Showing 78001 words to 81000 words out of 88313 words
Chapter 27 - ABUL KHAIRI Complete Hausa Novels by Nafisa Ismail lawan.txt
DEEBIZAH RETURN* 💧💧
*MALLAKAR:*✍️
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_
*SARAUNIYAR TSOKANAR PARFECT*🧝🏻♀️
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞
'''(WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)'''
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*✍️
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Mahaifiya ta Abar alfahari na, Uwata maganin kuka na, I love You so Much Momma_ ❤️
*________________________________*
*PAGE 39*
*________* Tun asuba da Maimuna ta tashi daga barci bata koma ba sai da ta gyara ko ina na gidan, kafin bakwai har ta gama komi nata har Breakfast sai ta koma kawai ta kwanta barci ko wanka bata samu tayi ba, sosai take jin barci a idanuwan ta kamar wacce bata samu tayi ba.
ABUL KHAIRI kuma zuwa takwas da rabi ya fito cikin shirin sa na farar jallabiya da gajeren wando itama fara a ciki, ya zauna a Parlour Yana ɗan kalle-kallen ta inda Maimuna zata fito, jin shiru sai ya miƙe ya wuce kan dainning, ganin an shirya komi sai ya zauna yayi serving ɗin kan sa ya hau karya wa yana tunanin, "me ya hana ta fito wa?" Sai wata zuciyar nasa ta raya masa, "ƙila fa ba ta jin daɗi ne," da sauri ya miƙe yana barin wayan sa a wurin ya nufi ɗakin nata, tura ƙofan yayi da sallama a bakin sa ya shige. A kan gado ya ganta sai sharan barci take yi ta ƙudundune kanta da pilow ta matse, sai ya taka ya nufi gaban gadon yana bin ta da kallo, be yarda da ko lafiyan ta lau bane tunda ba ya ganin tana koma wa barci sai ya saka hannun sa ya taɓa wuyan ta ya ji ko da zafi ne
A dai-dai lokacin ne ta farka tana ware idanuwan ta a kansa, sai da ta ɗan sake rufe su ta sake ware su sabida ta tabbatar shi ɗin ne, sanin shi ne yasa tayi saurin tashi zaune kamar wacce aka tsikara
Shi kuma sai ya ƙi ɗauke idanun sa a kanta yana me bin ta da kallo kawai, yayinda fuskar sa a sake kaɗan
Gaishe shi ta hau yi bayan ta sauke kanta a ƙasa
Be amsa ba sai ya tambaye ta, "lafiyan ki kuwa?"
Gyaɗa masa kai tayi
"Baki da baki ne?"
Cikin rawan murya tace, "lafiya ta lau".
Shiru ya ɗan yi kana kuma sai ya juya ya fice
Da kallo ta bi sa don ta kasa ma gane tunanin me zata yi. Tana nan zaune ita bata koma barcin ba ita kuma bata tashi ba, sai da ta shafe kamar mintoci a ƙalla goma kafin ta miƙe ta shiga bayi don yin wanka. Bayan ta fito ta shirya cikin riga da wando na Pakistan me ruwan zuma da kalan kuka, simple make-up ta yiwa fuskar ta don ba gwana bace wajen kwalliya, sai ta saka room slippers ta ɗauki wayan ta ta fita Parlour
Har a lokacin ABUL KHAIRI na zaune a saman dainning yana karya wa, sai dai yanzu ɗin waya yake yi da Rahina. A dai-dai lokacin da Maimuna ta fito yana dariya ne idanun sa suka faɗa kanta. Kasa ɗauke ido yayi a kanta har ta iso cikin parlour'n ta samu wuri a kan sofa ta Zauna don ta kasa ƙarisa wa wurin bare tayi Breakfast ɗin. Kasa ci gaba da wayan yayi saboda hankalin sa sosai ya rabu gida biyu, sai kawai yayi mata sallama yana ajiye wayan yaci gaba da abinda yake yi, can kuma sai ya ɗago kai fuska a ɗaure ya kalli inda Maimuna take zaune yace, "me kike yi a wurin baza ki zo ki karya ba?"
