Showing 81001 words to 84000 words out of 88313 words

Chapter 28 - ABUL KHAIRI Complete Hausa Novels by Nafisa Ismail lawan.txt

baiwar Allah Maimuna saboda tsorata har kuka tayi jikin ta sai rawa yake yi

Har ya tafi ɗaki sai kuma ya dawo yace, "idan bata rufe masa baki ba sai ya gasa ta a gidan nan, kuma idan tayi wasa babu inda zata je ko sama da ƙasa zata haɗe ita da gidan su har abada." Daga ƙarshe ma sanya ta yayi ta biyo sa ɗaki tayi masa tausa

Abun tamkar a mafarki ta ji zancen sa, sai dai kuma a yanda take a tsorace dashi babu musu ta bi shi ɗakin jiki na rawa ta soma masa abinda ya saka ta. A taƙaice dai bata baro ɗakin ba sai washe gari, tunda take a gidan bata taɓa kwana a ɗakin nasa ba sai yau. Yau ido buɗe ya amshi haƙƙin sa a wurin ta babu maganar ma tuna wa da raini

Bazan iya misalta muku yanda Maimuna ta kasance a lokacin ba. Har suka tafi ta kasa haɗa ido dashi tsaban tsananin kunya da ganin abun da tayi tamkar a mafarki, ko kaɗan ko kusa bata taɓa tunanin tana da matsayin ma da ABUL KHAIRI zai iya haɗa ɗaki da ita ba bare har ya haɗa shimfiɗa da ita, amma yau kuma abun sai ya zo mata a matuƙar bazata har ta kasa ma tantance anya shi ɗin ne ko kuwa wani ne?.




            Gidan Mamy suka je don su yi musu sallama, duk ta kasa sakin jikin ta gaba ɗaya sabida kawai abun da ya faru da ita a daren jiya, gani take yi kamar ma kowa ya san abun da ta aikata, ko magana ba ta iya yi

Mamy har dai ta gaji ta cire baki ta tambaye ta, "ko bata da lafiya ne?"

Amma ina ta kasa bata amsa don daƙyar ta iya girgiza mata kai idanun ta a ƙasa ko kallon su ba ta iya yi

Shi kuwa ABUL KHAIRI kallon ta yayi yana taɓe baki a ransa yana mamakin halin ta, kwata-kwata bata waye ba, shi yana son mace wayayyiya ba irin Maimuna ba, halin ta yana ɗaya daga cikin abubuwan da ya tsana a rayuwar sa, kullum ka ganta kamar wata muna-fuka, magana ma wannan yana mata wahalan yi.





           Duk yanda Batool tayi da tsokanar ta itama ɗin sai dai ta gaji ta kyale ta, ta zama tamkar sokuwa kamar wata za'a yanka ta a gidan.




             Zuwa biyu suka kama hanyar Kaduna. Har suka kai ko ƙwaƙƙwaran motsi ba ta iya yi a motan. Shima ko bi ta kanta be yi ba bare ya kalle ta.




         Dayake can Kadunan sun san da zuwan su, koda suka isa an yi musu tarba me kyau kamar za'a goya su domin sun ji daɗin zuwan su ba kaɗan ba

Be wani jima ba yace, "zai tafi".

Shi ne Ummu ta sanya ta ta je su yi sallama

Har bakin motan ta je ta same sa sabida a lokacin har ya shiga mota suna magana da Aliyu

Aliyun ya fara hango ta shiyasa ya saki dariya yana cewa, "oh su Maimuna me miji. wai kin zo rako sa ne?"

Duƙar da kanta tayi tana murmushi don ta kasa magana ganin har ABUL KHAIRIN kallon ta yake yi

Shi kuwa taɓe bakin sa yayi yana kallon Aliyun yace, "ka dena tsokanar min mata kaji ko? Idan ba haka ba ka san hali na".

Still dariya Aliyu yayi yana faɗin, "sorry bro baran ƙara ba, Ni kaga na tafi ma, ka gaishe da su Mamy don Allah".

"Babu komi za su ji".

