Showing 63001 words to 66000 words out of 88313 words

Chapter 22 - ABUL KHAIRI Complete Hausa Novels by Nafisa Ismail lawan.txt

TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)'''

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

           *P.W.A*✍️

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

            *SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Mahaifiya ta Abar alfahari na, Uwata maganin kuka na, I love You so Much Momma_ ❤️




*________________________________*

              *PAGE 33*

*________* Duk inda tabi yana bin ta da ido a sace har ta gama kwashe mata kayan ta mayar a akwatin

Ita kanta a takure take amma babu yanda zata iya, but ji take yi kamar tayi ta kurma ihu sabida a yanda take

Har ta gama zata fice da sauri ya tsayar da ita da faɗin, "shirya ta a nan ki wuce da akwatin ɗakin ki".

Babu yanda ta iya ta amsa mishi da sauri tana zuwa har gaban sa ta ja hannun Babyn, ji take yi kamar ta nitse sabida yanda ta kama shi yana kallon ta, da sassarfa ta isa gaban akwatin ta soma shirya ta

Babyn na mata ƙorafin, "ga kayan da take so a saka mata".

Amma ina ko jin ta ba ta yi, burin ta kawai ta bar ɗakin. Tana gama wa ta fice jaye da akwatin, kai tsaye ɗakin ta ta shige tana sauke numfashi, "oh Allah na kunya zata kashe Ni". Goshin ta ta kama tare da matse wa tana jin zuciyar ta kamar zata faso ƙirjin ta tsaban buguwan da take yi, ta jima a haka daƙyar ta daidaita nutsuwar ta kafin ta isa ga kayan ta ta saka, har da ƙara wa da hijabi don baza ta iya fita haka ba, kunya bazai bar ta ba, da ba don akwai Baby ba babu abinda zai saka ta sake fita, abincin ma ta yafe baza ta ci ba, shi kuma idan ya ci don kansa, ta san ko ta zauna ƙila zai kira ta ko don Baby. Tana fita kuwa ta gan su zaune a Parlour

Shi ya kwantar da kansa saman kujeran idanuwan sa a lumshe

While Baby na gefen sa tana masa surutu tare da danna Remote

Kallo ɗaya tayi musu ta kau da kai ta nufi Kan dainning, sai da ta zauna kafin ta ƙwala wa Babyn kira, "ta zo ta ci abinci".

Da sauri ta taso ta zo ta zauna itama a saman dainning ɗin. Har suka gama be taso ba yana a yanda yake

Maimuna gyara wajen tayi sannan ta wuce ɗakin ta

Ita kuma Baby wajen sa ta koma tana ta zuba mishi surutun da ba ta gajiya

Sai a lokacin ma ya samu ya tashi ya isa kan dainning ɗin ya ci abincin, bayan ya gama ya dawo parlour'n lokacin har Baby tayi barci, ɗaukan ta yayi ya nufi da ita ɗakin Maimuna

A time ɗin itama har barci ya soma fizgarta taji motsin shigowan su, da sauri ta buɗe ido tana ware su a kansa

Haɗa ido suka yi amma be ce mata komi ba illa ɗauke kansa da yayi ya ajiye Babyn saman gadon ta sannan ya fice, shima ɗakin sa ya wuce yayi shirin barci ya kwanta, gaba ɗaya ya kasa barcin sai juye-juye yake yi, duk idan ya rufe idanu surar Maimuna yake hango wa ya rasa ya zai yi ya kauce wa hakan, ba ƙaramin dauriya yayi ba da iya danne kansa a yau ɗin, amma kuma ba ya jin zai iya jure irin wannan rayuwan Gaskiya, wata zuciyan tace mishi, "to wa yace ka jure dama? Matar ka ce fa babu wanda zai hana ka zuwa gare ta, gwara ma ka cire komi a ranka ka je ka more auren ka, ai biyan buƙatan ka a wajen ta ba hakan ke nufin kana ƙaunar ta ba tunda matar ka ce ta sunna, kuma akwai haƙƙin ta ma a kanka". Mirgina wa yayi yana me kifa cikin sa tare da matse filon da ya riƙe, tunanin yanda zai iya fuskantar Wannan matsalan tasa yake yi amma ta ya ya? Taya zai iya zuwa wajen ƙanwar bayan-bayan sa domin biyan ɓukatan sa? Wannan ai raini ne ma, "kai amma wlh an cuce Ni, da ace wata ce ko ba na son ta sai na je gare ta". Yayi maganar a fili cike da haushin abinda iyayen sa suka yi masa na haɗa sa aure da Maimuna.



