Showing 18001 words to 21000 words out of 87436 words
Chapter 7 - KIRAN RABO BOOK1 COMPLET BY NANA HALEEMA.txt
siyasar nan amfani suke yi da ku wajan lalata rayuwarku su kuma su inganta ta ƴaƴan su, ku ɗauki makami ku je ku yi musu yaƙi su kuma su gina yaran su da ilimi. Kuna nan kuna wahalar banza kuna haƙilo ƴaƴan su suna gida cikin ac da kwanciyar hankali, ku kuma sun mayar da ku ƴan wahala waɗanda ba su san darajar kan su ba. In da gaske yaƙin neman zaɓen su ke yi su fito a yi da ƴayan su mana. Baza su yi ba saboda rayuwar ƴaƴan su ba irin ta ku bace, aikin ku ku salwantar da rayuwarku a kan su, su kuma su gina na su." Kallon Didin yayi ya ce, "Didi kenan."
"Ko nayi ƙarya ne?."
"A'a" ya faɗa yana ɗauko wayar sa ƙirar iphone yana dannawa.
Didi ta kalle shi ta ce, "Ni wai ya aka yi ka ke iya operating ɗin waya? Gashi ko labarai ne da turanci sai na ji ka karanta ka faɗa min, ya abin ya ke?." Ya kalle ta da mamaki ya ce, "Oh dan bana so ana yi min magana da turanci shiyasa ki ke yi min kallon ban iya ko?." Ta yi ƴar dariya ta ce, "A'a ban ce ba. Kawai dai na san ko secondary school baka yi handling ba, duk da ka ce jarabawa ce baka yi ba."
Ya kalle ta ya ce, "Ai kin san jarabawar ce ban yi niya ba, kuma mutum nawa na rubutawa waec ana biyana?. Ko ke da ki ke taƙama da wani NCE ko diploma sai mu zuba, wallahi sai na kai ki ƙasa ko motsi baza ki iya ba. In kina mamaki a feɗe biki biri har wutsiya." Ta yi dariya sosai ta ce, "Wane mutum! Ku ai gifted ne, ku karatu yake bi kuna guduwa. Da ka tsaya ka yi karatu ko Omar, da ba ƙaramin amfana za a yi dakai a ƙasar ka ba."
"Babu niya, tunda sai wanda yake da ilimin boko ne yake zama wani a duniya zan ta zama a yadda ku ke kallona."
Didi ta ce, "Allah ya ke bawa kafirai arzuƙi a duniya balle musulmi mai bauta masa?. Allah yana bada duniya ga wanda yake da wanda baya so, lahira ce sai rabo. Ba sai mai karatun boko ne yake zama wani ba Omar, in dai Allah ya saka maka albarka zaka iya zarce wanda ya kai matakin professor. Ilimin yana da amfani ne saboda goyayya da mutane."
"Mutane haka suke ɗauka, wanda bai yi boko ba babu shi babu arzuƙi a duniya. Turanci ne kaɗai ilimi a nigeria, duk ilimin ka in baka iya shi ba a banza ake kallon ka. Mu baza mu yi karatun ba, kuma baza mu yi turancin ba, in Allah ya ce yes sai na ga ɗan shegiyar da zai ce no. Ko yanzu in niya zan je a bani takardar da ku ke taƙama da ita, kawai babu niya ne."
Didi ta yi dariya cikin tsokana ta ce, "Ni dai ina so naji ya akayi ka ke iya karanta turanci? Ko duk zaman social media ɗin ne ya kawo haka?. Yadda ka ke zama ko yaushe cikin danna waya da kuɗi ka ke samu da ita da ka ji daɗi." Murmushi ya yi kaɗan bai ce komai ba.
Ta ce, "tsokanarka nake, ko a shekarun baya kana cikin wanda makaranta take ji da ku." Bai bata amsa ba sai girgiza ƙafa da yake yi, ta kalli ƙafar ta sa ta ce, "wai ni meye benefit ɗin wannan baƙin abun da ka saka a ƙafarka? Gashi dai yana yi maka kyau sosai, amma adon mata ne."
Taɓe baki ya yi bai ce komai ba ta ce, "ko da yake ko mace aka gani da sarƙar ƙafa wata fassara ake mata daban."
