi.
"Wannan satin zan shiga sokoto"
"Na sani ai shi yasa nake ta tambayarki."
         "Toh ba damuwa zan zo can."
      Daga hakan na juya cikin gida, shi kuma yayi tafiyar shi.

    .....--
Kwanan Jay biyar a Maiduguri, har da sarautar Yariman mai Borno aka bashi, sannan ya dawo inda ya narkewa Abban shi akan gina mishi asibiti, da farko Jaamal yaki amma ganin sam Jay bai san meye ake kira da mulki ba, yasa Baba Sarki yace a barshi Nan da wani lokaci.

...... Zaune yake suna cin abinci, kamar wanda aka zage shi sai cika yake yana batsewa,  Kallon Juna Sarah da Jaamal suka yi kowa ya d'aga kafada, sanan suka ci gaba da cin abincin su rai a sake.
  Ture abincin yayi alamun ya koshi kuma ko rabi bai yi ba, ya zubawa Sarah Ido cikin nasara yace.
"Mama! Dama wancan Yarinyar aure zata yi?!" Kallon mamaki suke mishi tare da tambayar.
"Wacce Y'a kenan?"

    Shiru yayi abin shi bai kuma magana ba, har ya mike, Jaamal yace mishi.
"Ya zaka mai da kowa sa'anka!? Wannan rashin girmamawa ba daga cikin ahalin gidan mu bane ko na mahaifiyarka."

.mik'ewa Jaamal yayi yazo gaban shi ya tsaya suna fuskar ta juna.
"Jannart har ta koma ga mahaliccin ta, bata tab'a banzarta da Aminiyarta ba, duk wani abu da zata yi cikin mutunta Sarah. Jannart ta hakura da rayuwarta sabida Sarah kai har ka isa tayi maka magana kayi banza da Ita?

   Zan dauki kome amma ban da...."

        "Nagode sosai Kawu, ka nuna mishi bani ce na haife shi ba, ka nuna min cewa ba."
  D'aga mata hannu yayi sannan ya juya ya bar falon, a sanyayye ya bar falon har zai shige shashin sa, ya juya tare da cewa Jay.
"Idan har zaman ka zai janyo min fitina da Iyalina na roke ka da ka fita ka koma inda ka fito.

                 Ban haifi d'an da zai tozarta ni a gaban jama'a ba, kana da damar kayi kome, amma ban da wulakanta min mata na ba."

         Yana gama fadar haka ya wuce dakin shi, ya zauna a bakin gado tare da zubawa hoton Jannart ido, yana jin babu dadi a ran shi.

     ... Shiru Sarah tayi tana me share kwalla, sannan ta kalli yaron, tare da mika mishi hannu, dawowa yayi ya zauna a kujeran kusa da ita, yace.
"Kiyi hakuri Mama!"

"Babu komai!" Ta faÉ—a a sanyayye, dan ta lura miskilancin da Jay yake halayyar Jannart ce, rashin magana da kafiya da naci halin Jaamal ne.
"Wacce yarinya ce ake maganar ta?". Tab'e baki yayi sannan yace.
"Wancan yarinyar ta sokoto!"

     "Fatimah ce yarinyar? Jay ka cika renin hankali, Fatimah ba yarinya bace, ba kuma sa'arka bace, Sa'ar Aliyah ce, don ka ganta kamar lomar tuwo."

                   Shafa kan shi yayi kamar bai ji haushin ce mishi ba yarinya bace.
"Mamah yarinya ce ai."

"Hmm! Yayi maka kyau! Tunda ka haife ta ba?"
"Me yasa bazaki bata shawara ta hakura da auren ba."

Yana fadar haka ya mike yana dariya, sakamakon kallon da take mishi.
           "Toh bamu bata shawara ba sai ka dauki mataki ko?!" Ta gaya mishi a fusace, dan ya fara bata haushi.
"Afuwa! Amma ki duba dakyau, ta sanadin auren maza ke mutuwa me zai hana ta hakura, koda yake tsugune bata kare ba, tunda."
."amma me yasa da aka ce ka aureta kace baka sonta?" Ta tambaye shi,

    "Nifa bana da ra'ayin bazawara ce! Kawai nafi son wacce bata kai ashirin zuwa da daya, sunyi hankali, amma ita fa? Tab."

Baki sake Sarah ke kallon shi tana gyada kan ta, kafin tace mishi.
"Allah ya kawo maka sauki cikin abubuwan ka".

Dariya yayi, tare da barin shashinta, ya nufi hanyar da zata kai shi cikin gidan, haduwa suka yi da Husnah. Ta tsura mishi ido, babu kyaftawa tace.
"Yarima Jalal, Barka da maraici."
   Watsar da ita tayi tare da tsuke fuska, kamar bada shi take ba.

