Showing 51001 words to 54000 words out of 95282 words
Chapter 18 - AFIYYA BOOK COMPLETE DOCUMENT By A'ishatu.txt
bakina wanting to pour out my heart all, Ina son naji zuciyata tayi wasai, bana son naji Koda digon bacon Rai, nasan na rike da yawa at this rate Ina jin kamar zuciyata zata fashe kamar bakin ciki zai kasheni. Na Gama kuka na sannan na Danna code din se gashi ya bude, na fara shafa littafin rubutun shi ne a ciki, ta gefe pictures Dina ne, title din chapter ARRIVAL OF OUR PRINCESS! kalamai ne masu Dadi masu sanyaya zuciya Wanda zasu tabbatar maka ko daga wanne baki ya fito to tabbas ba karamin son Wanda aka rubuta danshi suke ba. Na saki kuka Ina fadin
" Abbuna!"
Ganin kamar zanyi hauka yasa na rufe na Yi alwala nazo na dauka casbaha na fara ja, a hanakli naji nutsuwa tana saukar min, se naji kamar an bude zuciyata damuwa ta na evaporating cikin iska!
Junaidu ya kalla kanshi, ya kalli kofar Dana kulle yana iya juyo ihun kukan da nake, ya Kara kallon manhood din shi dake a kwance Babu alamar erectile muscles dinsa na aiki, ya Mike a mugun fusace ya maida wandon da sannan ya fito daga dakin, hannun shi na rawa ya fara Kiran Safiyyu
" Yane angon Amina?"
Ya buga tsaki yace
" Taki tashi!"
Cikin rashin fahimta Safiyyu yayi dariya yace
" Ka haike ma yar mutane Allah yasa baka kashe ta ba, wa yaga farin Shiga, ko nazo muje asibiti?"
Ran Junaidu ya Kara baci yace
" Banma shiga jikinta ba, abar Taki tashi kwata kwata..."
" What?!"
Safiyyu yayi exclaiming cikin mamaki yace
" Me ya faru?"
" Da na sani Zan kiraka ne? Fada min zakai yadda zanyi, golden time din na tafiya fa!"
Safiyyu ya fara tambayar shi yadda akai ya fada Masa shi kaiwa afka min yayi, Safiyyu ya dinga dariya yace
" Malam ai ba Haka zakai ba, se kayi romancing dinta kafin..."
" Kaga ni fa Banda wannan Saar bana tunanin Zan taba kallon mace naji wani shaawa"
" To Haka zaka Bari lokacin ya wuce, nasan ba sonta kake ba ba zakai shaawarta ba, to Amma idan ba Kai amfani da ita ba kenan kawai Sa'idu ka cikawa burin shi, kaga ya samu dukiya sannan ya saka kana bawa yarinyar da Bata ji bata gani ba wahala, kaci sadakin ka !"