"Ni kam yana burge ni."
"Sai matarka ta saka." Bai ce komai ba cikin tsokana ta ce, "Wai kuwa ka san me aure yake nufi?." Wani kallo ya ɗago ido yake mata na kin raina min hankali, Didi ta sheƙe da dariya ta ce, "to kai ba abokai ne da kai ba, ba wani waje ka ke zuwa ba ta ya zaka fahimta daidai?." Murmushi ya yi bai kula ta ba dan bazai kulata ba.
Kira ne ya shigo wayar Didi ganin sabuwar number sai ta ɗauka masu siyan abincin ta ne, ta saka a speaker daga can ɓangaren aka yi sallama jin muryar namiji sai ta amsa a sanyaye kafin ya ce, "don Allah da Aisha nake magana?." Didi ta ce, "eh itace. Wake magana?."
"Sunana Abdulhamid."
"Allah sarki!."
"Aisha ina so ki bani lokaci ina so zan yi magana dake." Didi ta kalli Omar da ya kafa mata idanu ta ce, "Magana da ni? Akan me?."
"Alkhairi. Magana a waya baza ta yu ba ikon ganin ki nake so ki bani." Didi tayi ajiyar zuciya ta ce, "To san sanar da kai."
"Yauwa na gode, don Allah ki saka lokaci mafi kusa in hakan zai samu."
"Shikenan, zan maka text."
"Na gode sosai, ki kwana lafiya" Didi ta amsa shi kuma ya kashe wayar.
"A ina ya samu number ki?" Omar ya tambaya yana kallonta.
"Omar ta ya zan sani? Ni dai kawai ya kira ni ne."
"Me ya ke nema?."
"Omar ta ya zan sani? A gaban ka fa ya kira ni."
Omar ya ce, "wanne lokaci zaki ba shi?."
"Bana ce ba." Ya kalli Didi cikin bada umarni ya ce, "ki faɗa masa yazo jibi, jibi juma'a kenan, ina gida nan zan so na zauna a tatauna dani. In da tsiya ya zo gidan ya tarar, in arzuƙi ne ya kawo shi ana yi masa maraba." Tayi murmushi ta ce, "to babban Yaya." Jin abinda tace sai yayi murmushi amma bai ce komai ba.
"Kai yaushe zaka yi auren ne?." Ya ɗan juya idanunsa ya ce, "kwana biyu meyasa ki ke yi min zancen aure ne?." Tana murmushi ta ce, "ai ka kai ka yi ɗin ne Omar, santalelen saurayi kamar ka ga kyau ga kwarjini ai dole ayi maka zancen aure."
"Ni wallahi bana kawo zancen aure a raina ko kaɗan."
"Ko me yasa?."
"Sai na fara aurar da ke" ya faɗa yana miƙewa tsaye.
Ƴar dariya tayi ta ce, "Ko kuma ni na fara aurar da kai ba." Bai yi magana ba ta miƙe tsaye tana kallon sa duk da ya kere mata a tsayi sosai ta ce, "burina naga kayi aure ka haifa mana mai sunan Mama Omar, duk macen da ta same ka zata yi sa'a, a haka ne ake kallon ka a baibai amma ni da na san ka, na san sa a tana tare da wacce zaka aura, musamman in ka ɗauki nasihar da nake yi maka a kullum."
Fuska sake yake kallon ta ya ce, "Yanzu in aka aure ni ba a yi sa a ba kenan?."
"Eh to, kusan hakan zan ce." Yayi murmushi mai sauti ya kalle ta ya ce, "ina zuwa." Fita yayi daga gidan gabaɗaya. Kasancewar unguwar akwai duhu da ya fito ƙofar gidan daga wajan gidan su ne kawai mai haske sauran wajan babu haske.
A hankali yake takawa yana jiyo magana na tashi ana daga inda yake nufa, muryar maza ya ji suna cewa, "hmm to Omar da Aisha meye basa aikatawa, kai a banza ta kai yanzu bata yi aure ba?. Wannan ingarmar namijin da take kwana dashi waje ɗaya ta tashi ba dole mugun abu ya faru ba."
