Showing 108001 words to 111000 words out of 119109 words
Chapter 37 - MAGAJIN IZZAH! COMPLETE Writing Mai Dambu.txt
Kura mata ido nayi sannan na rufe jikina. Muka tafi a hankali duk kofar da muka wuce sai masu tsaron kofar sun zube kasa. Wata ƙatuwar Fada muka isa. Inda ake ta muhawara tsakanin manyan Fadar..
"Taya zaku ce bil Adam ne zata mulke mu! Bayan bata da alaka na jini da masarautar Dafur? Idan an bawa Sarauniya ZIRYA damar zama sarauniya sabida ruwa biyu ke yawo a jikinta, Aanih Fatimah Khatoon kuma wacece ita? Bama bukatar bil Adam a cikin daular mu, domin zata iya zab'ar son zuciyarta sama da al'ummar ta. Idan kuma kuka dage sai ita Toh Tabbas zamu bukaci a sare mana kan Yarima Jalal! Shine Yarima na goma sha biyar dake bin bayan Aanih Fatimah Khatoon! Sarauniyar zubda jini! Yayi muku ko kuma me zaku ce!"
"Ba za a kashe Jalal ba! Amma kuma ni zan rike Aanih Fatimah Khatoon! Ziryana Burbasa Fairo..... Chaiiii 🤦🏽♀️?
10/23/20, 10:10 AM - Ummi Tandama: *_Banza ta kori wofi_*
"Itace zata ta rike abin da na kasa! Itace zata iya abin da banyi ba, dan haka kar naji wani yace bil Adam bazai iya ba, ina kuka kai rashin imani irin na d'an adam!? Ina kuka kai rashin tausayin irin ta d'an adam!....
Shiru Aanih tayi sannan ta cigaba da cewa.
"Zata iya! Tabbas zata iya! Nasan zata iya!." Tun tana fada da karfi har ta daina karshe na zuba a gurin ina kiran "Jay!!!" Kafin wani irin barci ya dauke ni.
"Bazlah ai sai ki maida ta, d'akinta." Sunkuyar da kai tayi cikin girmamawa tace.
"Ya shugabana ina niman Alfarmar ko za a maida ita gurin mijinta, inda yaso sai ayi ta bude mata idanu, amma ku duba Alamarin da idanun basira!"
... "Wannan maganar ki gaskiya ne, a maida da ta a dawo da bazirqa!" Gyad'a mishi kai tayi cikin girmamawa, sannan ta dafa goshina tayi wasu kalamai sai ga mu a cikin d'akina, a kan gado ta kwantar dani, sannan ta shafa cikina tana faɗin. Yana yin bai nuna akwai wani abu a tare da ita ba da zai tabbatar musu da ciki ne da ita..
A hankali take shafa kai na, sannan tace.
"Mun barki lafiya! Sarauniyar mu!" Daga nan suka b'ace baki abin su.
......... Farkawa Jay yayi ya ganni kwance, dan d'azun dake bazirqa ce, yayi juyin duniyar nan tazo ta kwanta, amma fir taki. Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya shafi fuskana, tare da shigewa jikina yayi tare da gyara min kwanciya, a jikin shi. Bayan yayi fatali da rigar jikina.
Da asuba, muka farka kunna wutar gadon yayi tare da leka fuskana, ya duba agogon gefen gadon, huɗu da minti biyar. Shigewa yayi jikina sosai yana kallona, tare da kallon yadda nake yatsina fuska, a hankali yake bin ilahirin jikina, har ya kai na ture hannun shi. Tare da zuba mishi ido.
"Aanihhhhhhhh! Don Allah karki min horo da hakkina." Yadda ya kira suna ya sani jin wani irin. Shiru nayi tare da lumshe idanu na..
Ina jin shi yana kidar shi, har zuwa lokacin da ya samu nutsuwa dani, gumi nake zubawa. Sabida turmushe da yayi. Gyara min kwanciya yayi tare da shafa kaina, a sannu na mike tare da barin gadon nayi wanka da alola tsaf sannan na fito.
