Showing 42001 words to 45000 words out of 95282 words

Chapter 15 - AFIYYA BOOK COMPLETE DOCUMENT By A'ishatu.txt

Ayshatuu   

16 Jul 2024

6652

ya fita. A hankali na Kai hannuna na rike kirjina dake min zafi,nidai ban cancanci wannan rayuwar ba!






" Me yasa kaki Mata magana?"


Safiyyu ya tambaye shi lokacin da suka dauki hanya, Junaidu yace


" Me zance Mata, nifa kaina mamakin yadda akai na yadda Zan aureta nake"


Safiyyu yayi dariya yace


" Nasan Mata basa gabanka Amma yarinyar nan karama ce Bata San komai ba , Dan Allah ka rike ta da kyau"




Junaidu ya kalleshi Yana sakin dariya yace


"Kai da bakin ka kake hadani da Allah?"


Ya Kara kwashewa dariya yace


" Kai kanka kasan badan an bani saa da aurenta ba Banga dalilin da zaisa na aureta ba, Kuma bayan Haka nafi son ta shigo da Shirin cewar uwarta zataci ba Dadi zata ji ba"


Safiyyu yace


" Tayi kankanta yarinyar, baka ganin kamar shima Sa'idun Yana da wani dalili na aura maka ita"


" Eh mana dama ban Gaya maka ba? Yarinyar nada dukiya wadda take hannun kannenshi, yasan idan ya bar yarinyar tayi karatu watarana zata karbi dukiyar ta shiyasa ya hanata karatu, sannan ya aura min ita, to shi Malam na Dan Issa ya fada Masa idan ya aura min ita Babu jimawa dukiyar zata dawo hannun shi, ni Kuma idan na aureta zata zame min kariya daga dukkan sharri, sannan gidan mu da nake son ya tarwatse to zai tarwatse"


Safiyyu ya jinjina Kai yace


" Akwai samu kenan! Amma dukda Haka banso a saka yarinyar a ciki ba"




Kamar yadda nayi tunani, washegari Sega Mummy da yamma itada Rooks, Kawu Tijjani ma ya iso. Ina daki na zubawa kayana Dana wanke idanu Amma ko daya na kasa ninkewa naji sallamar Mummy, nayi saurin sakin hular hannuna na mike, fuskarta dauke da murmushi ta rungume ni, Nima na rungume ta inajin sanyi cikin raina, ta sakeni ta zauna Nima na zauna se Kuma na dauki hijabi na fita Ina kallon Rooks da taki kallona, nayi murmushi na je wani shop kusa damu na siyo ruwa na dawo, Ina Zama Rooks ta matso nace Mata


" Ni nayi fushi!".




Mummy tana Mana dariya har muka fara Hira, na dubi Mummy nace




" Yanzun na bayar a siyo awara abincin ya Kare"


Tayi min murmushi yace


" To daughter, kawun ki yace min kin fitar da miji ko?"


Na danyi Murmushin yake na tuna kashedin da yayi min yau da safe akan kowa yazo nace ni nake son Junaidu ni na zabe shi, anan yake fada min shi din Dan kazaure ne. Na gyada Kai Ina sunkuyar da kaina , tayi murmushi tace


" Amma jikina na bani you were forced. Tell me Afiyya gaskiyar magana"


Na dago na kalla Rooks da ta ke Wasa da zoben hannunta Wanda take nuna nervousness dinta, nace


" Mummy da gaske!"


Se tayi murmushi again tace


" Amma shi ne baki fada Mana ba, se saura sati biyu yake fada Mana. Allah ya Sanya alkhairi Amma naso ace ba aure Kika zaba ba karatu Kika zaba, dukda auren ma is in line, But tunda Haka ne ki sani Ina tare da
Ke duk abinda kike so ki fadamin"


Na Share hawayen idanuna nace


" Mummy nagode!"