Haka yayi ta zuga shi har ya amince, nikam nayi wanka na fito saboda yunwar da nake ji, Babu abinci alamar ya shigo yaci kenan, spaghetti na dakko na dafa daidai cikina Dan bazan bashi abinci ba, alkawari nayi tunda zai iya daga hannu ya dakeni to tabbas na daina dafa mishi abinci. Ina Gama sauke taliyar na juye cikin collander, nasa stew din cikin microwave na fara warming, tana gamawa na juye a plate har lokacin bawai Ina jin ni din farin ciki nake ba Amma dai Babu laifi na samu sauki. Na fito rike da plate dayan hannuna da ruwa, shi baya sallama Dan Haka ban maki shigowar shi ba, Yana zuwa tamkar wani dabba ko Dan dabba ne tunda dabbbobi kawai ke amfani da wannan approach din ga partners dinsu. A tsorace na saki plate din hannuna ya tarwatse Haka ruwan ya bi nashi gurin, ya janye hijabina Wanda ya bayyana rigar dake jikina, Bayan nayi wanka Naga Babu amfanin saka Kaya kawai se na dakko daya daga cikin kayan baccina thigh lenght silky milk, duk kirjin net ne me Asalin kyan gaske, tayi exposing dukkan boobs Dina a waje, ya keta rigar wadda ta bayyana jikina take na silale kasa a kokarin Kare kaina ya bini ya fara exploring jikina, ana cewa wannan abin nada Dadi ko? That's idan zuciyar ka da gangar jikin ka ta amince, ni din Banda ciwo kunci, bakin ciki, tsoro , bacin Rai Babu komai a cikin zuciyata, Ina kallo ya raba kanshi da kayan jikin shi, ya daura bakin shi a nawa duk yadda nake kokarin kaucewa ban iya tserewa wannan awful kiss din ba, it was a moment da bana son a rayuwata na Kara tunawa, it was the most hardest moment of my life, Ina ihu Ina komai Ina Kiran sunan Allah, Ina kwalawa Rooks kira, Ina neman taimako se naji an hankada ni for the second time his manhood refuse to erect, ya saki wani ihu tareda yin wurgi da wani flower vase dake Kan center table, yana zuwa bango ya baje Karin aiki kenan, nayi saurin mikewa na nufi dakina Ina adduar Ina ma na koma gidan Kawu Sa'idu ya fiye min wannan zaman balain da kuncin!
Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment through 09063467258.36
Mu muna daki bamu San abinda take faruwa a parlor ba, Rooks nata kokarin ganin ta fahimtar Dani akan na dauki zaman mu dashi a matsayin jihadi, nayi kokarin daidaita rayuwar shi, kilan shi ne dalilin da yasa Allah ya kaddara auren mu, nidai nasan a kur'ani ance mace ta gari ta miji nagari ce, Dan Haka na sawa Raina ko ba yanzun ba ko da watarana ne se na rabu dashi, Kuma jikina na bani komai ya kusa zuwa karshe. Se yamma sannan Suka dauki hanyar tafiya, banyi kuka tunda Banga amfanin kukan ba, I've cried enough da ace kuka na canja ma mutum rayuwa tabbas da tuni bana cikin kuncin da nake ciki. Har gate na raka su Ina kallo suka tafi, na maida kofar na rufe na dawo na zauna a parlor very deep in thought, to Babu abinda zanyi seda suka gyara min komai da komai sannan Suka tafi. Ina nan zaune har dare yayi se wajen Sha daya naji motsin shi, ya shigo yadda Bai cemin ci kanki ba Haka Nima bance Masa ba, na maida hankalina akan kallon da nakeyi. Dakin shi ya wuce na zata bacci zaiyi Dan Haka na Kara sakin jikina deeply immersed a tunani, Dan ba ma gane abinda akeyi nake ba, tunani na duka Yana kan maganar da mukai da Rooks, nasan duk maganar da ta fada gaskiya ce Zan iya Zama silar shiryuwar sa but that's only idan Yana sona, to nikam kullum kallon da yake min kallon tsana ne da irin Bai taba ganin Abu so disgusting like me ba. Na sauke ajiyar zuciya Ina jin ta Ina Zan fara? Ya kamata na saka shi ya fara sallah but ta Yaya? Banma San Wasa nake da bakin wuta ba se washegari, very early na tashi wannan macaroni da banci ba saboda zuwan su Rooks na dafa na zuba cikin karamar warmer na aje sannan na danyi gyare gayren da ba zaa rasa ba na Yi wanka na shirya cikin bakar Abaya gashi na na kalla gaba daya ya cunkushe Ina bukatar kitso, duk lalacewar zamana a gidan Kawu Sa'idu Ina zuwa kitso. Na dakko comb na taje na saka band na kulle Kan na daura dankwalin abayar, Dana fito ya riga da ya fito Yana zaune kana kallon shi kasan Bai wanke fuska ba, na karasa nace
" Ina kwana?"