Kallona yayi tare da isowa gabana ya zuba min ido, kauda kaina nayi, na wuce na shiga niman kayana na saka, sannan na gabatar da sallar nafilla, shima yana fitowa ya nufi masalacin.
.........bai shigo ba sai karfe bakwai saura, yana zuwa bai ce min kome ba, yaja alluran da ya shigo dashi ya kalle ni ba tare da yace min kome ba, ya koma ta baya na zai min sai lokacin nace mishi.
"Karka fara dan bana so!"
Bai kula ni ba, ya min alluran. Sannan ya fita ya bar ni a gurin. Har dakin shi ya koma ya shirya, kafin ya dawo har barci yayi gaba dani, bai tsaya yayi feccewar shi. Sai gurin karfe biyu na rana ya dawo ya samu na farka, ina zauna akan abin sallah. Mika min kunun gyada yayi wanda ya amso min daga cikin gidan. A hankali na ke sha. Kallona yayi sannan yace min.
"Meye matsalar ki? Bana son shirun nan."
Kallon shi nayi na wasu lokuta, kafin na sunkuyar da kaina kasa.
"Jay! Kawai ina hango tarin banbancin dake tsakanin mu ne!"
"Kamar Ya?" Murmushi nayi me ciwo, sannan nace mishi.
"Kawai ina jin ba zan yi nisan kwana bane! Domin nasan dole zan rabu da kai. Akwai mutanen da suke son ganin bayan ka! Amma yanzun ba zasu iya ba.
Ban sani ba, amma ina da tabbacin, wani zai zo da tuhumar laifin, idan suka zo ka basu wannan."
Karba yayi yana kallona baki sake, sannan zai magana na d'aga mishi hannu.
"Mutanen da ake hukuntawa basu da laifi! Mai Baya cikin masarautar, sannan wanda yayi laifin yana cikin masarautan.
Ga wannan shima ka bawa Habu!"
Daga haka na ajiye kofin kunun, na zuba mishi ido.
"Jay! Duk abin da zaka yi ka tabbatar da gaskiyar, domin gaskiya bata karewa, amma karya tana karewa a duniya, don Allah karka.."
Tashi yayi tare da barin d'akin, jikin shi a sanyayye, yana son Aanih amma tsoron kar wani abu ya same ta shine burin shi, lumshe idanunshi yayi can ya kuma dawowa ya dame ni a kwance.
Karb'an kofin yayi ya kalle ni, ajiyar zuciya ya sauke, ganin yadda nake barci, ciro Alluran yayi ya min, sannan ya fita daga dakin.
Cikin barci na farka sabida ciwon ciki, a hankali na nemi tashi zaune na kasa sabida jikina yayi min nauyi, idan ban ƙaryata kaina ba, kamar abu ne ke zuba a jiki, ina cikin wannan tunanin sai gashi ya shigo ganin halin da nake ciki ya sa shi sauke ajiyar zuciya, sannan ya taimaka min bayan yayi min wani allura, ya taimaka min nayi wanka, sannan ya hadu min ruwan zafi nasha, sannan ya bani magani, sai da ya tabbatar nayi barci kafin ya fita.
Wanke kayan da ta bata yayi sannan ya dauki kayan cikin ta Yar karamar wando da dan kamfen ta ya zuba a wani baƙin leda ya haƙƙa rami ya jefa, sannan ya dawo cikin gida, ya gyara ko ina, yana aiki Zancen da suka yi da Baba Magaji na dawo mishi.
"Toh baba taya zamu kare lafiyarta da rayuwarta? Wallahi tausayi take bani!"
Girgiza mishi kai yayi sannan yace.
"Hanya daya! Kar ka bari ciki ya shiga jikinta, tunda suka fara bayyana ta sanadin zama a kujeran toh karshe idan suka fahimci zamu raba ta dasu, zasu shiga niman daukarta ko kuma su kashe mu baki daya."
"Ba dai har da ita ba?"