        A wannan daren dai daƙyar ABUL KHAIRI ya iya yin barci wanda har ya so ya makara da safe, a lokacin da ya gama shirin sa ya fita Parlour har Maimuna su ma sun gama nasu, sun yi Breakfast sannan ta zuba wa Baby wani a coolar

Tana ganin ya fito tayi saurin gaishe shi

Be amsa ta ba don mugun haushin ta yake ji, hannun Baby kawai ya riƙe suka fita tare

Itama Maimunan sai ta tashi tabi bayan sa duk ranta babu daɗi ganin be yi break ba, kuma ta haɗa masa abubuwa duk dan ta faranta masa. A baya ta zauna ganin Baby a zaune a gaban

Be ce mata komi ba ya ja motan suka wuce, yana sauke su ya wuce abin sa ko magana ya ƙi yayi, sai ɗaga wa Baby hannu da yayi.






▪️▪️▪️▪️▪️▪️▪️▪️▪️

           Wani mugun kallo Umma Sulaima ta sakar mata, cike da jin haushin ta tace, "amma wlh yanzu na san cewa ban yi dacen haihuwa ba Azeeza, yanzu dan uban ki duk abinda ya faru hakan be zamar miki ishara ba a kan ɗan iskan yaron can ba? To wlh ki ji da kyau da Baban ki zan haɗa ki bari ya shigo".

Kumbura fuska Azeeza tayi da cewa, "To Umma tsoron sa nake ji ne kin daɗe baki faɗa ba, wlh a kan ABUL KHAIRI sai dai idan ki kashe Ni amma bazan taɓa dena son sa ba, kuma na rantse da Allah sai na aure sa".

"Kan kutmar uba.. Ni kike cewa haka ko Azeeza? Wuyan ki har ya kai kaurin da zaki na faɗa min magana son ranki ko?" Sai ta kaɗa kai kawai tana ci gaba da tankaɗen garin ɗan waken ta

Kakar su dake zaune a bakin ƙofan ta duk tana jin abubuwan dake faruwa tace, "to ban da abin ki Sulaima mene ne aibun ta don ta so ɗan uwan ta? Ina ganin ai bata da wanda ya fi shi a yanzu, ke yanzu ba arziƙin ki bane Azeeza ta shiga cikin gidan nan mu dangwali arziƙi?"

"A'a Umma ki dena cewa fa arziƙi na, Ni tunda nake abun hannun Deebiza be taɓa tsole min idanu ba, wannan kuma sai ke da ɗan ki ku ne mayu amma ba Ni ba".

Shiru kawai Kaka tayi domin ta kasa magana ma, ta san abinda ya fi haka ma Umma Sulaima zata faɗa mata tunda bata gaji mutunci ba, iyayin ta ne ma yasa har ta tsulmiya musu baki a kan zancen su

Azeeza dake bakin rijiya zaune tana cuɗa wankin ta ta ɗago kai tana fito tare da dariyan shaƙiyanci tace, "Kaka kema me ya kai ki yin mata magana kin san ba shiri kuke yi ba? Ni dai tunda kina goyan baya na kawai idan Baba ya shigo ta faɗa mishi kika ga zai min faɗa, to ki ɗau mataki akai shi ne kawai abinda zaki iya min".

"To ai shikenan, bari ya shigo ɗin".

Dogon tsaki Umma Sulaima taja tana hararan Azeezan sai dai bata ce komi ba taci gaba da abinda take yi.


      Suna a haka sai ga Uncle Sani ya shigo gidan

Babu wanda ya fara magana sai Azeeza da cewa, "Baba dama ina so muyi magana ne".

