Showing 15001 words to 18000 words out of 87436 words
Chapter 6 - KIRAN RABO BOOK1 COMPLET BY NANA HALEEMA.txt
ta ce, "kenan ku ne masu yi masa gadina, sai baƙin da ku ka ga dama sannan zasu zo su ganni ko?." Zasu yi magana ciki tsawa ta ce, "ku fice ku bani waje!." Dole suka cika umarninta suka fita. Didi ta dawo da kallonta gare shi ta ce, "kar ka sake ganin baƙuwata ka sake yi mata ihu, in kai baka buƙatar baƙi ni ina buƙatarsu, wajena tazo ba wajanka ba dan haka babu ruwanka da ita."
Wani irin yake ji a jikinsa da zuciyarsa, ya zubawa Didi ido cikin abubuwan da suka tarar masa a ƙirji. Na farko kukan da Nayla take yi yana daga cikin abinda yake sake harzuƙa shi, a ganinsa dan shagwaɓa shi zata saka a gaba tana yiwa kuka, me aka yi mata?. Na biyu faɗan da Didi take masa a gaban baƙuwa yafi komai ɓata masa rai. Ta fi kowa sanin baya so ayi masa faɗa a gaban mutane balle kuma mace baƙuwa wacce bai santa ba, babban abin haushin ma ko gaisawa bata tsaya sun yi ba ta fara yi masa faɗa akan wata wacce bata da alaqa da ita.
Kallon Nayla ya yi a fusace ya ce, "dalla malama ki yiwa shiru ko na yanka bakin ki!." Wata irin firgita Nayla tayi sai gata ta dawo ƙasa daga kan kujera ta cure waje ɗaya jikinta na tsuma. Babu zato babu tsammani ta ji maganar shiyasa ta gigice.
Didi ta sake fusata ta kalle shi ta ce, "Omar fita ka bar min falo." Ido ya waro waje jin mamakin abinda tace, a daidai lokacin da Nayla ta kalle shi sai ta sake gigicewa ganin idanunsa kamar za a saka hannu a cire saboda girma. Kafin ya yi magana ta sake cewa, "na ce ka fita ko!?." Bai ce komai ba ya juya ya fita a zuciyarsa yana tabbatar da dole ma ya hukunta Nayla duk da bai santa ba.
Didi ta koma kusa da Nayla ta riƙe ta ta ce, "yi haƙuri Nayla, taso ki zauna." Ta faɗa tana taso da ita ta zaunar da ita akan kujera ta kawo mata ruwa mai sanyi ta ce, "sha ruwa." Ba musu ta karɓa tasha tana sauke ajiyar zuciya. Didi ta kalli gaishe ta sai ta bata dariya ganin hawaye shaɓe-shaɓe fuskarta har tayi ja kamar wacce aka yiwa duka.
"Yi haƙuri kin ji, haka nan yake shi in yaga baƙo ko baƙuwa in bai san su ba shikenan sai faɗa. Ki nutsu ai ya tafi ki goge hawayen nan."
Nayla ta goge idanunta tana jan numfashi amma har lokacin a tsorace take. Sai da Didi taga ta nutsu sosai sannan ta sake cewa, "kar ki damu bazai sake yi miki haka ba." Nayla ta ce, "ai bazan sake zuwa ba ma Didi, bara na ɗauki waya
ta na tafi."
Didi tayi dariya ta ce, "Wallahi babu inda zaki je, kuma in baki shigo gidan nan ba shi zan saka ya ɗauko min ke a wajan Hajja." Nayla tayi gum bata ce komai ba amma zuciyarta cike take da tsoron sa, bata taɓa ganin halitta ta mutane wacce take tsoro kamar sa ba.
Ganin ta yi shiru sai Didi ta tashi ta shiga kitchen ta ɗauko abincin da ta dawo kusa da Nayla ta ce, "ko zaki kai masa abincin?." Yadda Nayla tayi da idanu cikin firgici ya bawa Didi dariya ta ce, "wasa nake kwantar da hankalinki" ta faɗa tana fita tana dariya dan wallahi yadda ta tsorata dariya ta bata.