Hannu ya ƙara basa suka gaisa kafin ya wuce gida

ABUL KHAIRIN ɗago kai yayi ya kalle ta ganin har yanzu tana a inda take ta ƙi ƙariso wa, sai da ya ja gajeren tsaki yace, "me kike jira kuma a wurin?"

Ɗago kai tayi ta kalle sa, sai ya ballara mata harara, hakan yasa tayi saurin ɗauke nata idon a kansa tana matsowa wurin sa, sai dai ta kasa ma magana don bata san ma ta ina zata fara ba

"Idan baki da abun faɗa Ni zan wuce".

Hannayen ta take ta mulmula wa daƙyar ta iya buɗe baki still kanta na ƙasa tace, "dama Ummu ce tace in zo muyi sallama".

"Ok idan bata ce ba baza ki zo ba kenan?" Yayi maganar idanun sa a kanta

Shiru tayi

Shima sai yayi shirun kawai yana jingina kansa a motan tare da rufe idanuwan sa

Sun fi mintuna goma a haka babu wanda ya sake magana. Ba ma ta ɗago kai ba bare ta san a halin da yake ciki domin kunyan abun da ya faru da su jiya yasa gaba ɗaya ko kaɗan ba ta iya haɗa ido dashi sai a tsautsayi, tsananin kunyan sa da take ji yanzu ya ninku sosai.


          "Wai me kike jira ne?" Yayi maganar a fusace bayan da ya ɗago kai yana kallon ta

Murya na rawa tace, "kayi haƙuri don Allah".

Yanda tayin ne sai ta ba shi tausayi, gaba ɗaya tsoro ya nuna a tattare da ita har ɓarin jiki take yi. Be san meyasa take jin tsoron sa sosai ba, yana ga kamar hakan ne yasa ba ta iya sakin jiki da shi, shi kuma gaskiya bazai iya zama da ita a haka ba, shiyasa yanzu ɗin ya ɗan sassauta murya yace da ita, "babu addu'a?".

Har ɗago kai tayi ta kalle sa saboda jin muryan sa a matuƙar sanyaye kamar ba shi ba

Murmushi ya sakar mata

Wannan dalilin ne yasa ta ɗan ji sanyi a ranta, murya a raunane tace, "Allah ya tsare hanya Allah ya kai ka lafiya".

Hannu yasa ya riƙo nata ba tare da ya amsa ba yace, "ɗago ki kalle Ni".

Kasa ɗago wa tayi

"Ɗago mana ƙanwata wai meye na kunyan ne? Ina ce Ni mijin ki ne?"

Hoi! Maimuna tamkar ta nitse a ƙasa take ji a wannan lokacin, sai dai babu yanda ta iya dole ta ari jarumta sosai kafin ta iya ɗago wa ta kalle sa, bata bari sun haɗa ido ba ta sake mayar da kan ƙasa

Shi fa abun nata ma ya fara basa dariya, shiyasa yace, "ta zagaya ta shiga motan".

Babu musu tayi abun da yace

Hannun ta ya sake riƙo wa yace, "ta ɗago ta kalle sa".

A wannan time ɗin ma daƙyar ta ɗago ido ta kalle sa, still dai ta ƙi haɗa ido da shi

Shi kuma sai ya juya sosai yana facing ɗin ta tare da kama fuskar ta da tafukan hannayen sa duka ya ɗago kanta sosai ta yanda dole ko tana so ko bata so sai ta haɗa ido dashi

Ai kuwa tana saka idanun nata a cikin nasa ta mayar da su ta rufe don ta kasa jure wa

"Wai ke ina wasa da ke ne baza ki buɗe ido ki kalle Ni ba? Yau dole sai mun yi kallon ƙuda kafin na bar ki ki koma, idan kuma ba haka ba sai dai mu koma Kano a yanzun nan tare dake".

Jin abun da yace yasa ta buɗe ta zuba masa idanuwan nata bata da yanda zata yi

Guntun murmushi ya saki yace, "lallai ne yarinya kina da aiki. Amma meyasa kike jin kunya na ne haka?"

Bata iya basa amsa ba sai sauke kwayar idon nata ƙasa tayi domin ta kasa jure irin wannan kallon da yake mata, ji take yi tamkar wani abu yana jawo ta izuwa cikin idanun nasa, kuma duk soconni bugun numfashin ta na ƙara ƙarfi kamar zai faso ƙirjin ta ya fito tsaban yanda take ji, tafukan hannayen ta da ta tamke su duk sun jiƙe sabida tsoro

"I said if I'm talking to you don't keep me quiet."