Ɗaya daga cikin su ya ce, "wai don Allah da gaske ku ke?." Na ukun ya ce, "to kai gani ka ke wasa ne? Baka ganin yaron ko kula mutane baya yi saboda ya san iskancin da yake yi?. In da ma ace iya dabancin ya tsaya da sauƙi, to har da lalata da ƴar uwarsa. Ai ba a banza ta kai wannan shekaru babu aure ba, tana samun duk abinda ƴa mace take samu a gidan mijinta a wajansa. Kai baka ganin da an zo neman aurenta sai a gudu ba? Wannan mugun abun da suka binne ake tonowa."
"Kuma fa ashe gado ya yi, ubansu tantirin ɗan iska ne tsohon ɗan giya. Ai barewa baza tayi gudu ɗanta ya yi rarrafe ba, nan gaba zaman unguwar nan sai Omar ya hana mu."
Omar yana jinsu ya runtse idanu cikin ɓacin rai da ƙunar zuciya, ya koma da baya ya hangi yaransa a gefe yayi musu alamun da su yi shiru kar su yi magana su zo inda yake. Nuni ya yi musu da kowa ya kama mutum ɗaya a cikin ƴan majalisar da suke gulmarsu. Cikin sanɗa suka ƙarasa inda suke sai caraf ko wanne ya riƙe mutum ɗaya.
Omar ya tako ya bayyana a gabansu ransa a ɓace sosai duk suka kalle shi cikin firgici da tsoro. Alama yayi musu da su sake su, dukkan su suka sake su ya bisu da kallo dan dukkan su manya ne a haife zasu haife shi. Babu wanda yayi ƙoƙarin miƙewa a cikin su saboda duk sun tsorata matuƙa suna kallon Omar. Abin ka da wanda yake gulmar wani kuma ya kama shi, wanin ma kuma irin Omar."
Tsakiyar su ya shiga ya zauna tare da ɗauko ƙaramar wuƙa a ƙasan takalmin yana shafa ta a hankali ba tare da ya kalle su ba. Duk sun ruɗe, jikinsu ya fara ƙyarma cikin tsoro. Zaman da ya yi a cikin su yafi komai tsorata su, ga wuƙa kuma a hannunsa. Ajiyar zuciya Omar ya yi, ya daidaita kansa kana ya ce, "Ku maimaita hirar da naji kuma yi yanzu." Tsit suka yi kowa ya kasa cewa komai, Omar ya kalli ɗaya daga cikin su sai kawai ya zube a ƙasa saboda tsoro jikinsa na rawa sosai.
"Ku maimaita na ce" ya sake faɗa a kausashe yana kallon su. Nan ma suka yi shiru ya girgiza kai ya ce, "kenan kun san ba daidai ku ke faɗa ba ko? Shikenan, tunda baza ku yi magana ba bara na saka a saka ku magana."
Kallon na gefen sa ya yi nan take suka taho da wuƙa suka ƙaraso wajan. Omar ya sake kallon mutanen yaga duk sun tsorata gasu kuma manya dan suna cikin manyan unguwar.
Ɗaga musu hannu yayi alamun kar ya ƙarasa inda mutanen suke ya ce, "Maganar da ku ka faɗa a kaina da Didi naji kuma zan ɗauki mataki akan hakan, abinda ya saka bazan iya yi muku komai ba kun girma iyayen wasu ne ku. Ba dan ina jin tsoro ko kunya ba, sai dan haka na yi niya."
Bash ya ce, "Damisa ai in babba bai ji tsoron hawa jaki ba, jaki bazai ji kunyar kayar dashi ba."
"Allah ya baka haƙuri" ɗaya a cikin su ya faɗa yana kallon Omar. Omar zai yi magana wani matashin saurayi ya ƙaraso wajan ya ce, "Baba lafiya?."
Omar ya kalle shi ya kalli wanda ya kira da Baba bai ce komai ba yana jira ya ji ne zai ce. Murya na rawa Baba ya ce, "lafiya lau." Yaron ya ce, "lafiya naga wannan a tsakiyar ku da wuƙa a hannunsa?." Omar Bash ya kalla yayi masa alamun da a kawo yaron, ai kuwa suka damƙe shi aka ɗukar dashi a kusa da Omar.