Shan gaban shi tayi tare da tsare hanyar da zai kai shi shi cikin gidan.

       "Yarima Jay! Meye laifina, ban fi guzuma da buzuwar da aka had'a ku b..."

Take mata kafa yayi tasaka kara me shegen karfi wanda yasaka dogaran da suke kofar farko lekowa ganin shugaban su yasa su juyawa da sauri,suna fadin.
"Hutawarka lafiya magajin garin daura!" Murmushin ban haushi yayi wanda ya kuma bashi damar mutsuke kafar Husnah tana kuka.

             "Buzuwar bata da matsala domin zata iya karban kanta."
D'ago fuskarta yayi wanda ya jike da kwalla, ya cigaba da cewa.
"Koda wasa kika tab'a Lu'lu'ah sai na baki mamaki."

    Daga haka yayi wucewar shi cikin gida, inda ya samu Kakar shi ta dama mishi fura tare da gasasun zabbi.

    Zama yayi ya sha sosai ya kuma ci zabbin.

    ---
Shiga shashin sa tayi taga Balkisu tana fitowa rai a b'ace.

      "Aikin banza kiba a kunne! Mun san kome, matar cushe." Inji Balkisu.

   Dariya Sarah tayi sannan tace.
"Banza ba shi kai zomo kasuwa. Ko baki fada min ba, nasan kwanan zancen Balkisu."

           "Oho dai koma me zaki ce sai dai ki fada. Kowa ya ga shamuwa da kwushinta ya ganta haka zaki ganin ki bar ni. Sannan shi Yarima da kike takama dashi ai ba d'anki bane? Dan haka ki bar ganin karenki ya kama kura, da sannu zan mai dake abin kwatance."

        "Asha Ramanme kada mai kibba. Allah daya gari banban, ranki shi dad'e, zan shige dan ina da abinyi."

               Daga haka tayi wucewarta, bata kuma tankawa ba.

          ---
"Ina lauya ne? Ban gane shi ba kwana biyu?"  Inji Baba Sarki.
Gyara zama Jay yayi sannan ya shiga matsawa kakan shi kafar shi da take ciwo.
"Wai yana da aiyuka ne."

         Daga haka ya cigaba da abin da yaƙe, har zuwa lokacin da Kakan yace Mishi ya isa.
....
"Jalal! Har yanzun kana kan bakanka baka son FaÉ—imah?"

   Lashe bakin shi yayi sannan ya zubawa kasa ido.
"Kaka Ni bana sonta ne? Kuma bazawara ce"

          Shiru falon yayi sakamakon bayanin da Jay yayi,
"Allah ya sa haka shine mafi alkhairi."

         .....
Ta same shi tsaye ya zubawa hoton Jannart.
"Kawu!" Ta kira sunan shi a hankali bayan ta rungume shi ta baya.

       Ajiyar zuciya ya sauke, tare da cewa.
"Na rasa inda Jalal ya dauko rashin hankali, Jannart bata da matsala, amma shi ga baki daya ba tarbiyyar mu yake nuna mana ba.

       Yayi min wannan rashin girmamawan a gaban mutane, naji ba dad'i, mu iyaye ne. Kome lalacewar muna bukatar mutumtaka, balle kuma yadda muka kasance ahalin babban gida."

        "Karka ga laifin shi banbancin al'adun da dabi'un mu ya sha banban da na shi, halayyar shi ba daya bane da wanda ya fito cikin babban gida.
Banda zanen kaddarar mu ta shafe shi ai da a cikin mu zai taso da irin namu AL'ADUN, toh Matsalar da aka samu ya taso da aladun wasu ne, Insha Allah bazai kuma ba."

       "Toh me yasa baya magana?" Ya tambaye ta a sanyayye.
"Amma inji ka ko? Domin kuwa ban ga wani rashin maganar shi, kai ma haka kake da wannan wulakancin, sannan kuma Janny. Itama ai ba tayar baya bace gurin miskilancin da zurfin ciki.

     Kai kuma naci da kafiya, shi yasa banyi mamaki ba da aka ce min ya sace Fatimah, domin kuwa tayi mishi laifi kuma ya rama."
     Juyawa yayi yana kallon fuskarta, tare da sake murmushi yana cewa.
"Wacce yarinya ce yake maganar ta?!"

...... Dariya tayi sannan ta gaya mishi ai da Fatimah yaƙe.

Zaro ido tayi waje, yana faÉ—in.
"Yau naga abin mamaki! Ba cewa yayi baya sonta ba??"

