Showing 9001 words to 12000 words out of 88313 words
Chapter 4 - ABUL KHAIRI Complete Hausa Novels by Nafisa Ismail lawan.txt
*ABUL KHAIRI*
🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸
💧💧 *LABARIN DEEBIZAH RETURN* 💧💧
*MALLAKAR:*✍️
_NAFISA ISMA'IL LAWAL_
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏻♀️
*بسم الله الرحمن الرحيم*
𝐏𝐄𝐑𝐅𝐄𝐂𝐓 𝐖𝐑𝐈𝐓𝐄𝐑'𝐒 𝐀𝐒𝐒𝐎𝐂𝐈𝐀𝐓𝐈𝐎𝐍🌞
( 𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔻𝔼ℝ𝕊💪)
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
𝗣.𝗪.𝗔✍️
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad UmmuDahirah*👈
_Wannan shafin naki ne Sweetheart, SAFNA ALIYU JAWABI, Allah ya daɗa ɗauka ka ki amin._
*________________________________*
*PAGE* 5
*________* Batool da ta fito daga kichen, jin ana Nocking ta nufi wajen ƙofan ta buɗe, ganin Sagir Abokin ABUL KHAIRI sai ta washe baki ta soma gaishe shi cikin girmamawa
Murmushi yayi mata ya amsa yana shigo wa ciki
"Babu kowa ne a gidan sai ke?"
"A'a suna ciki, ya ABUL ma na ciki ai".
Sagir yace, "Ai na ga motan sa a waje, Mamy fa tana ciki?"
"Eh tana ciki". Ta ba shi amsa idanun ta a kansa
Shima dai kallon ta yake yi, ya sakar mata murmushi yace, "ya dai ƙanwata wannan kallo haka? Ko dai na sauya miki ne?"
Saurin sauke kanta ƙasa tayi tana rufe bakin ta tare da dariya ƙasa-ƙasa
"Uhm tom kira min Mamyn mana mu gaisa".
"To". Tayi maganar da sauri tana juya wa ta wuce
Da kallo ya bi ta har ta shige, sannan ya saki ajiyan zuciya yana ƙarisa wa cikin parlour'n ya zauna.
Tare da Mamy suka fito Parlour'n, ƙarisawa Mamyn tayi wajen Sagir suna gaisawa, ita kuma Batool ta shige ɗakin su
Maimuna dake zaune tana duba book ɗin ta na English; ta ɗago kai tana kallon ta, har ta zauna kusa da ita bata ɗauke idanun ta a kanta ba, sai ma tambayan ta da ta soma yi, "Sister lafiya wannan fara'a haka?"
Wani fara'an ne ya sake tabaibaye Batool, ta saki murmushi tace, "uhm sister babu komi fa".
"Ya za'a yi ki ce babu komi bayan na ganki kina murmushi da fara'a?".
"Babu komi wlh, kawai dai na tsinci kaina cikin farin ciki ne matuƙa tuna wani abu".
Kaɗa kai Maimuna tayi kafin ta mayar da hankalin ta kan Book ɗin ta, kasancewar ta ba me son magana ba shiyasa bata ja zancen ba.
▪️▪️▪️
Ɗakin ABUL KHAIRI ya shiga bayan sun gama gaisawa da Mamy
ABUL KHAIRI dake kwance tun gama wayan sa da Ziyada, ko motsi ya kasa yi sai faman ajiyan zuciya yake sauke wa idanuwan sa a lumshe, duk da kuwa ya ji sallaman Sagir be sa ya buɗe ido ba bare ya motsa
Kusa dashi Sagir ya ƙariso ya zauna gefen gadon; ta wajen ƙafafuwan sa, a tunanin shi barci yake yi don haka ya saka hannun sa ya janye pilown da ya matse a ƙirjin sa
Hakan yasa ABUL KHAIRI buɗe idanun sa ya sauke a kan sa
Murmushi Sagir yayi yace, "lallai ka samu lafiya wannan barci haka? Idanu har sun sauya kala, Kana jin daɗin ka fa aboki".
Shima ABUL KHAIRIN murmushin yayi yana ƙoƙarin tashi zaune yace, "uhm babu barcin da nake yi Aboki, ƙanwar ka ce dai ta caza min kai, ina tunanin gaskiya wata rana sai dai ku zo ku ga gawana idan baku aura min ita ba".