"Kayi haƙuri". Tafaɗa da rawan murya

Kallon ta kawai yake yi be sake cewa komi ba yana examines how beautiful her face is. Sai kuma ya matso da fuskar sa ya haɗe bakin su waje ɗaya ba tare da tayi tunanin hakan ba. He had been sucking her mouth for a long time before releasing his breath his eyes on her face which had already ta rufe idanuwan ta ruf ko motsin kirki ba ta iya yi, domin har yanzu yana rike da fuskar ta ya ƙi saki. "Ki kula min da kanki, ban da magana da maza ko waye ne har a cikin family ɗin ki, so be careful". Sai ya shafa fuskar nata har saman idanuwan ta yana zagaye su kafin ya sake kai bakin sa yayi kissing ɗin idanuwan sannan ya koma kan kujeran sa sosai yana ajiyan numfashi. Ɗan dafe kansa yayi na ɗan wani lokaci

While ita kuma tuni ta ja jikin ta ta sake cure wa wuri ɗaya, yanda ta shiga shock da abinda yayi mata ko yatsan ta ba ta tunanin zata iya ɗaga wa because of kunya

"Ki sauka zan tafi kar nayi dare". Yayi maganar a kasalance bayan ya mayar da idanun sa kanta

A hankali ta sanya hannu ta buɗe motan ta fice, ko juyo wa bata yi ba ta shige cikin gidan su

Shi kuma ƙofan yake ta bi da kallo ya kasa tafiya, ya jima a haka kafin ya ja motan ya wuce.















_Kun rage Comments. Ko a tafi hutu ne tunda naga kun gaji. Nima ɗin haka?. Bani da lafiya ina buƙatar addu'ar ku._
🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸

            *ABUL KHAIRI*

🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸

💧💧 *LABARIN DEEBIZAH RETURN* 💧💧

*MALLAKAR:*✍️
             _NAFISAT ISMA'IL LAWAL_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PARFECT*🧝🏻‍♀️


*بسم الله الرحمن الرحيم*


*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞

'''(WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)'''

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

           *P.W.A*✍️


*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈


            *SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Mahaifiya ta Abar alfahari na, Uwata maganin kuka na, I love You so Much Momma_ ❤️


_Masoya na na nesa dana kusa, waɗanda na sani da waɗanda ban sani ba, ina matuƙar ƙaunar ku sosai, Wannan shafin naku ne domin Allah. Allah ya bar mu tare. Amin._






*________________________________*

              *PAGE 41*

*________* Maimuna da ta shiga parlour'n su Aliyu da Shureim ta gani, Ummu kuma na ɗaki. Tana shigo wa Shureim ya taso da gudu ya rungume ta

Aliyu kuma tuni ya soma tsokanar ta

Itama kuma sai murmushi take yi ta samu wuri ta zauna kafin tace, "Haba yaya ka dena don Allah".

"Babu wannan zancen, idan kin ga na dena to sai dai kin bar gidan nan ne, Kaii! amma wlh kun dace sosai kin ga yanda a ɗan lokaci ƙanƙani kika sauya? Wooo Yaya ABUL ya iya kiwo alƙur'an".

Buga ƙafa ta soma yi zata yi masa kuka

Sai yayi dariya yace, "to kiyi kukan mana ai ga Shureim nan sai yayi miki dariya babu ruwa na".

Kallon Shureim ɗin tayi da cewa, "Wai haka Baby na?"

Girgiza mata kai yayi yace, "a'a Ni bazan miki dariya ba, kuma zan haɗa shi da Baba ne idan ya dawo".

"Yauwa sweet Baby na. Bani hannu mu kashe".

Ya miƙa mata hannun kuwa suka kashe suna dariya

Aliyu yace, "Ni Ko Shureim? Ai zamu haɗu ne idan ta tafi bazan riƙa zuwa da kai shan ice cream ba".

"Kaji nima ai zan siya maka ko?"