"To ƴar Baba Ina jin ki lafiya dai ko?" Yayi maganar yana dakata wa daga shiga ɗaki

"Baba a kan maganar ABUL KHAIRI ne, Ni gaskiya har yanzu na kasa haƙura da shi". Sai kuma ta soma hawaye tana ci gaba da faɗin, "haba Baba ya za'a yi ace ya yi aure amma a kasa sanar dani har sai da na dawo? (Dayake ta je Jigawa wajen ƙanwar Baban ta Halisa) Ni wlh Baba wlh na kasa cire sa a raina, ina ƙaunar sa, idan ba'a aura min shi ba na rantse da Allah zan bi duniya".

"To ka ji ko Sani sai kayi me yiwuwa tun kafin ɗiyar ka ta bi duniya, idan kuma hakan ta faru wlh Ni da kai ne". Inji Kaka kenan cike da fushi

"To Umma ya kike so inyi kina ganin dai yanda mutanen nan suka ci mana mutunci, wanda ba don Allah ya so ba da tuni ita Azeezan tana can a garƙame a gidan kaso an ɗaure ta a kan laifin da ba ita ta aikata ba, ƙiri-ƙiri Deebiza ta nuna mana bambanci a tsakanin mu, yo dama tun ba yau ba na san da haka ba mutunci ne da ita ba, tana ganin ta fi ƙarfin mu shiyasa, taya kike ganin ma zata bari ɗan ta ya auri ɗiya ta tunda ita ƴar matsiya ta ne? Gwara ma tun wuri ki haƙura tunda dai shi yayi aure hakan zai fi miki kwanciyar hankali".

Kuka sosai Azeeza ta saki tana miƙe wa tsaye tace, "yanzu Baba ka fi so in bi duniya a kan kaje ka nema min auren sa? Ni na yarda wlh zan zauna da shi ko mata uku ne da shi".

Umma Sulaima zagi ta ƙunduma mata tana faɗin, "saboda ke mara hankali ne mara tunani ina kika taɓa jin uban yarinya ne zai je neman aure gidan na miji? Kuma da kike cewa zaki bi duniya dama a kanki farau ne? Ai kafin ki yi nima nayi kinga kuwa tarihi sai ya maimaita kansa".

A lokacin Kaka ta fashe da kuka tana cewa, "kaico na wlh! kaicon hali na!! ki yafe min Deebiza tabbas alhakin ki bazai taɓa rabuwa da Ni ba, ga shi yanzu na cuci kaina na fitar da ke gidan ɗana kin je kin auri wanda ya fi shi, ƙazafin da muke miki kuma gashi shi Sani ya auro mana alaƙaƙai ta gurɓata mana gida, wai uwar arziƙi ne take cewa ɗiyar ta taje ta shiga duniya? Sani ka cuce mu wlh". Ta sake fashe wa da wani sabon kukan tana face majina

Umma Sulaima tace, "Oho dai can ta matse miki, in dai Ni ce na zame muku ɗuwawu dole ku zauna da Ni, kuma da kike ce min alaƙaƙai ai zamu je ne ya tarar da muje mu".

Shi dai Uncle Sani tuni ya shige ɗaki abin sa don ya san halin su idan suka fara fitinan nan nasu ba bari za su yi ba, shi kanshi Umma Sulaima ba ƙyale shi take yi ba bare yace zai shigar ma mahaifiyar sa, yanzu ne ma kura tayi lafiya.



       Ai kuwa dai ko da ya shige Umma Sulaima bata yi shiru ba sai habaici take yiwa Kaka tana gaya mata magana

Ita ce dai tayi shiru ta ƙyale ta

Azeeza kuwa gurzan wankin ta taci gaba da yi har da saka waƙa a waya jin surutun Umman nata ya ishe ta, ta ƙure ƙara kuwa tana yi tana cashe wa

Sai kuma Umma Sulaima ta koma kan Azeezan sai ƙunduma mata zagi take yi tana la'antan ta

Amma ko ci kanki bata ce mata ba

Dama duk abinda kayi dole za'a maka, Umma Sulaima bata yi la'akari da abinda take ma uwar wasu ba shi ne ɗiyar ta take mata ba. A juri zuwa rafi dai...