Bai cemin komai ba Wanda yasa na fara jin haushin dalilin da yasa na Masa magana ma in the first place. Kitchen na wuce na zauna na zuba Mai da yaji naci abincin da duk yadda na Kai da rashin cin abinci da yawa Bai gamshe ni ba. Na Sha ruwa na fito Yana nan inda na barshi se kawai na shige daki na kwanta Ina juyi Ina jin matsananciyar Yunwa na addaba ta. Kwalla min Kira yayi yasa na fito, alamar zai fita Dan yayi wanka ya Kuma canja Kaya, ya dubeni da ga sama har kasa yace
" Ki shirya zakije can gidan'
Na gyada kaina ba tareda nasan wanne gidan yake nufi ba, ciki na koma na canja kayana zuwa zani da riga na atamfa na dauka babban veil na yafa sannan na Dan tsinci abinda zanyi tsaraba dashi na fito, yayi gaba na bishi a baya, a kusan watanni biyu wannan ne Karo na farko Dana saka kafa ta a wajen gate, banma San ya yanayin unguwar yake ba, duk yadda ya kamata na Shiga makota na Amma ko kadan ban shiga ba, wa ya Isa ya barni inama Naga fuskar tambayar. Motar shi na Parke kofar gida se kyalli take, wani yaro a tsaye ya samu kwankwalatin lemu ya fara karto Masa mota tun daga farkon bomber zuwa karshe, kwankwalatin Nan ya cika Tam da paint din shi, nayi saurin saka hannuna na rufe bakina tausayin yaron da iyayen shi suka Kama ni, nasan yau rashin arzikin da Junaidu zaiyi se inda karfin shi ya Kare, ga yaron ya kusan 10years hakan ya nuna Yana sane yasan abinda yake ba daidai bane. Na kalle shi na dubi yaron da ya Yar da kwankwalatin ya nufi gidan su a guje, Junaidu ya cire rigar shi ta bayyana farar singlet din dake jikin shi, ya wullo min rigar a fuskata ya take kafafun shi yabi yaron nan da already ya riga ya shiga gidan su, na bishi da sassarfa Dan kada ya Shiga gidan mutane Amma nasan ni wacece, Ina zuwa ya Kama yaron Yana dukan shi tun karfin shi, ga uwarshi nata balai Amma ba zata iya kwatar shi ba. Na karasa na ruke hannunshi ba tareda nasan nayi hakan ba, saboda dukan yadda kuka San saan shi yake yiwa.
" Dan Allah ka rabu dashi, Dan Allah!"
Na fada Ina rike hannun shi, ganin yadda nasa karfina gaba daya na rikeshi, se yasa hannun shi ya bugeni, nayi baya tamkar Zan Fadi wata budurwa a gidan ta Dan girmeni ta rikeni seda na tsaya da kafafuna kafin ta sakeni, ya saki yaran Yana karbar ko nace yana wartar rigar shi a hannuna ya fice, da sauri nabi bayan shi na samu sunyi kicibis da Wanda nake tunanin shi ne baban yaron,
" Wa yace ka.shigar min gidana? Na Dade da sanin Kai jahili ne Amma bansan abin naka har ya Kai Haka ba, Dan Haka yau ofishin Yan sanda zaka kwana"
Banyi tunanin zaiyi Masa shiru ba Amma ga mamakina se Naga ya wuce ta gefen shi, hannun shi ya rike tareda fadin
" Ina zaka je kake tunani? Ka shigar min gida ka Kuma Dakar min Dana sannan kace zaka tafi, karya kake wallahi!"