Aka kawo awara tana ta min nasiha da guda min yadda zamantakewar aure take, se yamma Suka tafi Kawu yace na bisu saboda Shirin biki. Kwana biyu duk yadda nake son aiki ta hananin se hutawa kawai da nake tace nayi Rama da yawa kullum girki take koya min tana bani nutritious food Ina ci, ban Kara ji daga gurin angon ba, tunda ba waya ce Dani ba Dan ta gurin Yaya Shehu Kawu ya karba tun kafin na hada ta. Mummy ta Kira Nanny se gata ta taho ta fara guarani, nayi yar kiba nayi kyau. Da daddare tana mulka min wani yellow abu me azabar kamshi a jikina Rooks na zaune tana mitar se an shafa Mata tace


" Ku fada min gaskiya meye zancen aurennan?"


Nayi kirikiri nace


" Ai na fada Miki ni na fito dashi"


Tayi dariya kawai tace




" Yara kenan!"




Shirye shirye sosae Mummy keyi,saura sati daya Ina zaune a daki na hada kaina da gwiwa nayi shiru Kuma ni ba kuka nake ba Rooks ta zauna gefena tace




" Afeey yanzun auren zakiyi? Wanda Baki taba sani ba shi Zaki zauna dashi, Afeey Ina jin kamar I'm a bad person da nake kallo kina Shan wahala Amma na kasa fadawa kowa"


Na riko hannunta nace


" Watarana zanji Dadi karki damu"




A wañnan Daren Ummiey ta iso da family dinta, Haka Uncle Babawo Wanda min ringa munyi waya a wayar Mummy. Ummiey na yin wankan ta taho gidan Mummy ta same ni a parlor ana turara ni, Mummy nata duba kayan kitchen din da tayi order. Ummiey ta zauna Suka gaisa, Suka gaisa da Nanny


" Yanzun Maryam yarinyar nan tayi kankanta da aure shekara Sha biyar fa!"


Mummy ta sauke ajiyar zuciya tana kallona tace




" To ya zanyi? Ita ke son shi, da farko nayi tunanin Yaya Sa'idu ke fada kawai Amma ta tabbatar min da bakinta Haka ne"


Ta girgiza Kai tace


" To Allah ya Sanya alkhairi, shi Kinga mijin anyi bincike sosae"


Mummy tacr


" Munyi maganar da Sa'idu yace komai steady Kuma Wai baya gari shiyasa Bai zo min gaisa ba"


Itadai Ummiey kawai kanta take gyadawa Amma dukda Haka idan muka hada Ido se nayi saurin sauke idanuna Dan gani nake she's seeing through me.






AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment through 08063467258..29








" Ummiey tun tuni nace Miki Ina sonta Zan aureta, Ummiey Kika ki yadda! Ummiey gashi ina kallo a young age din nata zaayi Mata aure and I'm sure Bata son mijin!"


Ummiey ta dafe kanta, wannan dalilin ta so ace Shehu Bai biyo ta ba, Amma tunda yaji labarin aurennan gaba daya nutsuwar shi ta tafi, ita gani take kamar Wanda yake nema ya zautu.


" Me ka sani Shehu? Afiyya da kanta ta zaba mijinta, da bakinta race min ita tace tana son shi..."


Shehu ya Kara Shiga damuwa yace


" Se kuka yarda da ita Ummiey? Kina ganin gaskiyaa ta Fadi maki? That girl has already giving up! Ko Baku lura ba Ummiey? Ta riga ta cire tsamannni daga afuwar rayuwa, tana ganin rayuwa ba wajen da zaka samu sauki bane Ummiey! Why are you all blind Ummiey, ta Yaya zaku barta tayi ta Shan wahala a hannun wancan azaalumin..."


" Shehu!"


Ummiey ta daka Masa tsawa, ya dago idanun shi da sukai ja ya dubi Ummiey da take kallon shi a bace


" Ya zanyi? Shehu Yan uwan babanta ne, shi ne marikin ta Shehu. Ya zanyi Kuma banida wani kwakwaran shaidar cewar auren Dole ne, Afiyya tayi testifying cewar ita take son shi. What else do you want me to do!"