Sagir sheƙewa yayi da dariya yana tafa hannu yace, "iyeee abun har ya kai haka kenan? Lallai kam kana ruwa kusa da kada tsundum".
Hararan sa ABUL yayi yana saka hannu ya ƙwace pilown sa yace, "kai dai ka sani, Ni dai wlh na gaji ko ku bani ita ko in mutu".
Dariya Sagir kawai yake tuntsura wa, ganin yanda ABUL ɗin ya kwaɓe fuska tamkar zai yi kuka
"Allah kuwa da gaske nake yi Aboki, meye shawara? ina buƙatar aure da gaggawa, sannan kuma Ni bazan iya auren wata ba sai Ziya.. love, kai ka san matsala na, abun ya kai maƙura tunda har Mamy ta fahimta, kuma ka san idan ta ga babu sauƙi zata iya tada zancen wancan ƙwailan, musamman idan naje mata da maganar ma". Sai yaja numfashi yana sake sauya fuskar sa na tausayi, yaci gaba da faɗin, "amma kuma idan da maganar Ziya.. love na san bani da damuwa, zan iya shawo kan matsalan duk idan naje musu da maganar aure nake so, tunda ina da wacce zan nuna musu".
Sagir dake kallon sa yace, "haka ne Aboki, ko Ni ban goyi bayan ka je da maganar auren ka yanzu ba, sabida idan sun amince maka da maganar Ziyada, to ka ga shi Dady ya ce, "ba yanzu ba", hakan zai jawo maka matsala, don wlh maganar mutumiyar ka za'a tado dashi". Yaƙarishe maganar da dariyan shaƙiyanci
Pilown hannun sa ABUL KHAIRI ya wurga masa yana sakar masa wani kallo tamkar idanun sa za su faɗo ƙasa, yace, "ɗan iska uban wa yace maka mutumiya ta ce ita? Ka kiyaye Ni wlh, kasan hali na fa".
Shi dai Sagir be dena dariyan sa ba, har da ƙware wa sabida tsaban dariya
Hakan ya ƙular da ABUL yaja dogon tsaki yana cewa, "ka ga fa ban son iskanci idan zaka bani shawara ka bani, Allah zaka fitar min a ɗaki".
Rufe bakin sa Sagir yayi sabida wani dariyan da ya taho masa, daƙyar ya iya buɗe baki cikin dariyan yace, "to to Aboki Na dena, Allah ya ba ka haƙuri ko? Yanzu wani shawara kake so in ba ka?".
Shiru ABUL KHAIRI yayi be tanka sa ba, sai ma wani kallo da yake aika masa dashi
Matse bakin sa yayi yana haɗiye dariyan sa yace, "to shawaran da zan ba ka Aboki na, Ni a gani na ba wata matsala bane idan ka jira ta nan da two years ɗin, abinda zaka riƙa yi kawai ka nemi maganin sha'awa ka riƙa sha ko zaka ji sauƙi, sannan ku dena wannan banzan soyayyan shan mintin da kuke yi, hakan ke jawo maka matsala, kuma wlh duk wayon ka Aboki a kan baza ka kusance ta ba sai kun yi aure uhmmm wata rana abun da kake gudu; aikata zina shi ne zai biyo baya, to wai shin ma meye Bambancin abinda kuke yi da zinan? Kar ka manta ana zinan ido, ana yin na chart.."
Katse sa ABUL KHAIRI yayi da faɗin, "Ka ga Malam ba wa'azi na kira ka kayi min ba, yaushe ma ka zama malamin da zaka zo kana maganar?"
Sagir yace, "ai ba sai na zama Malami sannan zan maka wa'azi ba, kai ma ka san hakan babu kyau, kafi kowa sanin hakan, Ni dai shawara na ba ka kamar yanda ka nema, in ka so kayi amfani dashi; in kuma ka so ka zubar a ƙasa kabi ta kai ka tattaka, ya rage na ka. duk ranan da ka jawo mana abun kunya wlh babu ruwana, kar ma ka nuna ka san Sagiru".
Lumshe idanuwan sa ABUL yayi, tabbas ya san maganar abokin sa gaskiya ne, amma kuma a yanzu sun rigada sun yi nisa ga wannan halayyan, domin hakan ne kaɗai ke rage masa raɗaɗin wutar ƙauna da sha'awar da yake yiwa Ziyada, bazai iya juran yana ganin ta kullum be iya taɓa ta ba, itama haka, abun dai da yaga zai iya kawai shi ne bazai taɓa sanin ta ɗiya mace ba har sai da igiyoyin sa uku a kanta...