Junaidu ya dubeshi ya Kuma dubi hannun shi dake rike hannun mutumin, nasan he's going to do something stupid, nayi saurin kallon mutumin nace
" Dan Allah ka sake shi, ka bashi hakuri Dan ka ya Karta Masa mota"
Ya min wani mugun kallo da inaga ko Junaidu Bai taba min wannan disgusting look din da yasa naji ni totally embarrassed irin kallon da mutumin yayi min ba
" Rufe Mana Baki karuwar banza karuwar wofi, mu munyi tunanin babbar mace ce ma Ashe kece"
Se nayi shiru Ina jin jikina yayi balain sanyi, karuwa? Na tambaya kaina Ashe ban sani ba kallon da duk Yan unguwar kemin kenan ni din karuwar shi ce, suna ganin Babu iyayen da zasu dauki Yar su su bawa Junaidu aure, take na ja kafafuna da nake jin Kamar anyi musu duka na nufi jikin motar shi Ina tsaye, mutane suka taru saboda police har sunzo, ni ba damuwata abinda suke ba, damuwata kallon da ake min da nuna da ake Yi shi ne matsalata gashi Kuma ya kulle gidan sannan a yadda temper shi take high Ina Masa magana zai iya nada min duka cikin mutanen nan ba damuwar shi bace.
Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 0906346725837
Ina daga can gefe idanuna s unyi ja, a karamar shekara ta na kunshi bakin ciki kalakala Amma kowanne idan yazo Ina ganin kamar Zan iya coping se na kasa, baa taba sabo da Shan wahala. Tabbas ance kudi masu gidan Rana, quite sure kowa yasan yaron ne bashi da gaskiya Amma Junaidu ya dauki hukunci a hannun shi, ya Shiga gidan mutane sannan ya daki Dan mutane duka irin Wanda zaka yiwa saan ka, yaran duk fuskar sa tayi kacakaca da jini Amma a haka police officer ya cahrge iyayen shi akan se sun gyara Masa damages sannan su bashi hakuri Kuma, instead shima ayi charging dinsa for assault se suka kyale shi. Ina ta kallon ikon Allah, Haka Suka juya Bayan sunyi musabaha dashi suka tafi su Kuma parent din yaran suka dauki dansu zuwa asibiti, gashi tunda daga gidan kasan karamin karfi ne dasu Amma ai ya kamata ace ya biya kudin ko da magani ne. Muatnen gurin se tsine Masa suke suna fadain daga shi har Wanda ya rabe shi a wuta zasu, ni dai duk a tsorace nake ya dubeni ba tareda ya min magana ba ya bude gidan ya shiga, na bi Bayan shi cikin sauri jin an fara cewa ki jefe su, Ina Shiga dutse Yana bugan gate din, na sauke ajiyar zuciya Ina godewa Allah da Bai sameni ba, na shiga parlon na sameshi yayi daidai da drink a hannun shi Yana sha, ko Zama banyi ba aka Kira azahar naje nayi alwala na dawo na samu ko matsawa baiyi ba, nayi sallah na dawo nace Masa
" An Kira sallah gashi har an idar ma!"
Yayi min banza kamar yadda ya saba, maimaikon na kyaleshi se nace
" Ba kyau abinda kake Yi, abinda yake raba Arne da musulmi sallah ce kawai, tunda Suma a cewar su ai suna azumi Amma sallah ce basayi, Kuma idan kana sallah in har ta karbu ko sauran ayyukan ka baa dubawa..."
" Keeeeeee! Ni saan ki ne?"
Naga karfin halina nima, nace
" Ai waazi ba se saa ne yakeyi ba, baka ganin malamai nayiwa shugaban kasa waazi ba? Hakkina ne na fada maka gaskiya Dan idan ka mutu a Haka Allah kadai yasan me zai ma..."
Ban ma karasa ba naji saukar kyakyawan Mari a saman kuncina, na Mike tsaye idanuna Suka ciko da hawaye Amma har lokacin bakina yaki yin shiru na cigaba da fada Masa abinda ya kamata a fada masa aka ki fada masan, ni kaina nayi mamakin daga Ina na samu wannan confidence din? Ban taba ganin bacin ran shi irin wannan ranar ba, ya dakeni kuwa ranar, Dan duk jikina seda yayi birdin dukan da yayi min, nayi ta kuka a daki ni daya Ina jin duniyar gaba daya tayimin zafi but I still have to pick myself up, tunda Allah yasa ba mutuwa zanyi ba to ya kamata nasan abinyi, bazan cigaba da Zama cikin wannan rayuwar ba, Dole na nemawa kaina mafita.