Setroom ɗin da yake gidan wanda ya kasance ɗakinsa ta nufa, kafin ta ƙarasa ya fito har yayi wanka ya canja kaya zuwa na shan isa, dan rigar jikinsa ko hannu bata dashi sai wando wanda ya wuce guiwa da kaɗan. Kallon sa tayi ta ce, "sai mu koma ka ci abinci." Bai kula ta ba sai ma sake tamke fuska da yayi yana kallon ƙofar ɗakin da alama tana ciki tunda ga takalmin ta nan.
Didi ta ce, "Magana nake maka Omar." Nan ma ya share ta dan tsakani da Allah in ba dan ita bace da yanzu ba wannan labarin ake yi ba, ta bashi haushi sosai. Itama sai ta ɗaure fuska ta ce, "ina yi maka magana kayi min banza."
"Me zan ce miki? Kin nuna waccan abar ta fi ni" ya faɗa cike da jin haushi.
"To haka kawai daga ganin yarinya sai ka fara yi mata ihu baka san ta ba baka san daga inda take ba? kai baza a yi baƙi a gidan nan ba kenan?."
Ya kalle ta ya ce, "duk wanda zai zo gidan nan munafuki ne, yana zuwa yaga ya muke rayuwa ni dake." Didi ta ce, "in ma hakan ne babu ruwan ka, kar wata baƙuwata ta sake zuwa kayi mata abinda ka yi yanzu, Wajena suka zo ba wajanka ba." Ya kalle ta ya taɓe baki ya nuna kansa da yatsa ya ce, "ni ki ka yiwa faɗa a gaban wata yarinya, ni kika yiwa tsawa har ki ka ce na bar miki falo kuma duk a gabanta. Ni ko Didi?."
Didi ta kalle shi dama ta san zai ji haushi ta ce, "kaine ka jawo, lokacin da ka shigo da kun gaisa ka shiga ɗaki inda nake ai da hakan bai faru ba." Ya girgiza kai cikin ƙunar rai, baƙin ciki yake ji zuciyarsa, kamar shi tiger Didi ta yi masa faɗa akan wata banzar yarinya wacce bai ma santa ba. Ya kalli Didin da take kallon sa cike da ɓacin rai ya ce, "ni wai kika kora a gaban wata, ni Omar hmm....." ta kalle shi ta ce, "meye hmmm? Kar ka cutar da ƴar mutane, kar ka saka a zubar mata da jini."
"In ki ka ce kar ayi ɓata bakinki ke yi, zata san ta shigo gidan mu ta saka chaji har an yi min faɗa a gabanta. Nan gaba aka ce ta shigo baza ta yi wannan marmarin ba."
Ganin yadda yake cize baki yana maganar ya saka Didi ta ajjiye abincin da ta taho masa dashi ta riƙe hannunsa ta ce, "Omar kar ka saka ka cutar da ita, na faɗa maka kar ka yi mata komai." A fusace ya cire hannunsa daga nata ya ce, "to meyasa zaki yi min faɗa a gabanta? Meyasa?. daga wani gari na dawo ko tsayawa baki yi mun gaisa ba ki ka fara yi min faɗa." Didi ta ce, "shikenan nayi kuskure, amma kar ka yi mata komai na sake faɗa maka."
Kai ya girgiza dan maganar bata wani shige shi ba ganin haka Didi ta ce, "wai baka gane ta ba ma?." Kallon ta yayi alamun na san ta ne daman, ta ɗaga kai dan tana fahimtar saƙon ido in ya yi mata tunda ya saba ta ce, "ka san ta mana, Nayla ce fa jikar Hajja. Yarinyar da aka taɓa ƙoƙarin yi mata fyaɗe ka cece ta ka dawo da ita wajan Hajja?. Ka tuna har ka dinga yiwa Hajja faɗa akan ne aka barta ta fita ita kaɗai bayan a san baƙuwa ce bata san gari ba, ka tuna?."