Tashi tayi kawai ta taho da sanyin jikin ta, a hankali taja kujera ta zauna a wanda yake facing ɗin sa. Sai da tayi ƙoƙarin daidaita nutsuwar ta sosai kafin ta ɗaga hannayen ta dake faman rawa ta soma serving kanta
Shi kuma da mamaki yake kallon ta har ta gama abin da take yi, kamar bazai yi magana ba kuma can sai ya dube ta yace, "wai ke in tambaye ki Ni dodo ne a wurin ki?"
Da sauri ta ɗago kai tana kallon sa sabida jin maganar a bazata, yanda ya zuba mata ido sai tayi saurin mayar wa zuciyar ta na faman buga wa kamar zata faso ƙirjin ta, ta kasa ma ba shi amsa don bata san me zata ce ba
Tsaki ya ja ya tashi ya bar wurin
Bata sake motsa wa ba har sai da ta dena jin motsin sa, kana ta ɗago kai a hankali kamar mara gaskiya tana kallon cikin parlour'n, ganin babu shi sai ta sauke ajiyan zuciya ta soma karyawan. Bata san meyasa ba take rasa nutsuwar ta duk idan yana wurin ta, duk yanda ta so ta riƙa daure wa kasa wa take yi, ta rigada ta sanya wa kanta tsoron shi, ko a wani irin yanayi ne ba ta jure wa. Bayan ta gama ta kwashe komi ta wuce da su kichen tayi wanke-wanke sannan ta fito
A lokacin ne ABUL KHAIRI ya fito har ya sauya shiga ya bi ƙofa ya fice ba tare da ya kalle ta ba
Ita kuma ganin haka yasa ta wuce saman dainning ɗin ta ɗauki wayan ta sai ta dawo parlour, sai da ta kunna t.v kafin ta zauna ta soma latsa wayan ta ta kira Ummu. Sun jima suna waya har da su Shureim da Yayan ta Aliyu kafin ta kashe ta kira Mamy, itama sun jima suna wayan tana ta tambayan ta, "ko akwai wani matsalan?" Amma tace mata, "a'a". Sai da suka yi waya da kowa, kafin ta koma ta kira Batool ta wayan ta suka soma hira cikin nishaɗi, a nan Maimunan take ce mata, "ya kamata yau ta zo tayi mata weekend".
Dariya Batool ɗin tayi tace, "a'a Ni da gidan ki ai sai da babban dalili sabida tsaro, kin san halin yaya ABUL haka kawai bazan riƙa zuwa masa gida ba wlh."
Cikin marairaice murya Maimuna tace, "don Allah ke kuwa haba Batool, wlh babu abinda zai miki ba ya nan ma ya fita, kuma na san bazai dawo ba ƙila sai yamma".
"Ni dai bazan zo ba gaskiya. Idan gani na kike so kiyi ai gobe akwai school zamu haɗu."
"Yanzu baza ki zo ba?"
"Eh". Tafaɗa tana mata dariya
"Shikenan." Tace tana kashe wayan nata cike da haushi. A fili kuma ta furta, "nima wata rana zan rama insha Allahu". Kwanciya tayi taci gaba da kallon ta a tashar Hijira T.v. Dayake Film ɗin Indon ƙauye suka saka shiyasa ya ɗauke mata hankali sai kwasan dariya take yi. A haka ta wuni currr har sai da ta ga ƙarshen Film ɗin. Ƙarfe ɗaya suka gama sai ta wuce tayi sallah ta shiga kichen. Tun tana yin girkin cikin sauri kar ABUL KHAIRI ya dawo har dai ta koma yi a natse. Zuwa biyu da rabi ta gama ta shirya a saman dainning taci nata sannan ta wuce ɗakin sa, gyara masa tayi da sauri da sauri don kar ma ya zo ya ganta. tana gama wa ta wuce ɗakin ta, books ɗin makarantan ta ta ɗauka ta soma revision tunda exams ma ya kusa. Tana nan zaune ta jiyo ƙaran buɗe Gate, hakan ya tabbatar mata ya dawo kenan. Karatun ta taci gaba da yi.