Cikin takaicin da ya ke ji a zuciyarsa ya fara tsinke fuskarsa da mari cikin tsananin fusata. Ya jawo rigarsa ya kalle shi ya ce, "ku hana iyayen ku yin magana a kaina da rayuwata, in ba haka ba wallahi duk abinda nayi musu ku yi kuka da kan ku." Ya sauke numfashi cikin baƙin cikin da yake ji a zuciyar sa ya ce, "ina yiwa mutum alfarma sau ɗaya tak a rayuwarsa, to na yiwa iyayenka, na ga girman su duk da basu duba girman su ba suke faɗar ko wacce magana a kaina, ina gargaɗin ka da su kansu akan abin yazo ƙarshe daga yanzu, In hakan ya sake faruwa bazan ɗagawa kowa ƙafa ba" ya faɗa yana sakin yaron tare miƙewa zai bar wajan.
"Me ka ke taƙama dashi?." Yaron ya faɗa yana kallon sa." Juyowa kawai yayi bai ce komai ba ya juya ya bar wajan, inda zai je ɗin ma ya fasa dan in ya tsaya wallahi zai iya yiwa yaron kaca-kaca da fuska kawai ya bar wajan yafi alkhairi.
*KIRAN RABO.*
#Fitattubiyar2025
©️ *Nana Haleema.*
Wattpad@Nanahaleema
Arewabooks@nanahaleema11.
https://chat.whatsapp.com/K8IEI39TB803y9pEtzMmdp?mode=ems_copy_t
*Book 1*
*P 06.*
Duk abinda ya faru a kan idanun Nayla da Salma da suka ta dawo daga unguwa aka ajjiye su a farkon layin suka shigo a ƙasa. Sai da suka tabbatar ya shiga gida sannan suka shiga wajan Hajja Salma tana faɗin, "Shi wai wannan bawan Allah babu abinda ya iya sai mugunta?." Hajja ta kalli Salma ta ce, "wa kenan?." Nayla ta ƙaraso ta zauna ta ce, "Waye in ba wannan basamuden na gidan Didi ba, Hajja kin ga yadda ya kama fuskar wani yaro yana mara kamar Allah ya aiko shi?."
Hajja ta ɗan yi tsaki ta ce, "wai a cikin ku Hauwa'u da Salma wacece take son Ummaru ne?." Salma da take shan ruwa sai da ta ƙware jin abinda Hajja ta ce ruwan ya dawo mata ta fara tari. Nayla ta kalle ta ta ce, "Sannu Sis, dole ki ƙware fa, wannan kalami na Hajja sai ya saka zuciyarka ta daina aiki na wucin gadi. Wai so, Allah na tuba meye abin so a wannan mutumin? Sai dai hasken fata."
Salma da ta dawo daidai ta kalli Hajja ta ce, "So fa Hajja?." Hajja ta kalle su ta ce, "bai kai a so shi ɗin bane ba?." Nayla ta taɓe baki ta ce, "ya kai, amma a wajan ƴan jagaliya kamarsa. Da ilimin mu da komai Hajja ki faɗi wannan maganar a kan mu? Wannan ai kamar babban saɓo ne wallahi."
Hajja ta ce, "to tun ɗazu ku ke maganarsa har yanzu kun kasa dainawa, wanda ake so shi ake yawaita magana a kansa ai." Nayla ta kalli Salma suka ƙyalƙyale da dariya Nayla ta ce, "Shi tantirancin sa ne ya saka mu ke magana a kansa, kuma abin alfaharin sa ne ma mata masu class kamar mu suna maganarsa. Batun so kuma Allah ya tsari gatari da saran shuka, Allah na tuba ya wuce na zaunar dashi na koya masa karatu?. Wai a taƙaice ma yayi makaranta kuwa? Dan irin su wallahi basu cika karatu ba, addini ma gararar su yake yi."