Kallon Didi yayi jin abinda take cewa dan ya tuna abinda ta ce ɗin tsaf a ransa, har hango lokacin yake yi a idanunsa da yadda komai ya faru. Amma bazai gane ta ba, dan a yanzu ma ba ganin fuskarta ya yi sosai ba, gwara ma a da ɗin ya san fuskarta saboda suna haɗuwa bayan abin ya faru tana yawan zuwa wajan Didi kafin ta bar garin. Bazai manta da ita ba dan ta silar ta ya fara yankewa wani ɗan yatsa a duniya, tabbas a kanta ya fara zubar da jini saboda ceto. Batu ake na shekara tara zuwa goma baya ta ya zai gane ta banda abin Didi?.
"Ni ban san ta ba, ina kallonta a matsayin wacce ki ka yi min faɗa a gabanta" Abinda ya ce kenan ya wuce ya barta a wajan tayi dariya tana jinjina son girma, da son mulki, da zafin kai irin na ƙanin nata, abincin ta shigar masa dashi ɗakim sannan ta koma wajan Nayla.
*Book 1 free ne*
*Book 2&3 paid ne, akan naira 500 kacal*
*VIP group 1k*
*VIP2 on ArewaBooks.*
*domin biyan kudi ka tuntubi wannan number via WhatsApp*
wa.me/2349030398006
Dm to subscribe yours.
Nana Haleema❤️
*KIRAN RABO.*
#Fitattubiyar2025
©️ *Nana Haleema.*
Wattpad@Nanahaleema
Arewabooks@nanahaleema11.
https://chat.whatsapp.com/K8IEI39TB803y9pEtzMmdp?mode=ems_copy_t
*Book 1*
*P 05*
Didi da ta bar wajansa wajan Nayla ta koma ta zauna kusa da ita ta ce, "na bar ki ke kaɗai ko?." Ganin Nayla a tsorace har lokacin sai ta tausasa murya ta ce, "har yanzu a tsorace ke ki ke? Ki nutsu mana." Nayla ita dai gaban ta faɗuwa yake saboda duk abinda suke faɗa tana ji, tana ji Didi tana ce masa kar ya yi mata komai duk shine ta sake firgita. Dana sanin shigowa gidan ta mamaye mata zuciya, ji take ina ma bata shigo ba ta haƙura da chajin wayar.
Didi ta kalli Nayla ganin har lokacin tsorace ta ke sai tayi dariya ta ce, "Wallahi dariya ki ke bani, yadda ki ka firgita haka kamar kin ga wani abin tsoro, In kina nuna kina tsoronsa har haka sai ya fi cewa zai latsa ki. Omar fa yana da sauƙin kai, kawai shi bashi da saurin sabo ne, amma na tabbatar miki kafin ki bar Kano zaku saba, Zaki yi mamakin yadda yake da hira da kuma yawan murmushi." Murmushin yaƙe kawai Nayla tayi dan kawai tana jin ta ne, amma ta yaya zasu saba da dashi bayan abinda ya faru.
Didi ganin tayi shiru ta dinga jan ta da hira kaɗan-kaɗan tana amsawa duk da har lokacin a tsorace take matuƙa. Agogo ta kalla sai ta kalli Didi ta ce, "Didi bara na ɗauki wayata na tafi saboda zan kira Abiy na ji ya koma gida lafiya." Didi ta kalle ta tace, "Ko dai kina so ki gudu saboda Omar?."
"A'a Didi, Abiy zan kira na tabbatar yana jiran kira na."
"To Shikenan. Ina jiranki da daddare ki zo ki taya ni hira." Nayla ta ɗaga kai kawai ta tashi ta ɗauki wayarta da charger tayi hanyar fita Didi na bayanta.
Tana fitowa daga falon yana shigowa gidan idanunsa ya faɗa cikin na ta. Nayla bata san lokacin da wayar charger sun suɓuce a hannunta ba, wayar ta faɗi ta ɗan yi ƙara amma bata duba ba jikinta ya cigaba da rawa. Hannunta Didi ta riƙe ta bayanta, Nayla ta sunkuyar da kai cikin tsoro. Didi ta kalle shi bata ce masa komai ta kalli Nayla ta ce, "Nayla don Allah ki kwantar da hankalinki, kin ga kin yar da wayarki" ta faɗa tana sunkuya ta ɗauki waya da charger ta riƙe mata hannunta har suka bar cikin gidan.