Watanni biyu suka Kara Hawa akan Wanda nayi a gidan shi, ya tsiri wasu halaye Kuma na daban kullum se ya dakeni ko nayi Abu ko banyi ba, idan zai fita se ya daina barin gidan a bude se de ya rufe ni ta waje, gaba daya na hargitse banida wani aiki se kuka se plotting yadda zanyi na bar gidan, Babu Wanda ya Kara zuwa gurina se mummy da Rooks shima har kofar gidan suka zo Suka kirani se kawai nace ai bama nan munyi tafiya to ta Ina Zan fada musu cewar ya kulleni ne a gidan, lokuta da dama Ina jin ana knocking Wanda nasan Yan gidan su ne Amma Babu halin shigowa,zancen abinci sau daya ne a Rana yake bani, I remembered na taba jin suna waya da Kawu Sa'idu kafin ya fara bude min wuta sosae
" To Kai me kake tunani? Ni kaina bansamu abinda nake so ba, ai cewa akai se na kusance ta kafin burina zai cika, ni banyi ba Banda asara me auren ta ya tsinana min?"
Daga dayan bangaren Kawu Sa'idu yace
" Ni kaina bansamu abinda nake so ba Sabida Kai dinne madaogara, Amma ya zaayi kace min ka kasa kusantar ta Bayan na aura maka ita"
Junaidu ya dunkule hannun shi yace
" Zancen banza kenan! Idan Haka ne Zan sake ta Dan na gaji da ajiyar ta tunda ba amfani take dashi ba"
" Baka amsa tambaya ta ba, me ya hanaka ka kusance ta, Kuma ya zaka saketa bamu cika burin mu ba"
Se lokacin Junaidu ya Masa bayanin Ashe Erectile dysfunction or damun shi, an samu hakan bayan dogon bincike da akai a asibiti suka fahimci trauma ne na dukan da Yan sanda Suka ta Masa lokacin samar takar sa, ranar yini nayi Ina farin ciki a ganina Allah ne ya fara saka min duk zalincin da yayi min. Nafi tunanin a wañnan wayar Kawu Sa'idu ya fada Masa yayi ta duka na Dan nasan zaiyi abinda yafi Haka.
Ranar wata lahadi na tashi da zazzabi da azababben ciwo Ciki Wanda nasan Yunwa ce ta saka hakan, nayi kuka nayi juyin har bacci ya daukeni, se wajen asr na tashi nayi wanka sannan na fito Dan daura abinci, na samu shinkafar ba tafi gwangwani daya ba, na dafa sannan na zauna naci, Ina cikin ci naji muryar shi alamar Yana waya, ya shigo kitchen din ya tsaya Yana kallona, ko inda yake ban kalla ba na cigaba da cin abinci na, Yana tsaye Bai motsa ba yau a wuya nake Dan tunda na tashi a zazzabin na dauki alkawarin Rama duk abinda zaiyi min Koda zai kashe ni ne. Kamar yasan me nake tunani se ya fita daga kitchen din, na sauke ajiyar zuciya na Gama na fara wanke wanke se naji Yana kwalla min Kira, na duba kitchen din tas Ina neman makami, Idanuna Suka sauka akan set of knives da ban taba amfani dasu ba, na dauka butchers knife na zura cikin sleeve Dina na fito, yana tsaye Yana wurga min harara kamar idanun shi zasu sakko, na tsaya nesa dashi Ina Masa kallon tsana nace
" Menene?"
I swear seda Naga bakin shi ya bude saboda mamaki, ya nufo ni gadan gadan, na zaro wukar daga hannun riga ta, ya daga hannu shi zai mare ni nasa wukar na yanki damtsen shi sannan na wullar da wukar na tsaya Ina huci, hannun ya rike ya saki ihu, a take jini ya fara zuba, Dan na yanka tundaga rigar har jikin shi, nayi baya se daki na datse kofar Ina jin ihun shi, se naji me yasa ban ma kashe shi ba yadda idan yaso Nima se a kashe