"Eh toh idan ta kama haka za su iya aikawa" jikin Shi ne yayi sanyi, dan haka yana barin masalacin, sai da yaje ya sayo alkura. Yayi mata nafarko, kuma bata tambaye shi ba.
Ajiyar zuciya ya sauke, sannan ya cigaba da zama a d'akin ta, yana zaune yaji motsin mutum a saman yana lek'awa ya hango Munih yayi dan haka ya share ta, ya cigaba da zaman shi a d'akin..
---
Washi gari..
Da taimakon Husnah ya shirya, ya fita. Ina kwancen naga kamar ana shigowa da fita a saman kuma da gudu ake kome.
"Waye?!" Na daka tsawa, cak aka kuma daina, sannan nayi kwanciya na, ina kwance kawai na kuma jin wannan gudun, zanyi magana aka ce min.
"Kee ƙamar mara kunya! Yau..."
Kwala ihu aka yi, barci ne yayi gaba dani, bud'e idanuna nayi na ganni a zaune. Samar kujeran.
"Wayyo mun tuba!!"
"Ranki shi dad'e wannan shine gulab, ranki shi dad'e! Me zamu mishi?"
Kauda kai nayi nace.
"Ku Azabtar dashi mafi muni? Karku sassauta mishi, har sai ya fadi suwaye suka aiko shi."
Daga haka na mike zan bar gurin, kamar wacce aka yasha a barci haka na bude idanuna akan wayata da take haske. Dauka nayi tare da sakawa a kunne.
"Aanih! Kamar yadda kike ce Habu ya amshi zoben shi da wannan igiyar, toh ku kai shi inda zai baku bayani a nutse domin kuwa yana cewa zai magana a gurin sai gawar shi, Habu yayi muku illa sosai, domin shi ya karb'owa Fulani Hasiyah maganin da matan Abba ba zasu tab'a haihuwa ba.
.... Yana da wasu abubuwan da zai fada muku, idan kuka kaishe karku ce yayi bayani zai yi da kanshi."
Kashe kiran nayi na kwanta, ina jin babu dadi, kawai na share ina kwancen har aka kira sallah, shiru nayi na wani lokaci kafin na nufi ban daki na duba jikina har yanzun da akwai jinin, madafi na wuce nayi mishi abinci, dan na san gobe zai koma dakin Husnah, wacce da muke kirki da ita, yanzun kuwa kaf kafa take dani, Bata son mu hadu ma. Uwar marasa mutunci ne dai idan ta ganni koda zata ji wani abu sai ta harare ni.
---
Ina idarwa yana shigowa gidan, a hankali na gama kome na fito na same shi ya fito wanka, a d'akina hade hannuna nayi a kirji nace mishi.
"Yallabai sarki! Baka da daki ne?"
"Ina dashi amma ana mata na nake son yin uzurina ko zaki hanani ne?" Ya kafe ni da idanu.
"Gaskiya ana shiga hakkina, kuma wallahi kayi na karshe ka zauna a dakinka duk macen da take da bukatar ka ta bika ba kai zaka bi mace ba, meye amfanin turakar, haka kawai a hanani sukuni, ni gidan ma yayi min kaɗan, Yawwa domin d'akina na Dafur ya ci uban wannan da nake ciki sau biyar, kar na kuma ganin kafarka, kuma ka jawa matan ka kune, wallahi na kuma ganin wata ta turo min shirme zata gayawa makotan su, Babu abin da ya dame ni.
Mata zata ji a jikinta ne, kuma kuma ka dai ja musu kunne."
Cike da Mamaki yake kallona sannan ya sauke ajiyar zuciya yace min..
"A takaice ki ce min kar na sake zuwa miki daki, bawai ki kawo dogon magana ba, tunda bani da gata shi kenan..🤦🏽♀? kuyi hakuri gaskiya na gama gajiya
10/23/20, 10:21 AM - Ummi Tandama: *A yi sha'ani, ɗanbirni ya cuci na ƙauye.*
"Ka kyale ni, bana son damuwa tunda ni ban ya kula da kai ba, kaje ka sami matan ka, tun...."