          Azeeza na gama wankin ta ta yafa gyale ta bar gidan, kai tsaye gidan Gwaggon su Maria ta wuce, tana shiga ta kwaɗa sallama tana kutsa wa cikin ɗakin su

Ɗiyar ta Ummi dake zaune tana yankan ƙumba a saman kujera ta amsa mata tana cewa, "oh Azeeza idanun ki kenan?"

Sai da Azeezan ta zauna kafin tace, "ke ba wannan ba ina Gwaggon take?"

"Yanzu ta fita ta je kasuwa".

"Ok me kuka dafa yau? Wlh bazan iya cin ɗan wake ba shi Umma tayi mana, kuma Ni ban da kuɗin siyan wani abu".

Ummi na dariya tace, "mu ma nan ai ba wani abu me daɗi muka yi ba, tuwo ne idan zaki ci".

"Eh sawo min, ai gwara shi wlh a kan wancan ɗan waken. Kin san Ni ba na shiri da shi".

"Ai kuwa Ni ina so, bari in aika a amso min rabon ki". Ummin tafaɗa tana fice wa. Kichen ta nufa ta sawo mata a Plate ta dawo ta miƙa mata

Tana zama ƙanwar ta ta shigo ɗakin tana faɗin, "laa Aunty Azeeza ke ce?"

Gyaɗa mata kai kawai tayi don ta rigada ta fara saka loman tuwo

Ummi tace, "yauwa Ruƙayya amso min Ɗan wake mana gidan su Azeeza".

"To Ni kuma fa zaki tsanmin?"

Sai da ta harare ta kafin tace, "Eh".

"A'a ba fa maganar harara bace, don wlh bazan amso ki hana Ni ba".

"Dalla ki je zan baki".

"To shikenan Aunty Azeeza kina shaida ko?"

"Eh".

Daga haka Ruƙayya ta kaɗa kai ta fice.



          Ummi ta kalli Azeezan tace, "Wai ina Yaya Salihi ne kwana biyu ya dena zuwa gidan nan gaba ɗaya. Ko dai yayi tafiya ne?"

"Mtwssw tafiyan ƙaniya! Yana can dai yana sheɗanantan sa, nima yau ban saka shi a idanu na ba domin kafin in tashi ya bar gidan." Azeeza ta bata amsa.

       Ruƙayya na dawo wa da ɗan waken

Ummi ta amshe tana faɗin, "ya naga ɗan waken ɗan mutsulu ko dai kin cinye a kan hanya?"

"Uwar na cinye ne, ki dube Ni da kyau kinga mai a baki na ko a hannu na?" Ruƙayya tafaɗa tana hararan ta

"To gaskiya Ruƙayya sai dai kiyi haƙuri in cinye wannan, kin san na fi ki son ɗan wake kuma bazai ishe mu ba".

"Ni don Allah idan zaki bani ki bani ba na son surutu, riƙe wannan kwanon ki zuba min".

Ummi dai bata ce komi ba ta amsa ta zuba mata kaɗan bayan tayi ƙwafa

Ita kuma ta wafce kwanon tana zama a ɗaya daga cikin kujerun ɗakin da cewa, "gobe ma rana ne ai dani kike zancen".



Azeeza dake kallon Ummi tace, "ara min gyalen nan naki me ruwan madara don Allah".

"Ina zaki je?"

"Uhm gidan Ya ABUL zan je".

"Don Allah fa? Wlh ina ta son Nima in Koma in ga gida tunda ban je ba amma har yanzu ban samu dama ba, da Mama zata dawo yanzu ai da mun tafi tare".

Ruƙayya tace, "nima zan bi ki don nima ina son zuwa".