*******
ABUL KHAIRI na shigowa parlour'n kai tsaye ɗakin sa ya wuce, ya rage kayan jikin sa sannan yayi wanka ya sanya farar Singlet da three qwatern wando, computern sa ya ɗauka ya fita Parlour, zama yayi a saman sofa ya buɗe ya soma aiki. Yana nan zaune but hankalin sa ya rabu gida biyu yana jiran ko zai ga wulƙawan Maimuna. Jin shiru ya sa shi tashi tsaye yana jan tsaki ya nufi ɗakin ta, ko me ya tuna sai ya juya kawai ya wuce dainning ya zauna yayi serving ɗin kansa. Ba ya son ko kaɗan ya matsanta wa kansa da tunanin ta shiyasa gwara ya saba wa kansa da yin abu babu ita.
Yana gama wa Parlour ya koma ya ci gaba da aikin sa, har sai da aka kira sallan la'asar kafin ya tashi ya mayar da computern ɗaki ya ɗauro alwala ya fice.
A wannan daren ma ABUL KHAIRI haka ya sanya wa Maimuna maganin barci me ƙarfi a cikin fresh milk. Suna cikin cin abincin ne sai ya aike ta ɗakin sa ta ɗauko masa wayan sa bayan wayan na cikin aljihun wandon sa. Tana tashi ya buɗe na gaban ta ya sanya mata, dayake ta ɗauko nashi daya nata ɗaya
Sai da ta jima tana duba wa bata gani ba kafin ta dawo ta sanar masa
Ce mata yayi, "ta zauna taci abincin ta".
To dayake a takure take sai ta tsakula bata ci sosai ba ta tashi zata tafi ko taɓa fresh milk ɗin bata yi ba
Ya mayar da ita yace, "dolen ta taci abincin tunda ba asaran hatsi zata riƙa masa ba. Kullum ta dafa abinci sai ta ƙi ci sai kace shi ne uban masu kuɗi da zata riƙa masa albazaranci".
Maimuna dai babu yanda ta iya haka ta zauna taci gaba da cin abincin. Tsautsayi yasa ta ɗauki Fresh milk ɗin ta kora dashi, sosai ta sha kafin ta gama cin abincin
Shi kuma tuni ya tashi ma a wurin ya koma Parlour ya barta don ta sake
Ai ko tas ta shanye before ta tashi, dayake baki na son kwaɗayin. Bayan ta gama ta rufe coolarn ta kwashe komi ta kai kichen ta wuce ɗaki. Wanka tayi ta shirya cikin rigan barcin ta ta haye kan gado sai barci.
Haka ma wannan dare ABUL KHAIRI ya sake kusantan ta ba tare da sanin ta ba. Duk a tunanin ta wani mafarkin ne ta sake yi sai dai nauyin barci ya sa ta kasa tantance a gaske ne komi ke faruwa. Tun daga wannan ranan ABUL KHAIRI duk idan yana buƙatar ta babu ruwan sa sai dai ya ɗura mata maganin barci ya je gare ta
Al'amarin na bata mamaki domin tun tana jin canji a jikin ta har dai tazo ta saba da yanayin nan, kullum kuma sai ta roƙe Allah a kan ya yaye mata wannan matsalan amma abu sai ci gaba yake yi har ta gaji ma yanzu ta soma saba wa.
Da haka rayuwa taci gaba da gudana ga shi har lokacin jarabawan su ya zo na fast time.
****
Fannin Uncle Sani har gida ya zo ya sami ABUL KHAIRI da zancen auren Azeeza
Amma shi furr yace, "bazai iya auren ta ba".