Gyaɗa mata kai yayi

Tace, "yauwa Baby na, Ina Ummu ne?"

Shureim yace, "tana ɗaki".

"To bari in je in dawo akwai tsaraban da zan baka kaji?"

Ai ko tsalle ya fara yi

Ita kuma ta tashi tana murmushi ta shige ɗakin Ummu

Ummu na zaune a bakin gadon ta tana shafa mai kasancewar daga wanka ta fito. Bayan Maimunan ta shigo ne take tambayar ta, "har ABUL KHAIRIN ya tafi ne?"

"Eh ya tafi tun ɗazu".

"Ok ki je kema ki ɗibi ruwa a kichen kiyi wanka kafin a kira magriba, famfon Toilet ɗin ya lalace ne sai ki ƙara min zan yiwa Shureim".

"To". Tace da ita tana fice wa

Da kallo ita kuma ta bi bayan ta, a ranta tana me farin cikin ganin ɗiyar ta cikin kwanciyar hankali, tabbas ba kamar yadda suka zata bane da alamu suna zaune lafiya tunda ga shi har sakamako ya nuna, domin tun kallon farko ta gane tana da ciki. Murmushi kawai tayi tana ci gaba da shafa mai ɗin ta.





▪️▪️▪️▪️▪️▪️▪️▪️▪️

             ABUL KHAIRI ba shi ya shiga Kano ba sai takwas da rabi, kai tsaye gida ya wuce yayi wanka ya rama sallolin da ake bin sa, daga shi sai Singlet da gajeren wando ya fito ya shiga kichen ya haɗa tea ya koma Parlour ya zauna. Tea ɗin yake kurɓa but hankalin sa yana wani wurin, tun yanzu har ya soma jin zuciyar sa da gangan jikin sa suna kewar Maimuna, shi kansa mamakin hakan yake yi domin tun sanda ya baro wurin zuciyar sa ta hana sa sukuni. Shin meyasa kwana biyun nan take yawan tsaya masa a rai ne? Meyasa ko wani abun yake yi sai ya riƙa tunano ta zuciyar sa na fasalta masa yanda take da yanayin ɗabi'ar ta, kyawun ta da komi nata? Har yana jin tamkar zuciyar sa tana son kamuwa da soyayyar ta, amma kuma shi ya san SO ɗaya ce, kuma ita ya yiwa Ziyada, ba ya tunanin akwai wata ɗiya mace da zai sake ƙauna makamanciyar yanda ya so Ziyada, shiyasa ya kasa gane abun da yake ji a game da ita, idan har so ne, kenan ana iya ƙaunar mutum biyu a lokaci ɗaya? Wata zuciyar nasa tace, "tabbas ana iya wa, idan kuma ba ayi kai za'a fara ta kanka, abubuwan da kake ji a game da ita iri ɗaya ne da yanda kake ji a kan Ziyada, ta yiwu rashin Ziyada a gare ka yasa duk wani ƙauna da kake mata yake son juye wa izuwa ga Maimuna". Cup ɗin hannun sa ya ajiye yana me jingina kansa da kujeran tare da lumshe idanuwan sa, a ransa ya furta, "kenan dai zai iya kamuwa da son Maimuna kamar yanda ya yiwa Ziyadan shi? Amma taya?" Gefe na zuciyar sa tace, "sabida ta cancanta domin ita matar ka ce". Numfashi ya ja bayan ya buɗe idanun nasa, sai dai be sake motsa wa ba saboda tunanukan da suka sha masa kai. Sai kuma can ya ɗauki wayan sa da zummar kiran Maimuna domin ya kasa jure wa, muryan ta kawai yake son ji, ga kuma tsananin buƙatar ta da yake fama da ita, amma kuma sai ya tuna be da Numban ta, be san sanda ya saki wayan a saman kujeran ba yana kwantar da kansa yayi shiru abun sa

