Showing 84001 words to 87000 words out of 88313 words
Chapter 29 - ABUL KHAIRI Complete Hausa Novels by Nafisa Ismail lawan.txt
da suke yi
Tuni shi ya lumshe idanun sa yana ci gaba da sauraron numfashin ta dake dukan kunnen sa yana sake saukar masa da kasala. "Wai ke baki iya hira bane?" Yayi maganar a matuƙar sanyin murya
Daga can Maimuna saukar da kai ƙasa tayi kamar yana gaban ta, ta soma wasa da rigan jikin ta ta kasa furta komi, domin jin ta take yi a wani baƙon yanayi da bata taɓa tunanin kasancewar ta ba
"Duk ranan da na kama ki zaki sha mamaki na, I'm telling you don't keep quiet when I'm talking but ba kya jin magana ta".
"Kayi haƙuri don Allah bazan sake ba". Tayi maganar cikin rawan murya
"Shi kenan ya wuce. Ki kwanta kiyi barci, da safe zan kira ki".
Tace, "to".
Daga haka ya kashe wayan.
Ta kasa motsa wa daga inda take zaune sabida sosai abubuwan da ABUL KHAIRI yake mata daga shekaran jiya zuwa yau suka saka ta cikin wani irin yanayi, har mamaki take yi anya shi ne? Duk ya gama sauya mata kamar ba wanda ta sani ba. Tunanin sa yasa ta kasa kwanciya ma, ta jima a zaune a wurin daga ƙarshe ma sai ta koma ta kwanta tana me matse filow fuskar ta ɗauke da murmushi, "kar dai ace maganar Batool ne zai tabbata gaskiya? Ko dai ya fara son ta ne? Maybe ta fara shiga zuciyar sa". Da wannan tunanin yasa zuciyar ta tayi fari ƙal, one by one take tuna abun da ya faru a daren da zata taho, da kuma sallaman da suka yi jiya da zai tafi. A taƙaice dai daƙyar ranan Maimuna tayi barci saboda tunanin ABUL KHAIRI.
Haka shima a fannin sa ya gaza barcin, ganin zai ɓata wa kansa lokaci sai ya tashi ya soma jero salloli har zuwa asuba kafin ya samu yayi barcin, zuwa takwas ya tashi ya yi shirin sa, a lokacin ne ya ɗauki waya ya sake kiran Maimuna
Lokacin suna Parlour suna karin safe duk kan su, dayake suna kan dainning ne wayan kuma ta ajiye a can kan kujeran Parlour, ta ji wayan na ƙara, tuni zuciyar ta ta bata shi ne shiyasa tana rawan jiki ta miƙe ta nufi wurin
Su Ummu kuma sai suka bi ta da kallo babu wanda yayi magana sai Aliyu da ya ɗaga murya yana cewa, "Ƴar ƙanwata Yaya ABUL ne ya kira? Ki kawo mu gaisa to idan kin gama".
Baba yace, "kai dai kayi ƙaton banza Ali, ka bar yarinyata ta huta a gidan nan duk ka gama saka mata idanu fa".
Ita dai Maimuna tuni kunya yasa ta shige ɗaki da sauri, kamar yanda tayi zaton shi ne ya kira ta shi ɗin ne kuwa. Bayan ta ɗauka ita ta soma sallama
Ya amsa mata sallaman cikin cool voice ɗin sa
"Ina kwana yaya?"
Sai da ya ɗan ɗau soconni kafin ya amsa ta yana tambayar mutanen gidan?
"Lafiya lau suke suna gaishe ka, har da Yaya Aliyu".
"Hmmm ina amsa wa. Ya kwanan baƙunta?"
Maimuna idanu ta ɗan buɗe da mamaki ta furta, "baƙunta kuma?"
"Eh mana".
A karo na farko ta dara sabida yanda maganar nasa ya bata dariya
While lumshe idanuwan sa yayi sautin dariyan nata yana hautsina masa zuciya. A hankali yace, "why are you laughing?"
Shiru tayi, sai kuma ta tuna kashedin sa tayi saurin faɗin, "babu komi".