Uncle Sani yace, "wlh sai ya aure ta muddin yana so ya zauna lafiya, dole ne sai ya auri Azeeza don be isa ya wulaƙanta masa ɗiya ba, gwara ma ya shirya tun yanzu lokaci kawai ya ɗiba masa sai ya aure ta".
Maimuna duk tana jin abun dake faruwa daga ɗakin ta saboda ɗaga murya yake yi, a zuciyar ta sai da ta ji babu daɗi gaba ɗaya a ranan sai ta rasa nutsuwar ta sabida maganar ya tsaya mata a rai, idan ABUL KHAIRI ya auri Azeeza ya rayuwar ta zata koma? ta san tabbas akwai matsala baza ta iya kishi da Azeeza ba, inuwar su ma ba ta zama wuri ɗaya bare su zauna lafiya. Haka kawai ta ji sam duk ta damu
Shi kansa ABUL KHAIRIN ya ga ta sauya masa amma be tambaye ta ba tunda har yanzu ba wai shiga harkan ta yake yi ba, iyakan ya ci abincin ta idan ya ga dama ya amsa gaisuwar ta, idan yana da abinda zai saka ta ya sanya ta tayi mishi, sai kuma idan dare yayi ya je kamar muna-fuki yayi bidirin sa da ita ya gyara duk wani abu da zata iya zargin sa ya waske ɗaki, a haka kullum yake domin shi har yanzu ya kasa tausan zuciyar sa ya je wurin ta da yardan ta ya amshi hakƙin sa, gani yake yi ba son ta yake yi ba shi kuma bazai iya zama ya lallaɓa ta ba. Kuma har yanzu suna tare da Rahina suna soyayya, tun tana nacin ya turo su yi aure har ta gaji sabida ya ce mata, "ta bari sai auren sa ya ɗan kwana biyu sannan su yi." Duk da ya rasa mene ne ya ja hankalin sa da har yake soyayya da ita, shi fa a cikin zuciyar sa ko kaɗan ba ya ƙaunar ta amma kuma yana jin zai iya auren ta, ko yana son yayi mata wulaƙanci ya rabu da ita da zaran ya ji muryan ta yake kasa wa tunda tuni har yanzu sai bibiyan malamai take yi don dai ta mallaki zuciyar sa, sai dai Allah da ikon sa yana iya bakin ƙoƙarin sa wajen addu'o i da sallan dare wanda hakan ke sa wa duk wani asiri da take mishi ba ya tasiri sosai a jikin sa.
********
Sai da su Maimuna suka gama jarabawa kafin ya kai ta gidan Mamy, ai kuwa ranan kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha tun sanda yayi mata albishir ɗin ta shirya su je, har suka kai gidan bakin ta ya ƙi rufuwa sai murna take yi
Haka ma Mamy babu wanda ya kai ta murna tsaban farin cikin ganin yanda Maimunan ta sauya, ta yi haske abun ta ta ƙara kyau sosai, har ƙiba ta ƙara da girma tubarakalla, kowa ya kalle ta sai ya ji sha'awar ta
Shiyasa ABUL KHAIRI yanzu ba ya gajiya da kallon ta sabida ba ƙaramin sauya masa tayi ba, yarinyan da yake kallon ta ƙarama amma haka ta girma ko wata ƴar shekara 25 ɗin baza ta nuna mata komi ba. Sai yanzu ma yake ƙara ganin kyakykyawar surar ta da kyawun da Allah yayi mata, amma ada idanun sa sun rufe saboda wata. (Dama an ce sai an rasa wani abun ake gane muhimmancin wani abun).