Murza hannuna yayi a hankali, tare da d'ago kaina.
"Ke kam! Yaushe zaki daina kukan banza ne? Dube ki katuwa, dake kike kuka, idan kika cigaba, zan ga yadda zamu yi dake, nan gaba. Toh ba zan kuma maganar su ba, saboda karki yi min yaji na rasa inda zan fake."
Kifa kaina nayi ina jan majina, murmushi yayi sannan ya cigaba da cewa.
"Tun haduwar mu nake jin na zama magananne! Toh meye na jan majina kuma."
Shigowar Abba da sallama, da sauri ya juya abin shi, yana murmushi. Kunya ta sani saurin kwace kaina. Na shiga ban daki da sauri. Hannun shi biyu yakai wuyar shi tare da sakala hannun, ya sake murmushi, me cike da jin wani irin farin ciki.
Sannan ya buga min kofa yana fad'in.
"Zaki fito ko na shigo" da sauri na bude kofar ina zare idanuna, a hankali ya fincikoni, kirjin shi yana kallon yadda nake murmushi.
"Kina da matsala!" Kiciniyar kwace kaina.
"Toh kuma! Me aka yi? Kina son kirkiran rikici."
Cikin jin haushi nace.
"Kace ina da matsala!"
Waje yayi da idanun shi, sannan yace.
"Akan wannan al'amarin shine kike fushi? Toh ranki shi dad'e, ba zan kuma ba."
Juyawa nayi zan koma bakin kofar dan na san Abban shi yana gurin, yayi maza ya dawo dani jikin shi.
"Hala kun hada danganta da mage ko?"
Gyara rikon yayi sannan yace.
"Tayu kece magen ba!"
"Saraki! Abba yana waje fa."
Sako kan shi yayi kafada na, tare da faɗin.
"Ina zan sani, kin same Yaro qarami kin sanya shi a lungu kina lugwaigwaita shi!"
"Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun! Allah ya shirya ka." Na saka kai na fice bayan na saka hijab dina, baya asibitin baki daya, har zan shiga wani mutum ya mika min wata jaka.
"Inji mutumin da kuke zaman jinya dashi, wai na baki." Amsa nayi sannan na duba, jakat akwai kudi sannan yar takarda.
Ciro takardan nayi sannan na bude..
_Duk wani abun da kike bukata daga ke har shi, zaki iya amfani dashi kafin ku dawo, sannan ki gaida min shi zan koma tunda jikin yayi sauki._
. Sarki Jaamal... Kunya ce ta kama ni, ina shiga dakin ya dauke ni cak ta baya, zuɓewa kayan yayi, na saka yar karamar kara. Dariya yayi sannan yace min.
"Matsoraciya kawai! Ina Abbana?"
Juyawa nayi na kalle shi, kafin na sami damar bashi amsa, nace.
"Ya koma gida."
"Allah Sarki, Abbana kamar kasan Yaron ka yana son girma". Girgiza kai nayi na barci a gurin,
Hannun shi ya saka a baki, kamar me nazari kafin yace.
"Abba yace min lokacin da ban da lafiya binki nake kamar jeka"
Juyawa nayi tare da zuba mishi ido, sannan na juya na cigaba da abinda nake yi, a sannu ya tako, yana zuwa bayana kawai ya kwanta a bayan, ban san lokacin da na sake kwalbar hannuna akan kafana ba, da sauri na daka tsalle. Ina yarfe hannu na. Idanuna suna cika kwalla.
Cak naji yayi sama dani, a bakin gadon ya ajiye ni. Sannan ya rike kafar a tafin hannun shi, yana murza min, cikin nutsuwa. A hankali yake min tafiyar tsutsa, kallon shi nayi zan kwace kafana ya rike gam.
"Don Allah! Ka bari."