" Duk laifin ku ne Ummiey, da Kun riketa da kyau Kun jata a jiki how'll that animal in human form zai dinga wahalar da ita"


Yana Gama fadar haka ya saka kanshi ya bar parlon ya bar Ummiey zaune da tagumi. Sarki ya karaso ciki ya zauna gefen Ummiey sede baiyi magana ba


" Na sani munyi kuskure babba, min watsar da Yar Halima. Halima ta fiye min dukkan Yan uwana Amma bansan me yasa da ta rasu na kasa daukar Yar ta ba, bansan me yasa na dinga fushi da ita ba, I never imagined Yar Halima cikin wannan mess din. Sarki I'm a bad sister"


Ta fada tana riko hannun shi, ya gyada kanshi yace


" Haka ne Ummiey, the worst thing shi ne babu lokacin gyara, lokaci ya rigada ya Kure"


Se ta fara kuka tana Kara kankame hannun shi cikin nata. Babu jimawa se ga Yaya Shehu ya karaso gidan Mummy. Ina can bedroom din Mummy Ina Shan fruit, nayi kyau jikina yayi kyau se glowing yake irin na asalin amaren nan, ko raba ta kazo Yi zakaji kamshi me dadi dake tashi daga jikina, tabbas idan da ace Wanda na aura mutumin arziki ne ko Kuma ace dukkan mu muna son juna to Babu tantama da yayi saa, Nanny tayi kokari sosae. Duk wannan abin da ake Yi Kuma Banda Rama Babu abinda nake Kara Yi, Rooks dake zaune tana kallona yadda nayi shiru very deep in thought, I'm very stupid I know Amma Nima baa wannan lokacin nasan I was stupid din ba se daga baya idan na tuna abubuwan da Kuma shirmen da duk nayi se naji haushin kaina nake ji, naji Ina tuhumar kaina da rashin trusting Allah, da Kuma rashin trusting rayuwa, Dan da ace nayi trusting din rayuwa na Kuma game menene concept na kaddara I would have prayed. But I was so reluctant, na saka a raina Babu inda sauki zai zo, na sawa Raina duniya ba gurin jin Dadi bace na Kuma saka a raina Babu me zuwa kawo min dauki.


" Keeee tunanin me kikeyi Haka?"


Rooks ta tambaya tana bubbuga kafada ta, na girgiza Kai Ina sakin fork din hannuna cikin bowl din nace


" Ba komai, just some few thoughts!"


Tayi murmushi tace


" Ina Miki fatan alkhairi Afiyya,ke Kuma path din da Zaki bi kenan Haka Allah ya tsara Miki. Make this relationship work, ki bashi hadin Kai Allah kadai yasan me ya tanada Miki a ciki"


Nayi murmushi kafin nayi magana naki muryar Nanny na Kirana, nayi saurin saka hijabi na fito, ta dubeni tace min naje Mummy na Kirana a parlon kasa. Cikin nutsuwa na dinga tattaka stairs har na sauka kasa, na nufi parlon da Babu kowa a ciki, idanuna cigaba da cillawa se da nazo tsakiyar parlon sannan na lura da Yaya Shehu dake zaune ya hada kanshi da gwiwa, nayi saurin Zama Dan nesa dashi nace


" Yaya!"


Da sauri ya dago idanun shi ya sauke kaina, cikin sauri na kawar da nawa saboda yadda sukai jawur, ga Kuma bacin Rai da ya kwanta cikin idanun ya fito kurkuru. Cikin wata murya da take a hargitse kamar yadda shi dinma a hargitse yake, fuskar shi looks pale yace


" Are you stupid?"


Na kalleshi da mamaki idanuna a warwaje Amma ni din Afiyya ce indai wajen share mutum ne na Masa banza Ummaan su Yaya ma ta buga ta barni.


" Bakiji tambaya nayi Miki ba? Kina haukana zakice ke Kika ce kina son a Miki aure? Come on Afiyya Baki ce min karatu kike so kiyi a Oxford University ba? Didn't I promise you to stand for you and make all your dreams true? What does it takes ki ce musu auren Dole zaayi miki, why are you doing this?"


Nayi shiru dukkan kalmomin da take fada na dukan kunnena Haka hearing nerves Dina na dauka suna kaiwa kwalkwalwata tana interpreting Ina fahimtar me yake cewa. Na taba fada muku son da Yaya Shehu yake minis immeasurable? Ko ni bansan yawan son da yake min ba, bansan how much Zan fada muku irin son da take min ba, a wasu lokutan a rayuwar mu we always go for the wrong person kamar yadda Sofy tayi akan Alby dinta.