Ai Nayla bata iya cewa Didi komai ba, tana bata wayar ta kwasa a guje ta yi hanyar gidan Hajja. Didi tayi dariya ta dawo cikin gidan tana dariya suka sake haɗuwa da shi cikin dariya ta ce, "Kaji tsoron Allah ka daina tsorara yaran mutane don Allah, haba wannan bala'i daga haɗa ido da kai duk ta ruɗe?. Ni ban ga meye abin tsoron a nan ba." Bai ce komai ba ya sake shiga cikin gidan tayi dariya ta bi bayansa tana jinjina ƙarfin tsoron da Nayla take masa.
Nayla a haka ta faɗa cikin gida a firgice Hajja da Salma da suke zaune a falo suka ganta kamar an cillo ta Hajja ta ce, "ke lafiya?." Nayla ta sauke ajiyar zuciya ta ce, "Hajja har abada bazan sake shiga gidan Didi ba, na gama shiga gidan ko me za a bani." Salma ta wara ido ta ce, "shiyasa daman da Hajja ta ce min kina can nace wallahi bazan je ba, in yaga ka shiga gidansu kamar zai yanka naman ka haka yake ji. Sam baya so ya ga an shiga gidan, ba ya ƙaunar kowa ya shiga gidan su daga shi sai Didi."
Nayla ta ce, "wallahi Salma fitsari ne kawai ban yi ba, yau ni naga bala'i ganin idona. Salma duba min wayar nan ki ga ko screen ɗinta ya samu damuwa, dan yadda ta faɗi a hannuna da na ganshi na tabbatar daƙyar bai fashe ba. Wannan halitta ta mutumin nan akwai ban tsoro, ga ido kamar na aljanu." Salma ta karɓi wayar da take miƙa mata dubawa kana ta ce, "Wallahi ya tsage. Wannan bala'i har ina? daga gidan su ya jawo miki asarar sama da naira dubu ɗari biyu. Dan screen ɗin wayar ki in bai yi haka ba ya kusa."
Nayla ta faɗi akan kujera ta dafe kai ta ce, "gabaɗaya ban shigo Kano da ƙafar dama ba, da fari gidan nan babu haske, ga tashin hankalin da na haɗu dashi sannan ga asara." Hajja da take jin ta take kallon ta tayi dariya ta ce, "wai duk tsoron Ummarun ne ya saka ki ka firgice haka?." Salma ya ce, "ba dole ba Hajja, wannan mutumin kallon sa ma tsoro yake bawa mutane balle kuma ya harare ka ko yayi magana. Ni na jima ban ga mutum bai baƙin hali kamar sa ba, sai kyaun fuska kamar shi ya tsara kansa, amma zuciya da hali baƙaƙe."
Hajja ta ce, "ai kam yana da kirki sosai, kaf unguwar nan ni kaɗai ce nake kiransa da Ummaru ya amsa har yayi min magana. Duk da nima ɗin kafin ya amsa sai ya ce bana son sunan amma sai na faɗa, kuma zai gaishe ni wani lokacin da fara'a sannan ya tafi. Kawai shi baya so a raɓi yayarsa ne saboda mutanen unguwar nan suna yi musu wata fassara mara daɗin ji. Shiyasa sa baya son kowa ya shiga gidan su dan baya ƙaunar munafurci da gulma."
Nayla ta ce, "to mu ina ruwan mu da wata fasaara da ake musu Hajja? Shima ya san in ba dan Didi ɗin ba waye zai shiga gidan nan? To Didi tana da kirki sosai, tun ɗazu naso fitowa amma ta hana ni ta ce sai yanzu zan fito, shima ƙaryar zan kira Abiy ne ma ya saka ta ƙyale ni. Har tana cewa na dawo da daddare, to in ba aljanna ake bayarwa ba me zai kai ni gidan nan na ta?."
Salma ta ce, "bashi da mutunci bai san mutunci ba, ai ko dan yayarsa ya kamata ya dinga ɗagawa mutane ƙafa. Ni fa shiyasa wallahi bana ma shiga gidan dan bana so na haɗu dashi kwata-kwata, In ta shigo gidan nan ta dinga yi min mitar bana shiga inda take, kin san ni babu ɓoye-ɓoye kai tsaye na ce mata Omar yana gidan bazan iya shiga ba.." Nayla ta ce, "ina yaga kirki? shi ai abin alfaharinsa ne ma a shiga gidan su. Nima ba dan chaji ba da sai dai ta shigo ta ganni, duk abinda zata ce bazan je ba."