"A'a ba dai Ni ba, Ni kaɗai nake son zuwa, ɗauko min gyalen in tafi don Allah". Inji Azeezan tana fice wa. Wanke hannu tayi ta dawo, lokacin Ummi ta ɗauko mata gyalen; ta amsa tayi musu sallama ta fice. Kai tsaye gida ta wuce, tana shiga taga ruwa a kan murhu ta ɗauki bokiti ta sake ta kai bayi, ɗakin ta ta koma ta tuɓe kayan ta ta faɗa bayin. Wanka ta sillo ta fito ta koma ɗaki, nan ta soma shirya wa bata damu tayi sallah ba, ita shaf ta manta sai da ta caɓa kwalliya a fuskar ta sannan ta tuna, sai ta taɓe baki a fili tace, "idan na dawo na haɗa da sauran inyi". Tana gama wa ta shirya cikin doguwar riga me hannun fanka, sosai rigan ta ɗauki jikin ta sannan ta matse ta ainun, tayi kyau sosai domin sai maƙiyi zai kalle ta ya kushe ta, dama Azeeza ba baya ba wajen kyau shiyasa take gara kan Samari yanda take so, sai dai duk ba wanda take so ta aura sama da ABUL KHAIRI, ga shi ita kuma ba ta gaban shi ko kaɗan.



       Sai da ta fito zata fice ne Umma Sulaima dake bakin murhu ganin an ɗibe mata ruwa ta soma masifa tana aiko tsinuwa ga duk wanda ya kwashe mata, ai kuwa tana ganin Azeeza ta fito daga ɗaki taci uwar wannan kwalliyan ta tabbatar ita ce sai ta koma kanta tana zagin ta, "shegiya matsiyaciya in zuba ruwa dan ke mara mutunci ne ki ɗebe sannan ki kasa zuba min wani ko?"

Yamutsa fuska Azeezan tayi tace, "kai Umma wai a kan na ɗiba ruwa ne kike ta wannan masifan har maƙota suna jin ki? Shikenan yanzu dai sauri nake yi amma idan na dawo zan zuba miki kar ki damu". Ta taka tayi bakin ƙofa zata fice

Umma Sulaima tace, "Allah yayi wadaran halin ki ke dai, saboda na miji kin zama kamar karya, insha Allahu idan ma kika je sai ya sauke miki baƙin halin nan nashi a kanki".


Bata kula ta ba ta ƙarisa fice wa a gidan, har da saka hannu cikin jakan ta ta ɗauko chewing gum ta jefa a baki ta soma tauna.
🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸

                   *ABUL KHAIRI*

🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸

💧💧 *LABARIN DEEBIZAH RETURN* 💧💧

*MALLAKAR:*✍️
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PARFECT*🧝🏻‍♀️

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞

'''(WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)'''

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

                 *P.W.A*✍️

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Mahaifiya ta Abar alfahari na, Uwata maganin kuka na, I love You so Much Momma_ ❤️




*________________________________*

                   *PAGE 34*

*________* Me Keke napep na sauke Azeeza a bakin Gate ɗin gidan ABUL KHAIRI ta sauka ta biya sa kuɗin sa, ta gyara ma jakan ta zama tayi bakin ƙofan, Nocking tayi kafin me gadi ya leƙo, tace da shi, "Masu gidan na nan?"

"Suna nan. Lafiya dai?"

"Ƙalau. Buɗe min in shiga wajen me gidan na zo".

"Amma Malama ai kin bari in shiga in Yi musu bayani ko?"

Tsaki taja tana hararan sa tace, "dalla buɗe min ƙofa ko ka ga nayi maka kama da masu satan mutane ne?"

"To wa ya sani abu a duhu a dunƙule a baƙin leda?" Shima ya faɗa yana matsa mata a hanya

"Kai Ni fa ba na cike da iskanci, ka kama kanka tun kafin ka shiga gona ta wlh, don billahil lazi sai in maka sanadin da zaka bar gidan nan, banza kawai a jawo".

"Can ta matse miki shegiya". Yayi maganar ƙasa-ƙasa

Ita kuwa dogon tsaki taja tayi ciki abin ta. Tana zuwa bakin ƙofan shiga gidan ta tura ƙofan, amma jin a rufe ne sai ta soma Nocking.


               A Parlour'n Baby CE kawai a zaune tana buga Game da wayan Maimuna

Ita kuma Maimunan tana kichen tana silale musu farar shinkafa da miyan jiya da ya rage, dayake dawowan su kenan shiyasa take son sama musu abinci

Jin ana Nocking da gudu Babyn ta tashi ta nufi ƙofan ta buɗe

Azeeza washe baki tayi tace, "Babyn

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login