" Afiyya kiyi hakuri just tell them wannan animal in human form dinne yayi forcing din ki, kinada chance Amina ki fada yadda zaa San abinyi"


" Ni Ina son shi!"


Na fada Ina kawar da kaina, I dunno why I was so adamant, I really don't know, Ina furta hakan Naga gaba daya jijiyoyin dake wuyan shi da kanshi Wanda Zan iya gani sun tashi,idanun shi ya runtse tare da naushi sofar da yake Kai ya furta




" Damn it! See Afiyya, ba Dole se kin kula ni ba, ba Dole se kinyi reciprocating feelings Dina ba, Dan Allah ki Fadi gaskiya for once kiyi farin ciki cikin zuciyar ki, it's so obvious aurennan na Dole ne, duka shekaran ki nawa , yaushe Kika San meye so?"


Yafi mintinann da bazan iya lissafawa ba Yana persuading da ni ba, Amma Haka na ki Koda cewa komai. Karshe na Mike na tafi na barshi a gurin , why did I done that? Nima bansani ba, kawai na koma kawai auren nake son ayimin. Na koma daki na dinga kuka Ina Jim zuciyata na yimin zafi, Haka na hakura Dan kaina. Da daddare Ina kundundune cikin blanket se naji sallamar Mummy da Uncle Babawo, na Yi saurin mikewa na zauna Ina kirkiro murmushi nace


" Uncle"


Ya zauna yace


" Princess!"


Se idanuna suka ciko da kwalla, Abbuna he always call me Princess, Allah ya rahmushe shi ya jikan shi har da Mama da dukkan musulmi. Mummy tafita hakan ya tabbatar min magana zamuyi , na gyara zamana yace


" A Ina kuka hadu da wannan guy din Junaidu?"


Wani gumi a take ya karyo min, na fara fidgeting da fingers dina, kana kallona kasan banida gaskiya, shi Kuma se Bina yakeda kallo, se can nace


" I lied! Kawu ne yace na aureshi"


" You ok with that? Wait meyasa kika mana karya in the first place?"


Na share kaina nace


" He threatened me, Dan Allah Uncle kayi hakuri da na muku karya bansan yadda zanyi ba"


Ya danyi murmushi yace


" I know we failed you, mu ba iyayen arziki bane, but Afiyya ya kamata duk halin da kike ciki ki fada Mana. Though na Kara bincike sede wasu sunce ba mutumin arziki bane wasu sun Fadi akasin hakan. So far Zan Kara bincike kafin zuwa asabar din. Ki dinga cin abinci"


Se naji dadi har bansan hawaye ya sakko min ba, se naji wani hope yazowa zuciyata, har ma da ya fita se na kwanta na fara bacci cikin jin Dadi, sede cikin dare na farka maganganun Yaya Shehu suka tayimin echo a kaina se naji na damu sosae, naji fuskar shi da idanun shi sun kasa gushewa a idanuna. Shirye shiryen ya cigaba da tafiya ban Kara saka Yaya ko Yaya Shehu a idanuna ba se ranar saka lalle ko nace walima Dan a Ringim abinda Suka go kiranta dashi kenan. Da daddare Ina ciccire kayan jikina Nads tazo tace min nazo Yaya Shehu na Kirana, na saka hijab na nufi waje Ina jin kamar zanyi gudu saboda Ina son na ganshi na tabbatar da whether he's fine or not. Ina zuwa na samu Yan maiduguri aunties Dina sun zo, ana cewa a kirani mu gaisa, nayi saurin rufe fuskata na fita, dan nasan aka tsaya wannan formalities din bazan je ba. Kamar yadda ta cemin Yana parking space nan na tarar da motar shi, Yana hangoni ya bude min gaban seat dake gefen shi, Babu musu na Shiga na kulle, ai kuwa ya saka central lock ya datse sannan yayi reverse ya fita daga gidan a Dan guje, a tsorace nace


"Ina zaka kaini? Me za Kai min?"




Ba tareda ya kalleni ba yace


" I'm eloping you! Dole se na Hana aurennan at any cost...."










Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria. Send evidence of payment through 09063467258










Talla!