Hajja tayi dariya ta ce, "ke dai kawai ya firgita ki ne Hauwa'u."
"Wallahi sosai Hajja, haka na saka Didi a gaba ina kuka tana rarrashi." Hajja tayi dariya sosai ta ce, "ke fa babu abinda zaki cewa Omar wallahi, ya taimake ki a lokacin da ake gab da tuntsurar miki da budurcinki. Ba dan shi ba da yanzu ana zancen an yi miki fyaɗe shekarun baya."
"Hmmm!" Shine abinda Nayla tace kawai tana sauke numfashi. Salma ta ce, "Kai Hajja! daman wai shine ya taimake ta?." Hajja ta ce, "Ke duk labarin da ake yi baki sani ba?."
"Ban taɓa tsayawa na fahimta ba ai."
"Shine wallahi. Haka ya ɗauko ta kamar jaririya saboda a tsorace take sosai sai kuka take yi daman ita sarkin shagwaɓa. Gashi babu riga a jikinta sun yaga rigar atamfar da take jikinta, hakan ya saka shi ya cire rigarsa ta sama ya saka mata sannan ya dawo da ita."
"Innalillahi wa'inna ilahir raji'un! Don Allah Hajja ki daina faɗar haka bana so wallahi" Nayla ta faɗa da ƙarfi tana runtse ido. Salma ta sake cewa, "Hajja wai kina nufin rigarsa ya sakawa Nayla?." Hajja ta ce, "ƙwarai kuwa."
"Tab! amma ya cuce ta wallahi."
"Meye na cuta shi da ya yi taimako? Kuma magana ake ta shekaru takwas ko tara baya."
"To Hajja shekara tara baya a ƙalla tana da shekara sha uku ko sha huɗu."
Hajja ta kalli Nayla da har lokacin idon ta yake a kulle ta ce, "Kuma da yake tana da girman jiki ƙirjinta a cike yake shiyasa ma suka so lalata ta." Nayla tashi tayi ta bar falon cikin takaici da baƙin cikin wannan labari, ta tsani ta ji ana bada labarin nan ko kusa.
Salma ta ce, "Gaskiya Hajja ki daina bada labarin nan, hakan yana nufin fa ya gama ganin halittarta tun shekarun baya. Yanzu kallon raini yake mata shiyasa ma yake tsoratata."
Hajja ta ce, "to sai me? Da ya gani ɗin wani abun yayi mata? Da ya barta a wajan su da ba lalata ta zasu yi ba?. Ni tun daga lokacin nake ƙaunarsa saboda abinda ya yi mata, daga ranar ya fara riƙe amfani da makami dan a kanta ya fara zubar da jini, akan taimakon ta ya fara saka makami a jikin mutum. Haka yazo gidan nan yana faɗa kamar ƙanwar sa aka ao cutarwa. Ni yayi min, kuma har gobe ina kallon sa da wannan ƙimar."
Salma tayi shiru bata ce komai ba Hajja ma tayi shiru dan da alama tana taya ƴar uwarta kishi dan ance ya ɗauko ta babu riga. Ita kuma bata ga abin fushi ba, taimako ne kuma ya wuce wataƙila ma shi ya manta.
Omar kuwa bayan Nayla ta fita shima fita ya yi bai dawo ba sai bayan an yi sallar magriba as usually shi da mutanen sa. A falon ta suka baje suka ci abinci kamar yadda ya saba ciyar da su kafin ya sake fita. Bai dawo ba sai tara na dare ya same ta a zaune da waya a hannunta tana dannnawa.
Kallon sa tayi bayan ya shigo ta ce, "baka faɗa min me ya faru a Abujaa ɗin ba." Zama yayi ya kalle ta ya ce, "wani ɗan aiki zan yi zuwa wani satin."
"Allah yasa ba harkar siyasa ba ce ba." Murmushi yayi kaɗan amma bai ce komai ba. Ta kalle shi ta ce, "ina so ka gane ƴan