"A'a ban yarda ba sai kin faɗa".
"Allah yaya babu komi". Tayi maganar cikin shagwaɓa
Wani irin yarrr ABUL KHAIRI ya ji daga saman kansa har ƙasan tafukan ƙafafuwan sa, da sauri ya sami wuri ya zauna a gefen gadon sa yana me sakin numfashi a hankali a hankali. Tsit yayi be sake furta komi ba
Ita kuma jin shiru sai tace, "Hello Yaya".
"Umm". Ya furta cikin wani irin murya
Itama kasa magana tayi saboda yanda muryan nasa ya saukar mata da kasala, sai ta koma wasa da kwalliyan rigan ta tana sauraron bugun numfashin sa da a yanzu ya sauya sosai
"Tell me you miss me?" He spoke in a very low voice
Take ta lumshe idanuwan ta tana me kwanta wa a kan gadon, ta kasa ma magana sabida jin abin da ya tsarga mata daga cikin zuciya zuwa ilahirin jikin ta, Suddenly her heart rate changed
"You are silent?"
Cike da tsananin kunya har tana rufe idanu tace, "Yes I miss You".
"Really?"
Gyaɗa masa kai tayi, sai kuma ta tuna ba ya ganin ta sai ta amsa masa da, "um".
Numfashi ya sauke kafin yace, "ok in zo in ɗauke ki gobe kin fi son zama da Ni ko?"
Tsit tayi tana sake ƙudundune fuska
Cikin sanyin murya ya kira sunan ta, "Maimuna".
"Umm".
"Ko kar in zo ɗaukan ki?"
"Eh".
Numfashi ya sauke be sake cewa komi ba, sai kuma can yace, "wato ba kya son zama dani ko?"
"A'a ina so". Tayi maganar da sauri
"Ok amma kin ce kar in zo? Why?"
"Babu komi".
"Shikenan. Zan tafi Office Kar in yi late, take care". Daga haka ya kashe wayan be jira cewar ta ba
Ita kuwa kasa motsa wa tayi daga kwancen da take, haka kawai take ji gefe na zuciyar ta ta shiga ƙunci da kashe wayan da yayi, bata so hakan ba, ji take yi kamar su dauwama suna tare a haka. While wani sashi na zuciyar ta kuma tsananin farin ciki ne ya cika ta, tana ji tamkar babu wanda ya kaita farin ciki a wannan time ɗin, gaba ɗaya ta kasa sukuni sai juye-juye take yi tana faman tunani, ta rasa wani irin yanayi ne take jin haka a wannan lokacin. Ta fi ƙarfin mintuna goma da gama wayan nasu amma bata tashi ba. Sai da Shureim ya shigo ɗakin ya kira ta, wai in ji Ummu, "idan ta gama wayan ta fito haka nan". Shi ne fa ta tashi tabi bayan sa. Duk ta tsargu daga kallon da Ummu take mata, domin a lokacin ita kaɗai ce a zaune a parlour'n; Aliyu da Baba sun fita
"Ki zauna ki ƙarisa karin naki lokaci na ƙure wa kar su ji ki shiru kin zo kuma baki shiga kin gaishe su ba".
"To". Kawai tace tana wuce wa kan dainning ɗin, abincin ta ci gaba da ci har ta gama kafin ta taso ta je ɗaki ta ɗauko gyalen ta, babban mayafi ne baƙi ta sanya tun daga saman kanta, jikin ta kuma sanye da riga da skert na lees me ruwan madara da ratsin baƙi-baƙi na kwalliya da aka yi, sun yi mata kyau kayan sosai domin ba ƙaramin sake haska ta suka yi ba, ga shi yanda ta ɗan yi ɓul-ɓul da ita tayi fresh kowa ya kalle ta sai ya sake kallon ta babu hassada
Ummu tace, "su tafi da Shureim ya raka ta".