Na faɗa muryana yana rawa, sake kafar yayi a hankali ya taso inda nake, zai had'a bakin mu na kauda kaina. Sumbatar wuya na yayi na rike rigar shi, naji sakon har cikin raina. Da sauri na juya ina kallon fuskar shi, lebbena na kasa ya kama, nayi maza na rufe idanuna, ina sauke ajiyar zuciya kamar wacce nayi tsare.
A hankali ya janye daga jikina, ya juya min baya. Nima haka ce ta faru, na rasa wani irin kunya nake ji, lokaci guda na kasa sake jikina da shi, sai da na kwashe minti goma sannan na mike daga gadon, yaki ya juyo min kawai nace.
"Wasssssh kafana!" Da sauri ya juyo gare ni, kashe mishi ido nayi tare da sake mishi dariya na shige ban daki, sai da na gama na fito.
A bakin kofar shiga na same shi, cikin nutsuwa na ture hannun shi zan fita ya dawo dani da hannu ɗaya. Ya hada ni da kirjin shi.
"Ina son abubuwa akanki, sai dai bazan iya ba! Ina da matukar kishi. Ina son kasancewa dake! Ina kishin ki, bawai dan ina son ki ba, a'ah kawai ina ƙyamar abin da wani yaci ya bari ne."
Mutuwar tsaye nayi domin ban sannan zai iya gaya min magana haka ba, gyada mishi kai nayi sannan nayi wuccewa ta nayi sallah, ina zaune da yar karamar Alqur'ani, malamar jinya tazo ta bashi yace ya ajiye ni yake bukata na bashi. Ina jin shi nayi banza da shi. Da gayya baki kammala karatun dan kar ya dame Ni.
Shiru yayi shima, ya gabatar da sallar da yake kan shi, wasa wasa har lokacin shan maganin shi ya nemi wucewa, bai ce min kome ba, ran shi ya b'aci dan haka da kan shi ya sha maganin, da gayya naki kula shi, har dare muna nan a gurin.
Koda lokacin bashi na dare yayi sun zo bai hana matar ba, ya amsa nata, da dare ina kwance. A dogon kujerar dake cikin dakin, sai ji nayi ya d'aga ni cak, zuwa gadon. Buge hannun shi na fara ƙoƙarin yi, amma ya danne ni da kirjin shi, tare da mai damin hannuna baya, kauda kaina nayi raina na kara b'aci nace mishi.
"Sake ni!"
"Ba zan sake ki ba, kin zata wani abu zan nima a jikinki? Ko ce miki aka yi zan ratsa hanyar da wasu kartin maza suka bi ne, ni zaki ne, duk abin da zanci mike fara farautar shi, idan na gama na barwa sauran kananun namun daji suci, ke har kin isa kiyi fushi dani, dan na kyale ki, ina wasa dake?
Wallahi ki shiga hankalinki, ko kuma na baki mamaki, zan miki abin da ko suna na aka kira sai kin rintsa idanun ki, dan haka ki cigaba da abinda yayi miki Bazan hanaki ba."
Kallon shi nayi cikin wani irin kuka, na buge hannun shi da yake rike dani, na shiga ƙoƙarin ture shi, mutum sai kace bishiyar kuka. Sake danne ni yayi cikin ko in kula, yake azabtar dani. Kuka nake sosai tare da ture hannun shi, murmushi yayi sannan yace.
"Ina jin kunyar ki sosai! Ki k'iyayye haka, kuma ki bani abinda zanci."
"Bazan baka ba, kaje ka sami matan da kake so su baka, me zan maka ina sauran wasu." Had'iye kukan nayi sakamakon, (🙈🙊🙉) yunkurin amai nake, amma mara kirki sai da ya tura min bakin shi cikin nawa, kai....kai.. abu dai bai dad'i ba. Domin Jay ya rena ni, sai da ya tara min gajiya sannan ya kyale ni ya sauka daga gadon, ya koma saman kujeran yayi kwanciyar shi. Saboda kuka idanuna har yaji suke min.
Mai da al'amarin babba yayi dan fushi ya dauka dani, sai nima na share shi, ko ya zata bazan iya share shi