       Dariya tayi tana fadin.
"Kamar kumbo kamar kure!"

     .........
Yana fitowa daga cikin gidan, ya dauki wayar shi ya latsa can ya manna a kunnen shi.....
Acct: 0472282105
GTBNK Ramlat Abdulrahman Manga 300â‚? katin mtn 300 normal posting 21/October Insha Allah
Zahrahn Addah Ramlat domin nuna shaidar biya! ita za a turawa....
07035133148/ +22784506476 yan Nijar zasu iya samun A'isha Indo Nijar....
#Mai_Dambu
              
10/23/20, 9:57 AM - Ummi Tandama: *Kowa ya rena tsayuwar.... Wata ya hau ya gyara*

"Zan ga yadda za ayi da.."
Katse shi tayi cikin jin haushi.
"Ba zaka fita hanyata ba? Ba zaka dai min shishigi kwala kai a faranti ba"

"Ke da wa kike?".kashe wayar tayi abinta. Shafa fuskar shi yayi cikin jin dadi, ko babu kome yasa ta tayi magana, da muryanta irinta yaran nan. Tsaki yayi tare da fada a ran shi.
"Zai ga uban da zai aura mata wancan mutumin."

      Yaja tsaki tare da barin guri .

    ---
Tunda na shirya kayana, nake kallon su jikina yana kara sanyi, sabida faduwar gaban da nake ji. Haka na fito ina kallon Aunty Aina'uh, na kakaro murmushin dole.

                 "Yau kam zaki koma gida, sai murna kike kamar kin zauna akan ƙasa!" Inji Aina'uh,

Tab'e baki nayi tare da fita waje, ina faÉ—in.
"Baki kuma gani Nana gidan ki sai nazo da mijina."

     Zaro ido tayi waje, na d'aga mata gira, a hankali tayi min fatan Alkhairi, sannan na shiga mota, tunda muka isa Airport naga kamar ana bina, ban damu ba, kawai na tsinci kaina da turawa Saif sakon karta Kwana.

        _Bam san waye ba! Amma yana bina, kuma ban yarda da shi ba_

    Bayan kamar minti biyar, sai ga kiran shi.
Sai ga kiran shi, ya shigo min tare da cewa.
"Kamar ya baki san shi ba? Zai biki, ki gayawa yan sandan da suke gurin zasu taimaka miki da wani abu."

                   Ban ce mishi kome ba, dan koda na juya ban ga mutumin ba, haka muka taso ina duba shi ban gan shi ba, har muka iso sokoto, kafin tashi na hango shi tsaye yana kallona, tsoro ne ya kuma kamani, garin na turawa Saif sako, ashe wai Jay na turawa.

         _Don Allah kayi wani abu kaji sace ni zasu yi gashi nan yana shirin tawowa inda nake don Allah kayi wani abu_

          Fita mutumin. Yayi nima na fita, koda na iso inda za a zo dauka na, kawai naji an watsa min abu a jikina, ina dubawa naga madara, dan haka na juya da sauri na nufi ban daki domin na goge jikina, ina shiga kaina a sunkuye, kamar ance na d'ago kawai naji an toshe min bakina da hancina, shaƙar hodar bilis nayi ban  kuma sanin abin da ya faru ba.

       Sauke numfashi Asood yayi tare da sanya min nikkaf ya fito dani a hankali har inda suka ajiye motar su.

             ----
Yana aiki da laptop din shi ne ya ga sakona,kamar bazai bude ba kawai ya buÉ—e.
Sharewa yayi ya cigaba da abin da yake can yaji zuciyar shi tana girgiza, gwada kiran layin yayi. Ta katse, ya kuma kira ta katse.

       Saka smart watch din da yake hade da wayar hannnta yayi ya shiga ƙoƙarin gano ainiyin inda take, bai samu nasarar gano kome ba, amma wayar tana airport.

    Mik'ewa yayi a hankali ya shirya cikin kananun kaya, bakakke, sannan ya dauki duk wani abin da yake bukata, yana fitowa ya kira Najim.
"Duk abin da kake mu hadu yanzun nan zaka kai ni tashar jirgin sama"

   Fitowan yayi har falo ya sami Mamah bayan sun gaisa da Mamah yace mata.
"Bari na dan fita bazan jima ba Insha Allah."

             "Ubangiji ya tsare, ya kare ka da kariyar shi. Allah ya dawo da kai lafiya!"
"Amin Ya Allah! Nagode sosai Mamah na!" Daga haka ya fita. Ya sami Najim yana jiran shin. Koda ya shiga yayi ƙoƙarin tambayar shi inda za shi amma yayi banza da shi.