"Kai tunanin me kake yi haka ina magana kana ji na?"
Maganar Sagir ɗin ne ya sanya sa buɗe ido yana kallon sa
Sagir ya sake faɗin, "tashi mu yi sallah ana kira".
Toilet Sagir ya soma shiga ya ɗauro alwala, kafin shima ABUL ya shiga yayi nasa, a tare suka fito suka nufi masjid, ana idar da sallan magriba suka fito, a hanya suka haɗu da Abba suka yo gida gaba ɗayan su, sai dai shi Abba ciki ya shiga yabar su a waje, sai da suka ɗan tattauna kafin Sagir ya hau motan sa ya bar gidan, shima kuma ABUL ya shige ciki
A Parlour ya tarar da Abba suna zaune shi da Mamy da Amir, zama yayi gefen Amir yana sauraron hiran da su Abba da suke yi, har aka kira sallan isha'i kafin su sake fice wa su uku zuwa masallaci.
Da suka dawo time ɗin har an shirya dinner a kan leda a tsakar parlour'n, zama suka yi suka soma cin abincin.
Bayan sun kammala Mamy ta kalli ABUL dake latsa wayan sa yana tura wa Ziyada text, kasancewar ya ji wayan ta akashe, tace, "Babana gobe idan Allah ya kai mu su Maimuna suka dawo school, za su je gidan gona su ɗibo Fruits sabida na gida ya ƙare, kuma ka ga har yanzu ban samu keey ɗin fannin ba, sai ka bani naka muyi amfani dashi za su ɗibo min".
Ɗago kai yayi yana kallon ta yace, "a'a Mamy kibar su kawai, zuwa goben zan je da kaina sai in ɗibo".
"To babu matsala, ɗazu Zainab ta faɗa maka saƙon uncle ɗin ka kafin ta tafi?"
Girgiza kansa yayi yace, "a'a bata faɗa min ba".
Gajeren tsaki Mamy tayi tace, "kai! wani lokacin Zainab shirmammiya ce, ce min tayi akwai saƙon da Abbas ya aiko ta zata ba ka, to Ni dayake ina aiki ban bi ta kanta ba, ai sai ka kira a waya kaji meye saƙon".
Batool tace, "ai ta faɗa min kafin ta tafi, tace kaje gobe wajen aikin Uncle yana son ganin ka".
Wani kallo ya aika mata dashi yace, "dama kina ji kenan ake magana?"
Sauke kanta tayi ƙasa cikin tsoro
Abba dake jin su yana aiki a cikin computer'n sa yace, "tashi ka je kar ka zare wa ɗiyata ido, ba yanzu kuke maganar ba kuma ta baku amsa?"
ABUL dai be ce komi ba ya tashi ya wuce ɗakin sa
Ita kuma Mamy cewa tayi, "Abban su ai ta san halin yayan na su, da taji ana maganar meyasa bata faɗa ba?"
Batool tace, "wlh ban ji ku bane, muna can muna magana da Maimuna".
"To ya wuce dai abar maganar". cewar Abba, kafin ya mayar da idon sa kan Baby da tazo ta maƙale masa tana kallon abinda yake yi, sai da ya shafa kanta yace, "Autana baza ki kwanta bane kin san da school gobe? Kar kuma a tashe ki kina ƙi".
"Abba Ni ban jin barci".
"To yi zaman ki, saura inji an kawo min complain an tashe ki kin ƙi tashi".
Murmushin jin daɗi tayi tana sake shigewa jikin sa ta yanda zata kalli computer'n da kyau.
A haka dai suka zauna suna ta hira jefi-jefi gaba ɗayan su, don itama Mamy tuni ta saka Amir ya ɗauko mata Laptop ɗin ta a cikin ɗaki
Maimuna da Batool kuma kallo ya ɗauke musu hankali, sai Amir ne dake kwance kan kujeran yana buga Game.
▪️▪️▪️▪️▪️▪️▪️▪️▪️▪️
Ƙarfe 08:30pm Ziyada ta dawo gida, ana buɗe mata Gate ta shiga Shima Sagir ya shigo da tashi motan gidan, time ɗin da ta fito daga motan shima ya fito yana bin ta da kallo, gaishe sa tayi,
Ya amsa yana faɗin, "Daga ina haka my sister da daren nan?"