Tare suka fice suka wuce gidan Kakannin su wajen Mahaifiyar Baba. Dayake mahaifin sa ya rasu ita kaɗai ce a gidan sai kuma kusa da gidan da sauran dangin su suke, can kuma babban gida ne da Yayyin Baba da ƙannin sa suke ciki da iyalan su. Gidan Umman suka soma shiga
Ganin su yasa tayi farin ciki matuƙa domin basu da labarin zuwan nata sai yanzu da Baba suka fice yake faɗa mata. Tayi murna matuƙa musamman da ta ga yanda ta sauya gaba ɗaya har da ɗan tsaraban ciki da ta ƙyalla ido ta gani. Hakan yasa take ta haba-haba da ita ta kawo mata wannan ta kawo mata wancan na abubuwan ƙwalama da su tsofaffi ba a raba su da shi
Sosai kuwa Maimuna ta ji daɗin hakan, shiyasa ta ci ta ƙoshi kamar ba yanzu tayi karin safe ba, to ranta ya biya musamman kwaɗon zogalen da ta bata, shi har a leda tayi guzurin sa. Ta fi awa ɗaya a gidan kamar baza ta tafi ba ta shantake sai hira suke yi da Umma suna kwasan dariya. Sai daga baya suka wuce babban gidan nasu tabi sasa-sasa tana gaishe su
Ai kuwa sun yi murna da ganin ta, kowa yace, "Maimuna.. Maimuna.."
Ita dai sai murmusawa take yi cike da kunya irin nata
Yayinda yaran gidan duk inda ta saka ƙafa bin ta suke yi, kun san Amare da farin jini bare ita ta jima ba ta garin sun yi kewar ta matuƙa, har da sa'annin ta na gidan suke biye da ita, kowa ya kalle ta sai ta ba shi sha'awa kamar ba ita ba sosai tayi musu girma a idanu ta sake sauya kamanni
Shiyasa da ta tashi tafiya har gidan su suka bi ta. A can suka ƙarisa zaman su suna tare da Maimunan har dare sannan suka tafi.
Washe gari kuma sai ta wuce gidajen su ƙannin Baba da ƴan uwan sa mata. Haka dai Maimuna tayi ta biye-biyen dangi. Har gidan su Aunty Rufaida da Aunty Naana duk ta je ta yi musu wuni. A can ne ma Aunty Naanan ta sake zaunar da ita tana ta koya mata dabarun zama da miji da yanda zata riƙa sace zuciyar mijin ta da kuma tattalin sa, musamman yanda ta ga ta sauya don itama har ta gane tana da shigan ciki shiyasa ta ɗibi kayan gyaran ta duk ta zuba mata a jaka tayi mata bayanin yanda zata riƙa amfani da su, ta kuma koya mata wasu daga cikin kayan fruit da yanda zata riƙa sarrafa su tana sha don amfanin kanta
Dayake Maimuna ta san halin Aunty Naana shiyasa ko tari ba tayi, ta natsu sosai ta fahimci komi da ta koya mata.
Satin ta ɗaya a wannan lokacin kullum sai sun yi waya da ABUL KHAIRI, har wani sabo ne ya shiga tsakanin su domin ɗayan su ba ya iya barci be ji muryan ɗaya ba, gaba ɗaya sun kamu da tsananin soyayyar junan su amma babu wanda ya amince da hakan.
Ana saura kwana huɗu ta cika sati biyun ne ta wuce Zaria gidan Aunty Fatima shima a can zata yi mata kwana biyu before ta koma Kaduna, daga can kuma ABUL KHAIRI zai zo ya ɗauke ta.