✌🏼Fitattu biyu masu ban mamaki🫀Hakika babban goro sai magogin ƙarfe 😍, Hakk'un wani kaya sai amale ke d'auka🐫, Fitattu biyu👯🏽‍♀sun shiirya tsaf domin nishad'antar daku 🤓 sun shirya tsaf domin fadakar daku🧠 sun shirya tsaf domin dilmiya zuciyoyin ku cikin bege da shauk'in so💋💞, wohoho tabbas ️sahun giwa👣 mai ɓadda na raƙumi 🐪,Fitattu biyu😍✌🏼 masu tafiyar k'asaita, sheƙi, da walwali hak'ik'a koda kud'in ka saida rabon ka😘🏃🏽‍♀️ Fitattun Ƙarshen shekara😍 salon su daban ne dana sauran domin natsuwa da tunani sunyi aiki pure love and romance abun dai sai wanda yakaranta😍 maza ku hanzarta neman naku karku bari abaku labari🏃🏽‍♀️

#Oum Sumayya:- *GAMIN GAMBIZA*✍🏽 Nrml 300 Vip 500
#Oum Ikram:- *SOYAYYA CE SILAH* ✍🏽 Nrml 300 Vip 500


Duka biyu 400👌🏼
Vip 700👌🏼
Via 4210014214
Eco bank and send the evidence of payment via 08139624956
Or mtn/airtel credit via 07017296839 banda vtu hoton kati kawai!30






" Eloping?!"


Na mainaita Ina kallon shi da mamaki, Sam ba kallona yake ba hasalima hankalin shi na kan shi da dukkan hankalin shi suna Kan tukin da yake,


" Me kike tunani? Kina tunanin son da nake Miki kadan ne? Ko Kuma tunanin ki Zan zuba idanu ayi Miki aure ba tareda son ranki ba, idan kikai wannan tunanin to ba kiyiwa son da nake Miki adalci ba"


Na sauke ajiyar zuciya me nauyi, sure wannan Yana bashi babban matsayi cikin zuciyata ba tareda shi kan shi ko Nima na sani ba.




" Yaya Shehu kasan duk abinda hakuri Bai bayar ba rashin shi bazai bayar ba, you can't just do this. Dan Allah ka maida ni gida"




Ya maka min wata harara wadda nasan tsabar yadda ranshi ke bace ne yasa ba ma zai iya min magana ba. Na dauke kaina Amma zuciyata Taki aminta da Wai na gudu, why should I be a coward, I've to accept whatever comes my way! Zuciayata ta tuna min, se kuwa na fara kici kicin bude kofa dukda yayi locking duka kofofin, wannan kicinayar da nake Yi yasa hankalin shi ya dawo kaina gaba daya, har ya kasa controlling brakes din, se ji nayi


" Gab!"


Ya bugawa wani mota. Tuni na sake kofar Ina maida numfashi, yayi saurin parking ya fito, me motar shima ya riga da ya fito, tuni mutane suka fara taruwa Dan kallon abinda ya faru, ni dashi Banda mun saka seat belt da Babu abinda zai hana mu bugu.






" Gimbiya wancan kamar motar Shehu nake gani?"


Daddy ya fada Yana duban Ummiey dake amsa waya, tayi saurin kallon gurin tace




" Subhannallah! Wallahi shi ne"


Daddy yayi saurin parking ya fito, Ummiey ma haka, crossing titin sukai zuwa inda ake ta gutsitsira magana, Shehu na tsaye ya dafe Kan shi ni Kuma Ina cikin motar se zazzare idanu nake, gabana yayi mummunan faduwa ganin Ummiey da Daddy, na fara kokarin fita Amma babu halin hakan saboda yadda ko Ina yake a kulle, yasan Zan iya komawa gida shiyasa ya kulleni, baifi 30 minutes ba Naga mutane na ta tafiya daya Bayan daya,Ummiey na rike da hannun shi ya zura key ya bude motar, kaina a kansu nayi tsuru tsuru kamar kace fit in zura a guje, Ummiey da mamaki take kallon fuskata sannan ta kalla tashi, Daddy yace


" Afiyya!"


Nayi saurin sunkuyar da kaina kasa, Ummiey ta maida kanta Kan Daddy sannan ta dubi Yaya da yayi shiru yana Kara tamke fuska, cikin sanyin murya Ummiey tace




" Shehu me kukeyi tare? Ina zaka kaita?

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login