Wayan nasa ne tayi ƙara saboda kiran da Rahina tayi masa

Daƙyar ya iya ɗago kansa don ganin wa ke kira? Arba da yayi da sunan Rahina sai ya ja dogon tsaki cike da tsananin takaicin ta a zuciya, har wayan ta katse be ɗauka ba, wani ta sake shigo wa, nan ma be ɗaga ba har ta katse sannan yasa hannu ya kashe wayan gaba ɗaya, ya miƙe da wayan a hannu yayi ɗaki. A wannan ranan daƙyar barci ya suri ABUL KHAIRI, yanda zuciyar sa ta ƙwazzabe sa da tunanin Maimuna har yake ji bazai taɓa iya jure rashin ta har na tsawon sati biyu ba, ba don dole Abba yayi masa ba babu yanda za'a yi ya barta ta je can uwa duniya ta bar sa, haba ai wannan cin zalun ne ma a ganin sa. Shiyasa washe gari da ya tashi duk ya rasa walwalan sa, be san meyasa ba har kuzarin sa ya rasa kawai harkokin sa yake yi ba don yana jin daɗin jikin sa ba. Yana tashi a wurin aikin sa kuwa gidan Mamy ya yiwa tsinke, zuwan sa ne ma yasa ya ɗan samu natsuwa sabida sun haɗu da Sulaiman suna ta hira.




           Har dare yana gidan be tafi ba, duk kan su suka haɗu a Parlour suka ci abincin dare, bayan sun gama kuma suka koma hira, a nan ne ABUL KHAIRI ya cewa Batool, "ta ɗauko masa wayan Mamy". zuwa tayi ta ɗauko ta miƙa masa. A nan ya laluba ya cire Numban Maimuna

Duk a tunanin sa babu wanda zai fahimci abin da yayi, nan kuwa tuni Mamy ta harbo jirgin nasa, haka kawai zuciyar ta ta bata Numban Maimuna yake nema, sai kawai tayi murmushi tana kallon sa tace, "kuɗi zaka sanya min ne Baba na da kace a ɗauko maka?"

Murmushi yayi yace, "a'a wane Ni Mamy? Ai ke ce milonia, mu kam sai dai mu roƙa a wurin ki".

Dariya suka yi gaba ɗaya har su Abba da suke jin su

Sai ya miƙa wa Batool ɗin wayan yana me miƙe wa tsaye da cewa, "zai tafi". Sallama yayi musu sannan ya fice ya wuce gida. Sai da ya gama shirin sa ya kwanta kafin ya soma laluban Numban Maimuna.








               *********


              Lokacin Maimuna tana shirin kwanciya itama, tana saka rigan barcin ta ta ji wayan ta tana ring, tsaya wa tayi tana nufan wajen gadon ta ta ɗauki wayan dake saman gadon ta duba, ganin baƙuwar number sai bata ɗauka ba ta mayar ta ajiye sannan ta ƙarisa sanya rigan, sai ta zauna a gefen gadon a lokacin aka sake kiran nata, wannan karon ɗaukan wayan tayi bayan ta kara a kunne, sai dai bata yi magana ba

Daga can shima ABUL KHAIRI shiru yayi kawai yana sauke numfashi tare da jin sanyi a ransa jin ta ɗauki wayan. Ganin baza ta yi magana ba sai yace, "ba kya magana ne?"

Da sauri ta ciro wayan tana duba wa saboda jin muryan ABUL KHAIRI, zuciyar ta bata yarda ba sai da ta sake mayar wa tace, "Hello wane ne?"

"Wano ne, baki iya magana bane nace?"


"Na iya". Ta furta cikin sanyin murya da tsananin mamakin jin shi ne dai ya kira ta. "Ina wuni?" ta sake faɗa da sauri bata jira yayi magana ba

Sai da ya mirgina kwanciyar sa kafin yace, "Ƙalau. Ya mutan gidan?"

"Lafiya lau".

Sai kuma shiru ya biyo baya. While itama tana tunanin ta yanda aka yi ya samu Numban ta har ya kira ta

Shi kuma yana tunanin abun da zai ce mata, domin sai yanzu ma tunanin nasa ya dawo jikin sa tare da mamakin ya aka yi ma ya nemi wayan nata? Numfashi ya sauke kana yace, "yanzu me kike yi?"

Tace, "babu komi zan kwanta ne".

"Ok". Ya furta yana yin shiru

Kamar shuɗewar mintuna biyar babu wanda ya sake magana illa sauraron hucin numfashin su dake fita a hankali

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login