Mamy dai sai nan-nan da ita take yi domin tunda tayi mata kallo ɗaya ta gane tana da shigan ciki a jikin ta, abun har mamaki ya bata sai kuma ta koma dariya a ranta tana cewa, "oh su Baba na manya ana so ana kaiwa kasuwa, sai kace ba shi ne ya gama hatsaniya a kan auren ba amma ga shi har da guzuri muka samu, Kaii Allah ya shirya Baba na maza basu da kunya ko misƙala zarratan, ya gama ciko baki kuma ya zagaya ya bumbura wa ƴar mutane ciki ɗan ƙwal uba".
_Ina ma ɗaukacin masoya na fatan alkhairi. Allah ya bamu albarkatun wannan rana ta juma'a. Sharrukan da ke ciki Allah ya kare mu Amin ya Allah. JUMA'AT MUBARAKH FAN'S. 🤩💃💃💃🤸 🤸🤸 ayi weekend Lafiya._
🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸
*ABUL KHAIRI*
🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸
💧💧 *LABARIN DEEBIZAH RETURN* 💧💧
*MALLAKAR:*✍️
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_
*SARAUNIYAR TSOKANAR PARFECT*🧝🏻♀️
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞
'''(WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)'''
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*✍️
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Mahaifiya ta Abar alfahari na, Uwata maganin kuka na, I love You so Much Momma_ ❤️
*________________________________*
*PAGE 40*
*________* Sai dare suka yi haraman tafiya. Da za su tafin ne Abba ya ce, "ya saka rana a wannan satin ya kai Maimuna can Kaduna tayi hutun ta, inyaso idan sun koma school sai ya je ya ɗauko ta".
ABUL KHAIRI dake zaune yana jiran Maimunan ta fito sai da ya ɗago ya kalli Abban, kamar bazai yi magana ba sai kuma ya kasa jure wa yace, "Abba kana nufin har two weeks zata yi a can?"
"Eh mana. ko da wani matsala ne? Ka san dai bazai yiwu ka hana ta zuwa ba, yarinyan nan tun kafin auren ta take nan garin; sannan za'a yi auren nata ma bata je can ba sabida kara irin na iyayen nata, ka ga kuwa dole yanzu ta je ta zauna na kwanaki don ta gaisa da dangi, ai sun mana mutunci wlh".
Be dai sake cewa komi ba har suka fito suka hau mota suka wuce gida, suna shiga ko kallon inda Maimuna take be yi ba ya zarce ɗaki, maganar Abban ne duk ya tsaya masa arai, "to a kan me zai bar matar sa ta tafi wani uwa duniya har na tsawon sati biyu bayan shi kuma yana tsananin ɓukatar ta? kai gaskiya bazai iya ba dole akwai sake".
Koda washe gari yayi haka ya tashi duk a cikin fushi, ko kallon Maimuna ya ƙi bare ya ci abincin da ta dafa mishi, abu kaɗan sai yayi mata tsawa kamar tayi masa wani laifi
Hakan yasa itama ta kama kanta ko fito wa a ɗaki ta kasa yi gudun kar ya bige ta, sai dai duk ta damu sabida ganin sa a cikin damuwa, but baza ta iya tambayar sa ba tunda ma bata ga fuska ba har yanzu
Shi kuwa ya so ya kaita gidan Hajiya Mama ne da gidan su Abba a yau ɗin, amma jin abinda Abba yace duk sai ya fasa acewar sa, "bazai kai ta ɗin ba".
Bayan kwana uku ko maganar be sake yi ba sai da Abba ya kira sa ya tuna masa kuma yayi masa umarnin, "goben nan su wuce Kaduna". Dalilin da yasa kenan ya sanya ta ta shirya kayan ta ya sanar mata inda zai kai ta
Ai murnan da ta nuna sai kuma abun ya zame mata matsala, domin a ranan rufe idon sa yayi ya dinga mata faɗa wai, "gasa ta yake Yi a gidan ko kuma gidan nasa gidan yari ne da har take murnan fita a cikin sa?" Ta inda yake shiga dai ba ta nan yake fita ba, har so yayi ya mangare ta tsaban haushin ta da yake ji
Ita kuwa