Murmushi ta saki tana ɗan sosa kai tace, "Yaya daga wajen Bie mana nake".
Kafe ta da ido yayi yace, "faɗa min gaskiya, ABUL KHAIRIN da muke tare yanzu da magriban nan muka rabu, shi ne kuke tare?"
Turo baki tayi cike da borin kunya tace, "sorry yaya nayi maka ƙarya, ina tare da Rahy ne".
Ɗan tsira mata ido yayi na wani lokaci kafin yaja numfashi yace, "mu je to, but ki dena fitan dare kina jina ko Dear?".
"Insha Allahu yaya, wannan ma buƙatar hakan ne". Ta amsa mishi tana bin bayan sa
A tare suka shiga parlour'n, sai dai babu kowa
Kallon sa tayi tace, "Yaya bari in Kira maka Momyn maybe tana ciki ne".
"No bar ta ta fito, nima ba yanzu zan wuce ba".
"Ok bari in shiga to in watsa ruwa". Ziyada ta faɗa tana yin upstairs
Da kallo yabi ta har ta ƙule wa ganin sa, kafin ya sauke ajiyan zuciya yana lumshe idanun sa, shi kaɗai yasan me yake ji, tabbas idan yaci gaba da zama a haka watarana zuciyar sa zata iya bugawa, dole ya san mafita a kan halin da yake ciki, amma kuma taya? Wannan hanyan ce ya kasa samun sa bare ya magance abinda ke addabar sa shekara da shekaru.
▪️▪️▪️
Ziyada na shiga ɗakin ta tayi saurin dafe ƙirjin ta, domin duk a tsorace take jin ta, ji take yi tamkar za'a iya gane abinda ta aikata a yau ɗin, tafiyan ta ta dai-dai ta kafin ta ƙarisa bakin gadon ta ajiye jakan ta, a dai-dai time ɗin ne wayan ta tayi ƙarar shigan text, ciro wa tayi ta duba, sai ta ga ABUL ne ya turo mata kalaman soyayya kamar yanda ya saba akoda yaushe, karanta wa tayi sannan tayi masa reply a kan "zata kira sa ya bata time tana wani abu ne". Ajiye wayan tayi ta shiga Toilet, nan ta sake haɗa ruwan wanka me ɗumi ta yanda zai gasa mata jiki sosai ta rage raɗaɗin da take ji, shiga tayi cikin ruwan ta lumshe idanuwan ta tana jindaɗi na ratsa ta, nan ta afka tunanin da yaja ta time me yawa, sannan daga bisani tayi wanka ta fito ta shirya cikin riga da wando na Barci, ta fice a ɗakin
Koda ta isa parlour time ɗin tuni Sagir ya bar gidan, sai Momy da Dady ta gani zaune suna hira, da sauri ta ƙarisa wajen sa don baza ta iya yin gudun da ta saba ba, ta rungume sa tana faɗin, "Dady i miss You so Much".
Dariya yayi yana shafa kanta yace, "i miss You more than you Babyna, yaushe kika dawo ne? Momyn ki ta ce, "kin fita".
Zama tayi tana dariyan farin ciki tace, "tare muka shigo da Yaya Sagir ai, na je wajen Rahy ne".
"Ok Masha Allah Baby na, to ya school ɗin ki, ana dai karatun ko?"
"Eh Daddy sosai ma, ka tambayi Momy ma, ba na wasa ai".
Murmushi Momy tayi tace, "ai ba sai na faɗa masa ba, shima ya shaida hakan, Babyn mu me ƙoƙari ne ba ta wasa da karatun ta".
Dady yace, "yauwa good girl, dama fatana kiyi karatu sosai Baby, hakan zai faranta min rai sosai, shiyasa ma yanzu na sanjo miki mota don ki samu farin ciki kamar yanda kike faranta min".
"Wow! Da gaske Daddy?" Tayi maganar tana ware idanun ta tare da rufe bakin ta da hannayen ta
"Ƙwarai kuwa Baby, but zuwa nan da two days zai iso insha Allahu".
Rungume Dadyn tayi cikin tsantsan farin ciki, ta dinga mishi godiya, su kuma suna mata dariya. Daga ƙarshe dainning suka nufa suka zauna cin abinci, suna yi suna hira cike da nishaɗi.
🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸
*ABUL KHAIRI*
🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸
💧💧 *LABARIN DEEBIZAH RETURN* 💧💧
*MALLAKAR:*✍️
_NAFISA ISMA'IL LAWAL_
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏻♀️
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞
( 𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔻𝔼ℝ𝕊💪)
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
𝗣.𝗪.𝗔✍️
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga mahaifiya ta Abar Alfahari na, Uwata maganin kuka na. I love You so Much Momma._ ❤️
*________________________________*
*PAGE 6 & 7*
*________* Washe gari ƙarfe 01:00pm. ABUL KHAIRI ya tashi daga aiki, sosai ya ƙosa ya isa gidan gonan sa yaje ya haɗu da Ziyadan shi, sabida ji yake yi tamkar ya shekara be ganta ba, tun faɗan da suka yi shekaran jiya rabon shi da ita, wanda hakan be taɓa faruwa ba, don a rana sai su ga juna sau uku ma, kuma kusan ko yaushe suna tare, idan basu a gidan gona, to zai bi ta school ɗin su, wajen aikin sa ne kaɗai ba ta zuwa sabida Companin mahaifin sa ne, kuma shima yana aikin a ciki, idan taje dole wata rana zai ji labarin yana kawo mata, ya san halin mutanen Abban shi, akwai ƴan sa ido sosai.
Ƙarfe 01:40pm. Ya ƙarisa gidan gonan, Gate man na buɗe masa ya kutsa hancin motan ciki, a inda Ziyada tayi parcking shima ya ajiye nasa
Dama ita tuni ta iso tunda yau ba school take dashi ba, tana zuwa ta ɗaura musu girki me rai da lafiya sai tashin ƙamshi yake yi, kasancewar ta me tsananin ƙaunar girki shiyasa take zaƙe wa tana koya, babu girkin da Ziyada bata iya ba, domin har makarantar koyan girki tana zuwa, duk idan ta yiwa ABUL KHAIRI girkin ta, sai yaji tamkar babu wanda yafi shi sa'ar samun mata, domin Ziyada ta haɗa abubuwa ta ko ina, komi da komi da yake nema wajen mace ya samu a wajen ta, idan dai biyayya ne tana masa sabida tsananin ƙaunar da take masa, sabida shi zata iya barin ko me yace, dai-dai gwargwado tana da tarbiyya duk da iyayen ta sun shagwaɓa ta, sannan uwa uba tana da tsantsan kyawu matuƙa, wanda ko wani namiji ya kalle ta sai ya rasa nutsuwar sa, ga shi ita ɗin ƴar gayu ce ta ko ina, tana da son kwalliya sosai akwai ta da tsafta, ga iya wanka, ga iya girki, kaii komi dai a wajen sa ta iya ne.
Tunda ya buɗe ƙofan parlour'n ƙamshin girkin ya doki hancin sa, sai kuma runguman da Ziyada tayi masa ya biyo baya, nan da nan shima jikin sa na rawa ya ƙanƙame ta sabida jin tattausan ni'imar jikin ta a jikin sa, yanda suke ƙwaƙume da juna zai tabbatar da cewa sun matuƙar kewar juna, be sake ta ba sai ma ɗaukan ta da yayi zuwa kan kujera ya zauna yana aza ta ajikin sa, nan ya soma gaya mata kalamai masu tsananin tsada da babu wanda ya isa ya ji su face ita, wanda suke ƙara dulmiyar da ita a kogin shauƙin ƙaunar sa, tana sake jin babu wanda ya kai ta Sa'a na samun abokin rayuwa, ji take yi tamkar ta jawo ko wani second, ko wani minti, ko wani awa; ko wani rana, sati, Wata, zuwa shekaran da ya rage musu, ta mallaki magudanan numfashin ta, wanda idan babu shi a cikin rayuwan ta, to, tabbas babu ita ne, domin tana ji a ranta muddin ta rasa ABUL KHAIRI ta dena numfashi, ƙaunar sa ya rigada ya mamaye jiki da ɓargon ta, ya zama jinin jikin ta.
Tun a kan kujeran soyayyan tasu ta sauya salo tamkar yanda suka saba, daƙyar suka iya tashi suka shiga wanka, a tare suka yi suka fito suka haye gado suka ci gaba da nuna wa junan su ƙauna tsantsa, wanda babu algus a cikin ta, kowa so yake yi ya nuna wa ɗan uwan sa yafi sa iyawa, kuma yafi sa buƙatan sa.
Sun shafe fiye da awa suna abu ɗaya ko gajiya