        Tun da suka fita yake tsaki yana ce Mishi ya tsaya yayi musaya shi ya dawo gurin zaman shi Najim yaki tare da cewa.
"Wa? Ni zaka kashe wallahi ban isa ba"

   Dan haka ya kara gudu sosai, kamar zasu tashi sama, Allah ne ya kai su airport yana zuwa dakyar aka sami jirgin da zai isa sokoto, sabida sun  gama diban fasinja.

        Ji yaƙe kamar ya riga jirgin isa Sokoto, koda suka isa abin da ya fara shine kiran layinta da yake cikin airport din, haka ya isa ya samu suna, ana niman ta sabida kayanta da aka gani. Nan ya gaya musu abin ta tura mishi.

  Nan aka nimo yan sandan, tare da danginta, Baabi ne ya zo, bayan an mishi tambayoyi ya tabbatar da sunyi magana da ita.

     Kallon Jay yayi cikin nutsuwa yace mishi.
"Kai kace ta tura maka sako?!"  Nuna mishi wayar yayi sannan ya ce.
"Ban san a akayi ba amma Tabbas ta turo min sakon, kuma wayar har yanzun a bude take."

         Nan aka kuma gwada kiran wayar tana karar, dan haka aka shiga tambayar mutane, wani ne yace yaga wucewar ta ban daki daga nan bai ga fitar ta ba, sai wani mutum rungume da wata mata me sanye da nikkaf.

              Shiru Jay yayi da a rikice ya shige ban dakin, wayarta ya shiga kira. Can yaji "ziiiimmm"

Yana dubawa yaga wayar ce a kasa, da sauri ya É—auka, tare da duba wayar akwai ki.

Goge fuskar wayar yayi bayan ya fito, ya tsaya yana gwada budewa.

          Duk taki buɗewa, dole ya haɗa da agogon hannun shi ya shiga niman yadda take cire key din wayar.

             Yana sakawa kuwa, wayar ta buɗe. A hankali ya shiga bin sakon wayar har idanun shi ya sauka akan sakon da Ikrama ya tura mata. Da cewa.
_Yadda Mahaifinki ya hanani aurenki haka nima sai na lalata miki roman ki_

Sai sakon Asood da ya tura mata,
_Kamar yadda kika ki amincewa da ni! Haka kina ji kina gani zan,,,, karasa abinda wancan jahilin yayi miki wato Jay_

       Kallon sakon yayi lokacin kusan daya suka turo mata, fitowa yayi ya sami Baabi ya ja shi gefe suka yi magana, sannan Jay na zuwa ya sallami yan sandan, da wani abu aka kashe maganar.

    Sannan ya dauki kayanta, suka nufi gida da Baabi, ya kalli Baabi kadan sannan yace mishi.

"Baabih, kasan me yasa nace kar yan sanda su shiga Maganar?!"

   Girgiza kai yayi yana jiran ta cewar Jay.
"Sabida darajarta! Sabida wnada zata aura, bai dace ace sunan ta yana b'aci ba, sabida faduwar kimarta. Idan aka bar abun a rufe babu wanda zai tab'a sani, sannan Insha Allah nan da awa goma zan dawo maka da ita, kaga maganar aure ba abin wasa bane.

               Dan haka Insha Allah zan dawo da ita!"

  ..... Har cikin gidan ya ajiye baabi, sannan ya cewa driven yazo ya raka shi, suna fita. Duk wani inda ake harkan banza sai da Jay yayi, kan shi ya kulle.
.a karon farko da yaji yana son Hikmi ya taya shi aiki. Ya kira shi ya gaya mishi.

       Sannan ya tura mishi sakon Number Asood da Ikrama, bayan wani lokaci ya turo mishi inda a suke tare da Asood a guri guda, har da tasiwerar gurin.

            Kamar mahaukaci haka ya finciki motar.
        ---
Lokacin da aka kaini inda suke, wurgani suka yi, sannan fita.

          Ruwa suka, watsa min me shegen sanyi, sannan  Ikrama yazo ya tsaya a kaina, tsare da zuba min ido.

    Nan ya saka hannun shi, ya gaya min rigar jikina, dake har zuwa lokacin ban farka dai dai ba.

    Haka suka yi ta, tozartani ba tare da na san abin da ke faruwa ba.
               Har kusan karfe bakwai na dare, ina yashe a kasa, kafin Asood ya taso ya fara kokarin tsinka bra din jikina, lokacin na bude idanuna da suka min nauyi dakyar na had'iye yawun baki na nace mishi.
"Don Allah karka min abin da, zai wulakanta ni!"

         

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login