Hajja ta murmusa kawai bata ce komai ba Salma ta ce, "to ina ya ga lokacin yin wani karatu kullum ana yawo da wuƙa? Kuma wallahi laifin ƴan unguwar nan ne da ba a samu wani shegen da yafi shi hauka ya koya masa hankali bane shiyasa yake abinda ya ga dama. Haka kawai ya kama mutum yana zabga masa mari ga iyayensa a zaune." Hajja ya ce, "na faɗa muku Omar bashi da matsala, kuma tunda ki ga haka ɗayan biyu ne, in ma an zagi mahaifiyarsa ko kuma an yi magana mara daɗi akan Aisha."
Hajja ta kuma cewa, "kun san mutanen hausawa da wani banzan tunani, tunda Aisha bata taɓa aure ba kuma suna zaune gida ɗaya da ƙaninta shikenan ake musu kallon ƴan iska. Majalisar maza ake zama ana dasa gulmar su wai neman junan su suke yi." Nayla ta buɗe idanu ta ce, "a'uzubillahii! Kaji wani jahilci don Allah."
Hajja ta ce, "Wannan maganar ba baƙuwa ba ce ba a unguwar nan, sau da yawa za a zo neman aurenta amma da wanda yazo neman auren ya
tafi shikenan bazai dawo ba an je an zuga shi an ce ai tana bin ƙaninta suna lalacewa a gida. Jinkirin aure bashi da daɗi, dan babu yadda zaka canja ƙaddararka ne amma wanda yake cikin irin yanayin shi kaɗai ya san halin da yake ciki. Aisha kam tana ganin jarabawa, wanann ya zo sai an fara abu kamar na kirki sai a watsar, gobe ma wani yazo shima ya gudu."
Salma cikin tausayi ta ce, "Allah sarki Didi! Amma duk masu faɗar wannan kalami mai munin tsiya ba su yi mata adalci ba, kuma sai Allah ya yi musu hisabi."
Hajja ta ce, "tunda ku ga yana wannan hukuncin daƙyar ba maganar yaji suna yi ba, dan shi zaki iya zagin shi ya wuce ki amma kar ki taɓa Aisha, sonta yake kamar ya bata ran da yake dashi ta haɗa da nata, saboda Aisha itace kamar uwarsa da ubansa."
Nayla ta ce, "gaskiya indai haka ne yayi daidai wallahi, in ma ƙara ya kai su gaban hukuma ai daidai ne. Wannan wanne irin ƙazafi ne mai baƙin muni haka?." Salma ta dawo kusa da Hajja ta zauna ta ce, "Hajja to ina ƴan uwan su ne?." Hajja ta kalli Salma ta ce, "ke bacci nake ji, in Allah ya kaimu gobe na baku labarin asalin su Aisha da Ummaru." Nayla ta ce, "kai Hajja ki faɗa mana yanzu mana." Hajja ta harare ta ta ce, "yanzu da nace wata tana sonsa cikin ku sai kuka ce a'a, in ba so ba meye na son jin labarinsa?."
Nayla ta gimtse fuska ta ce, "Hajja ki daina kawo batun nan ko da wasa don Allah, kawai muna so mu sani ne ba dan wai wani abun ba. So ki ke Daddy yaji labari ya zane mu?" Ta faɗa tana kallon Salma suka ƙyalƙyale da dariya. Hajja tunda taji sun ce Daddy ta san mahaifin Salma suke nufi babban ɗanta kenan. Hajja ta ce, "ko shi daddyn in ɗaya tana son Umar ɗin ina ruwansa?."
Salma ta wara idanu ta ce, "Maza ki yi istigifari Hajja, dan wannan babban saɓo ne." Hajja tayi dariya ta girgiza kai ta ce, "Ni ko labarin gidan Daddyn ma baku bani ba, kun shigo kuna yi min hirar saurayin Hauwa'u" ta faɗa tana kallon Nayla da tsokana.
Nayla ta ce, "Hajja ki daina cewa saurayina, saurayina yana Kaduna ba a Kano yake ba. Sannan ba sunana Hauwa'u ba Hawwa nake, ki dinga cire u ɗin nan don Allah."
"Bazan cire ba, Hauwa'u zance, Kuma na faɗa Umar saurayinki ne." Nayla rai ta ya ɓaci amma ganin Hajja tsokanarta take yi sai tayi dariya suna hira da Salma dan Hajja ya shiga ɗaki.
*Kaduna.*
Abiy da Mama a zaune a