_Idan da yiwuwar gobe zaku ji Ni to.. har yanzu ina bukatar addu'ar ku ina fama da matsanancin ciwo sosai. I do this for your joy because of my waiting you do. Sai kun sake ji na._
🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸
*ABUL KHAIRI*
🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸
💧💧 *LABARIN DEEBIZAH RETURN* 💧💧
*MALLAKAR:*✍️
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_
*SARAUNIYAR TSOKANAR PARFECT*🧝🏻♀️
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞
'''(WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)'''
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*✍️
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Mahaifiya ta Abar alfahari na, Uwata maganin kuka na, I love You so Much Momma_ ❤️
*________________________________*
*PAGE 42*
*________* Kwanan Maimuna biyu a Zaria kafin ta koma Kaduna. Sanda ta cike sati biyu sai ga ABUL KHAIRI da ƙarfe 10:20am. Ya dira a gidan
A lokacin itama har ta gama shirin ta don shi kaɗai take jira tunda ya sanar mata ta shirya ɗin
Suna Parlour ita da Ummu ya shigo. Sai da ya zauna kafin suka gaisa da Ummu tana tambayar sa hanya
Maimuna da tun shigowan sa ta mayar da kai ƙasa sai a lokacin ta gaishe sa
Ya ɗago kai yana kallon ta, amsa mata yayi idanun sa ƙyam a kan ta sabida mugun sauya masa da tayi, tayi wani irin cika sosai tayi luwai-luwai kamar wacce ya shekara be gan ta ba, a ransa yace, "ko dai Ummu wani abun take bata ne?"
While Ummu kuwa farin ciki ne sosai ya sake cika ta ganin gaba ɗaya hankalin ABUL KHAIRIN ya tafi ga ɗiyar ta, wannan ya nuna mata tabbas Maimuna tana a cikin zuciyar sa, hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba. Ita ce ta kalli Maimunan ganin ta kasa tashi bare ta ɗauko mishi ko ruwa ne, sai tace, "haka zaki bar sa babu wani abun? Ki tashi ki ɗauko mishi drinks mana".
"To". Tace mata tana tashi ta wuce gaban Fridge ɗin nasu
Har ta je ta dawo ta kawo masa a gaban sa kallon ta yake yi ya kasa ɗauke ido a kanta. Bayan ta zuba masa ya amsa ya sha kafin ya kalli Ummun yace, "ina su Baba ne?"
"Sun je wajen aiki, amma dai yanzu zai dawo don ya ce idan ka zo in Kira sa kuyi sallama".
Jinjina kansa yayi yana ɗan sake ɗago kai ya saci kallon Maimuna
Itama duk ta takure saboda sosai ta ji a jikin ta yana kallon ta, ga tsananin kunya da ya rufe ta duk da ta saka mayafin ta a jiki domin a shirye take tsab tafiya kawai za su yi.
Babu jima wa Baba ya dawo suka gaisa da ABUL KHAIRIN, basu wani jima ba suka yi musu sallama suka kamo hanyar Kano
Tunda suka shiga mota babu me magana haka yake ta tuƙin nasa. But jefi-jefi yana mayar da hankalin sa gare ta amma ya kasa furta mata komi
Ita kuwa sai wasa take yi da yatsun hannun ta, kaɗan-kaɗan kuma tana jefa idanuwan ta saman kwalta tana kallon hanya.
A haka har suka shigo Kano, kai tsaye gidan su Mamy suka wuce
Sun yi murnan ganin su ba kamar Mamy ma, sosai taji daɗin ganin Maimunan ta sake sauya wa hakan ya sake tabbatar mata tabbas akwai ciki a jikin ta.
A can suka wuni sai dare suka wuce gida
Kai tsaye Maimuna ɗakin ta ta wuce ta soma wanka saboda gajiyan mota, gaba ɗaya ta gama gajiya ga mugun barci da take ji, shiyasa tana gama wanka ta saka kayan barcin ta tabi lafiyan gado tunda sun ci abinci a gidan Mamy.
Shiru-shiru ABUL KHAIRI yana tunanin zai ganta a Parlour amma ya ji ta tsit, dole ya taso ya biyo ta ɗakin ya hange ta har tayi nisa da barcin ta ma. Tsaya wa yayi kawai yana kallon ta ya kasa koma wa. Sai da ya ɓata lokacin sa a tsaye a wurin kafin ya juya ya wuce ɗaki, wanka yayi ya shirya ya wuce ɗakin nata cox he would never tolerate her because he missed her so much
Maimuna na barci ta ji mutum a jikin ta, bata ma gama tantance a magagin barci take ba taji muryan sa yana raɗa mata magana, dole ta wartsake a barcin. But she could not, so they spent the night together sai da asuba ya bar ɗakin.
Haka rayuwa taci gaba da gudana, a ɗan ƙanƙanin lokaci rayuwar auren su tana neman sauya wa domin abubuwa da dama yanzu sun sauya a zamantakewar su. Tun Maimuna tana jin kunyan sa sosai tana ganin abubuwan ne tamkar a mafarki, sai dai kuma a haka take jure wa tana yin duk abun da zai faranta masa rai, duk abinda ta san yana so tana yi domin farin cikin sa, bata da buri a yanzu sama da su kasance a haka, shaƙuwa me ƙarfi ta shiga tsakanin su, ba sa iya jin daɗi idan ba sun ji ɗumin juna ba, ko a yaushe suna a tare, ko a Office yake yana ƙoƙarin ya ga ya kira ta sun yi waya, ko yana son hana zuciyar sa amma ba ta hanuwa dole sai ya ji muryan ta kafin yake samun sukuni, haka itama, shi a yanzu sosai ya fahimci ya kamu da ƙaunar Maimuna, domin duk abubuwan da yake ji a game da ita the same abubuwan da yake ji ne sanda yake soyayya da Ziyada, tabbas ya yarda son ta yayi masa kamu a lokacin da be taɓa tsammani ba, shiyasa ya saka a zuciyar sa da ita zai rayu, zai koya mata yanda yake son matar sa ta kasance, duk wani kunya nata da rashin waye wa yana iya bakin ƙoƙarin sa wajen ya ga ta dena ta saki jiki sosai da shi, sai dai kuma abun a jinin ta yake, amma ita kanta ta fahimci ABUL KHAIRI yana son rayuwar wayewa shiyasa dai-dai gwargwado tana iya bakin ƙoƙarin ta koda daga baya zata koma tana jin kunyan sa ne, idan har zata faranta masa to zata yi
Duk wani sauyi da ya samu yanzu a tattare da matar sa shi ne dalilin da ya fara sanja akalan tunanin sa ga Rahina, yana ga kamar bata da abun da zai so ta da ya fi wadda Maimuna take dashi, shiyasa be ga amfanin auren ta ba, duk da dai har yanzu ya kasa yakice ta a jikin sa, wani ɓangare nasa yana jin son tarayya da ita, amma kuma kaso mafi yawa a zuciyar sa mugun haushin ta yake ji, shiyasa a yanzu ya tashi tsaye sosai yana sallan dare da roƙon Allah ya tsayar masa da zuciya wuri ɗaya, yanzu haka har yana samun damar gaya mata magana wanda a baya be samun hakan, kullum cikin faɗa suke da ƙorafin, "ta ishe sa".
Ita kuma sauyin da ta gani ne yasa ta sake bazama neman malamai duk dai ta siye zuciyar ABUL KHAIRI, ta zama tamkar karya a kansa. Ana haka tsautsayi ya gifta mata garin zuwa wajen Malamin ta tayi hatsari, take a nan ta mutu ko shurawa bata yi ba
Shi kansa ABUL KHAIRI be da labarin mutuwar nata domin tunda ya samu ta dena kiran sa ya goge numbobin ta. Ta fannin Azeeza ma tuni ya taka wa Uncle Sani birki domin yanda ya sako shi a gaba da sai ya auri Azeeza, shi kuma ya ce, "wlh bazai taɓa auren ta ba". Duk yanda aka juya sa ya ce, "bazai aure ta ba matar sa kaɗai ta ishe sa rayuwa". Har su Mamy da Abba sun shiga maganar sabida yanda maganar take so ta zama tsiya raga-raga, amma firr ya ƙi
Azeeza kuwa hakan yasa ta gudu ta shiga duniya tunda uban ta ya kasa mata abun da take so, baƙin cikin rasa ABUL KHAIRI ya hana ta sukuni shi ne ta gudu, tana ga kamar hakan zai sa ya ji tausayin ta a nemo ta ya aure ta
But shi